Rundunar Ƴansandan Kaduna ta kama mutane 27 da ake zargi da aikata laifuka bayan farmakin da suka kai wuraren da ake zargin masu laifi ke amfani da su a yankin Kawo. Aikin ya gudana ne da haɗin gwuiwar Sojoji, da DSS, da ƙungiyoyin mafarauta.
Kakakin Ƴansandan jihar, DSP Mansir Hassan, ya bayyana cewa an gudanar da aikin ne a ranar 8 ga Yuni, 2025. An ƙwato tarin makamai kamar wuƙaƙe da gatari, da kuma haramtattan magunguna ciki har da tarbar wiwi.
- An Karrama Dalibar Kaduna Da Ta Zo Ta Biyu A Gasar Karatun Alkur’ani Ta Duniya
- Shugaban Hukumar DSS Ya Kaddamar Da Cibiyar Koyar Da Addinin Musulunci A Kaduna
Kwamishinan Ƴansandan jihar, CP Rabiu Muhammad, ya yaba da haɗin kai tsakanin hukumomin tsaro. Ya tabbatar da cewa ba za a ɗaga ƙafa ga duk wani laifi a jihar ba, inda ya ce aikin wani ɓangare ne na dabarun kawar da ƙungiyoyin masu laifi.
“Kaduna jiha ce mai zaman lafiya kuma muna da azamar ci gaba da kiyaye hakan. Ba za mu ƙyale masu laifi su ɓata wa al’umma zaman lafiya ba,” in ji kwamishinan.
Ya kuma yi kira ga duk wanda ke da niyyar aikata laifuka ya tuba, yana mai tabbatar da cewa ba za a samu mafakar masu laifi a jihar ba.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp