ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

12 Ga Yuni: Muhimman Abubuwan Da Buhari Ya Fada A Jawabinsa Na Ranar Dimokuradiyya

by Muhammad
4 years ago
12

Ranar 12 ga watan Yunin kowacce shekara ake bikin zagayowar Ranar Dimukuradiyya a Nijeriya.

An fara gudanar da bikin wannan rana ce tun daga shekarar 2002, haka kuma shugaba Muhammadu Buhari ya kara wa wannan rana karfi a shekarar 2018 bayan da ya sauya Ranar Dimokuradiyyar daga ranar 29 ga watan Mayu zuwa ranar 12 ga watan Yuni.

  • 12 Ga Yuni: Atiku, Tinubu Da Obi Da Ragowar Wasu Za Su Sanya Furanni A Kabarin Abiola
  • 2023: An Bukaci Tinubu Ya Dora Kan Irin Salon Mulkin Buhari Kwabo Da Kwabo

Aminiya-trust ta wallafa jawabin da shugaba Buhari ya gabatar a safiyar ranar Lahadi, cewa ya soma ne da bayani kan muhimmancin Ranar Dimokuradiyya inda ya jaddada muhimmancin zaben Yunin 1993 a tarihin Nijeriya.

ADVERTISEMENT

Shugaba Buhari ya ce kada ’yan Nijeriya su manta da irin gudunmawa da sadaukar da kai da gawarazan dimokuradiyya suka bayar a 1993.

Ya bukaci ’yan Nijeriya da su yi koyi da kishin kasa irin na magabata a duk lokacin da za su zabi shugabanni.

LABARAI MASU NASABA

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

Shugaban ya sake tuna wa ’yan Nijeriya cewa wannan ce Ranar Dimokuradiyya ta karshe da zai yi a matsayinsa na Shugaban Kasa inda ya ce yana cike da kudirin tabbatar da cewa an zabi sabon shugaban kasa ta hanyar zabe na gaskiya da adalci.

Haka kuma Shugaba Buhari ya yaba da yadda aka gudanar da zaben fitar da gwani a kasar inda ya ce daya daga cikin abin da ya birge shi da zaben shi ne yadda mata da matasa a kusan duka jam’iyyun suka fito neman takara, “wannan alama ce da ke nuna dimokuradiyyar Nijeriya ta kara bunkasa a cikin shekara 23 da aka shafe.

“Yayin da muke shiga kakar yakin neman zabe da kuma zabe na gama gari, kada mu taba daukansa a matsayin wani alamrari na a mutu ko a yi rai, dole ne mu tuna cewa dimokuradiyya ta yi tanadin abin da mafi rinjayen kaso na alumma suke so, saboda haka dole za a samu masu nasara da masu faduwa.

Shugaban ya bayyana cewa a shekara bakwai da ya shafe kan mulki, gwamnatinsa ta yi kokari wurin gyara Dokokin Zabe da yanayin gudanar da zaben domin kare kuri’un al’umma.

Kan dai batun zaben, Shugaba Buhari ya bayyana cewa bangaren Zartarwa da Dokoki da kuma Shari’a na da kudirin ganin sun aiwatar da wadannan sauye-sauye na Dokokin zabe a yayin zaben 2023.

Shugaba Buhari ya kuma bukaci duk ’yan Nijeriya su saka wadanda rikicin ta’addanci ya rutsa da su cikin addu’a, yana mai cewa a kullum yana kwana yana tashi da bakin cikin wadanda aka yi garkuwa da su.

Ya bayar da tabbacin cewa duk hukumomin tsaron kasar na yin duk mai yiwuwa domin ceto wadanda aka sace.

“Na san cewa muna cike da damuwa kan yadda ake fama da kalubale na matsalar tsaro a sakamakon ayyukan ta’addanci, a matsayinmu na gwamnati muna aiki tukuru don shawo kan wadannan kalubale.

“Don ganin an samu biyan wannan bukata, dole kowa ya bayar da gudunmawa. Ba aikin gwamnati ba ne ita kadai, akwai bukatar dukkan yan kasa su ba rika bai wa jamian tsaro hadin kai ta hanyar mika musu rahoton duk wani mutum da ake zargi da aikata laifi ko wani motsi da basu yarda da shi ba.

“Zan karkare wannan jawabi na Ranar Dimokuradiyya, wanda kuma shi na karshe da zan yi a matsayina na Shugaban kasa, ta hanyar tabbatar muku da kudirin da na dauka na kare Najeriya da ‘yan Nijeriya daga dukkan makiya daga ciki da waje.”

Buhari ya rufe jawabansa da Yi Wa Nijeriya Addu’a.

12
Muhammad
+ postsBio
  • Muhammad
    Cikin Shekaru 28, Kudiri Ƙasa Da 10 Sanatocin Zamfara Ta Arewa Suka Gabatar A Majalisa – Shinkafi
  • Muhammad
    2027: NNPP Ta Yi Wa Korarrun Mambobinta Afuwa, Ta Yi Alƙawarin Basu Tikitin Kai-tsaye
  • Muhammad
    Musulunci Na Fuskantar Barazana A Karƙashin Mulkin Tinubu — Datti Baba-Ahmed
  • Muhammad
    Kwankwaso Tamkar Tsuntsu Ne A Siyasa Da Yake Sauya Sheƙa Daga Nan Zuwa Can – Ganduje

MASU ALAKA

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu
Labarai

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi
Labarai

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
Next Post
12 Ga Yuni Sam Ba Ta Dace Da Ranar Dimokradiyya Ba A Nijeriya —Ra’ayin Najib Sani

12 Ga Yuni Sam Ba Ta Dace Da Ranar Dimokradiyya Ba A Nijeriya —Ra'ayin Najib Sani

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.