Ɗan majalisar wakilai mai wakiltar mazabar Jaba/Zangon Kataf a Jihar Kaduna, Hon. Amos Gwamna Magaji, ya fice daga jam’iyyar PDP zuwa APC.
Magaji ya sanar da sauya shekarsa ne a wata wasiƙa da kakakin Majalisa, Abbas Tajudeen, ya karanta a zaman majalisa na ranar Talata. Ya danganta ficewarsa da rikicin cikin gida da ke addabar PDP daga matakin ƙasa har zuwa jihohi.
- Gobara Ta Yi Sanadiyar Asarar Miliyoyin Dukiya A Kasuwar Katako Da Ke Jos
- Haƙar Ma’adanai Na Sa Yara Ficewa Daga Makaranta A Jos
Sauya shekar Magaji ya kara yawan ‘yan majalisar PDP da suka koma APC a majalisar wakilai ta 10 zuwa huɗu, bayan Hon. Chris Nkwonta (Abia), Hon. Eriatheke Ibori-Suenu (Delta), da Hon. Suleiman Gumi (Zamfara).
Sai dai jagoran marasa rinjaye, Kingsley Chinda (PDP, Rivers), ya buƙaci a ayyana kujerar Magaji a matsayin babu kowa, yana mai cewa bai bi tanadin doka kamar yadda Sashe na 68(1g) na kundin tsarin Mulki na 1999 (wanda aka gyara) ya tanada ba.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp