• English
  • Business News
Friday, September 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara

by Abubakar Sulaiman
2 months ago
in Labarai
0
Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Rundunar ‘Yansanda ta Jihar Kaduna ta cafke mutane shida da ake zargi da aikata garkuwa da mutane, tare da ƙwato makamai daga hannunsu. An samu nasarar ne sakamakon atisayen haɗin gwuiwa da ‘yansanda suka gudanar a sassan jihohin Kaduna da Zamfara.

  • Tsoffin Ƴansanda Sun Fara Zanga-Zangar Ƙuncin Rayuwa A Abuja
  • Edo Da Taraba : ‘Yansanda Sun Ceto Mutum 31 Da Aka Yi Garkuwa Da Su Bayan Musayar Wuta

Kakakin Rundunar ‘Yansanda ta Kaduna, DSP Mansir Hassan, ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa cewa lamarin ya samo asali ne daga wani rahoton gaggawa da wani mazaunin Ungwar Ninzom a Jagindi Tasha, ƙaramar hukumar Jama’a ya bayar ranar 22 ga Fabrairu, 2025, inda ya sanar da sace ɗansa, Hussaini Ibrahim, da wasu ‘yan bindiga suka yi.

Bayan samun rahoton, jami’an Ƴansanda daga sashin Kafanchan suka bazama don farautar masu garkuwa da mutanen. Koda yake an ce masu laifin sun tsere a farko, an ceto Hussaini daga dajin da ke kusa da yankin bayan kwana biyu, duk da cewa yana da raunin harbin bindiga a ƙafa. An ba shi kulawa a asibiti sannan aka mayar da shi ga iyalansa.

Bincike ya kai ga kama mutane huɗu: Umar Yusuf Jabiri (30), da Buhari Muhammad wanda aka fi sani da “General” (31), da Ahmadu Nasiru (51), da Zakari Saleh (50) — dukkansu mazauna Jagindi Tasha da Gidan Waya. Jami’an tsaro sun ƙwato bindiga AK-47 guda ɗaya da kuma wasu bindigogi uku ƙirar gida daga hannunsu.

A wani ci gaba kuma, bisa sahihan bayanan leƙen asiri, rundunar sashin yaƙi da garkuwa da mutane ƙarƙashin jagorancin CSP Sani Zuntu, ta gano wani kaya mai ɗauke da bindiga ƙirar AK-47 da aka ɓoye cikin buhu daga Jos, Jihar Filato zuwa Gusau, Jihar Zamfara.

Labarai Masu Nasaba

Buƙatar Daƙile Yawan Ɓacewar Mutane A Nijeriya

Hasashen Ambaliyar Ruwa: Gwamnatin Kaduna Ta Ƙaddamar Da Shirin Ko-ta-kwana

Hakan ya haifar da cafke Abdulmumin Sani da Naziru Musa a Gusau, inda ake zargin sun je karɓar bindigar. Rundunar ta ce za a gurfanar da su kotu bayan kammala bincike. Kwamishinan Ƴansanda na jihar, CP Rabiu Muhammad, ya yaba da ƙwazon jami’an da suka gudanar da waɗannan atisayen tare da tabbatar wa da jama’a cewa rundunar ba za ta yi ƙasa a gwuiwa ba wajen kawar da ‘yan ta’adda daga jihar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: KadunaZamfara
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ko Kin San… Matsalolin Mahaifa Da Suke Hana Haihuwa 

Next Post

Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

Related

Buƙatar Daƙile Yawan Ɓacewar Mutane A Nijeriya
Labarai

Buƙatar Daƙile Yawan Ɓacewar Mutane A Nijeriya

32 minutes ago
Hasashen Ambaliyar Ruwa: Gwamnatin Kaduna Ta Ƙaddamar Da Shirin Ko-ta-kwana
Labarai

Hasashen Ambaliyar Ruwa: Gwamnatin Kaduna Ta Ƙaddamar Da Shirin Ko-ta-kwana

9 hours ago
Gwamnan Kebbi Ya Dakatar da Kwamishinan Ma’aikatar Lafiya Biyo Bayan Sakaci A Aiki
Labarai

Gwamnan Kebbi Ya Dakatar da Kwamishinan Ma’aikatar Lafiya Biyo Bayan Sakaci A Aiki

9 hours ago
Shettima
Labarai

Shettima Ya Bada Umarnin Gaggauta Raba Lamunin Naira Biliyan 250 Ga Ƙananan Manoma 

11 hours ago
Rashin Tsaro: Zanga-zanga Ta Ɓarke A Jihar Kogi 
Labarai

Rashin Tsaro: Zanga-zanga Ta Ɓarke A Jihar Kogi 

12 hours ago
Boko Haram Na Yin TikTok, Suna Sarrafa Jirage Marasa Matuƙi Don Sa Ido Kan Sansanonin Soji – Bulama 
Labarai

Ƙwararren Masanin Tsaro, Bulama Ya Ƙaryata Iƙirarin El-Rufai Kan Biyan ’Yan Bindiga Kuɗaɗen Fansa

13 hours ago
Next Post
Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

LABARAI MASU NASABA

Buƙatar Daƙile Yawan Ɓacewar Mutane A Nijeriya

Buƙatar Daƙile Yawan Ɓacewar Mutane A Nijeriya

September 12, 2025
Tattalin Arzikin Sin Babban Ginshiki Ne Na Karuwar Tattalin Arzikin Duniya

Tattalin Arzikin Sin Babban Ginshiki Ne Na Karuwar Tattalin Arzikin Duniya

September 12, 2025
Duniya Za Ta Ci Karin Gajiya Daga Karfafuwar Hadin Gwiwar BRICS 

Duniya Za Ta Ci Karin Gajiya Daga Karfafuwar Hadin Gwiwar BRICS 

September 12, 2025
Hasashen Ambaliyar Ruwa: Gwamnatin Kaduna Ta Ƙaddamar Da Shirin Ko-ta-kwana

Hasashen Ambaliyar Ruwa: Gwamnatin Kaduna Ta Ƙaddamar Da Shirin Ko-ta-kwana

September 11, 2025
Sin Ta Kasance Kan Gaba A Yawan Hakkin Mallakar Fasaha A Bangaren Tattalin Arziki Na Dijital

Sin Ta Kasance Kan Gaba A Yawan Hakkin Mallakar Fasaha A Bangaren Tattalin Arziki Na Dijital

September 11, 2025
Gwamnan Kebbi Ya Dakatar da Kwamishinan Ma’aikatar Lafiya Biyo Bayan Sakaci A Aiki

Gwamnan Kebbi Ya Dakatar da Kwamishinan Ma’aikatar Lafiya Biyo Bayan Sakaci A Aiki

September 11, 2025
Za A Gudanar Taron Tattaunawa Karo Na 12 Na Dandalin Xiangshan A Nan Birnin Beijing

Za A Gudanar Taron Tattaunawa Karo Na 12 Na Dandalin Xiangshan A Nan Birnin Beijing

September 11, 2025
Shettima

Shettima Ya Bada Umarnin Gaggauta Raba Lamunin Naira Biliyan 250 Ga Ƙananan Manoma 

September 11, 2025
An Zabi Wuraren Ban Ruwa Hudu Na Kasar Sin Domin Shigar Da Su Jadawalin Wuraren Ban Ruwa Na Kasa Da Kasa

An Zabi Wuraren Ban Ruwa Hudu Na Kasar Sin Domin Shigar Da Su Jadawalin Wuraren Ban Ruwa Na Kasa Da Kasa

September 11, 2025
Rashin Tsaro: Zanga-zanga Ta Ɓarke A Jihar Kogi 

Rashin Tsaro: Zanga-zanga Ta Ɓarke A Jihar Kogi 

September 11, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.