Ƴan bindiga sun kai farmaki garin Tsiga da ke ƙaramar hukumar Bakori a Jihar Katsina, inda suka sace mutane da dama, ciki har da tsohon Darakta Janar na hukumar NYSC, Manjo Janar Maharazu Tsiga (ritaya).
Harin ya faru ne da misalin karfe 12:30 na daren Alhamis, lokacin da ‘yan bindigar suka afkawa garin, lamarin da ya jefa al’umma cikin firgici da tashin hankali.
- Yara 536,000 Ba Sa Zuwa Makaranta A Katsina – UNICEF
- Gwamna Radda Ya Samar Da Keke Napep Don Saukaka Zirga-zirga A Katsina
Rahotanni sun nuna cewa hukumomi sun samu labarin harin, kuma jami’an tsaro na ƙoƙarin ceto mutanen da aka sace.
Har yanzu ba a tabbatar da cikakken bayani game da sauran mutanen da aka yi garkuwa da su ba, yayin da ake ci gaba da bibiyar lamarin.
Zamu ƙarin bayanai idan sun samu.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp