• Leadership Hausa
Friday, August 19, 2022
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result
Home Labarai

12 Ga Yuni: Muhimman Abubuwan Da Buhari Ya Fada A Jawabinsa Na Ranar Dimokuradiyya

by Muhammad
2 months ago
in Labarai
0
12 Ga Yuni: Muhimman Abubuwan Da Buhari Ya Fada A Jawabinsa Na Ranar Dimokuradiyya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ranar 12 ga watan Yunin kowacce shekara ake bikin zagayowar Ranar Dimukuradiyya a Nijeriya.

An fara gudanar da bikin wannan rana ce tun daga shekarar 2002, haka kuma shugaba Muhammadu Buhari ya kara wa wannan rana karfi a shekarar 2018 bayan da ya sauya Ranar Dimokuradiyyar daga ranar 29 ga watan Mayu zuwa ranar 12 ga watan Yuni.

  • 12 Ga Yuni: Atiku, Tinubu Da Obi Da Ragowar Wasu Za Su Sanya Furanni A Kabarin Abiola
  • 2023: An Bukaci Tinubu Ya Dora Kan Irin Salon Mulkin Buhari Kwabo Da Kwabo

Aminiya-trust ta wallafa jawabin da shugaba Buhari ya gabatar a safiyar ranar Lahadi, cewa ya soma ne da bayani kan muhimmancin Ranar Dimokuradiyya inda ya jaddada muhimmancin zaben Yunin 1993 a tarihin Nijeriya.

Shugaba Buhari ya ce kada ’yan Nijeriya su manta da irin gudunmawa da sadaukar da kai da gawarazan dimokuradiyya suka bayar a 1993.

Ya bukaci ’yan Nijeriya da su yi koyi da kishin kasa irin na magabata a duk lokacin da za su zabi shugabanni.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Nijeriya Na Kashe Naira Biliyan N18.397 Kullum A Bangaren Tallafin Mai

Yadda Aka Sace Kwamishina A Nasarawa

Shugaban ya sake tuna wa ’yan Nijeriya cewa wannan ce Ranar Dimokuradiyya ta karshe da zai yi a matsayinsa na Shugaban Kasa inda ya ce yana cike da kudirin tabbatar da cewa an zabi sabon shugaban kasa ta hanyar zabe na gaskiya da adalci.

Haka kuma Shugaba Buhari ya yaba da yadda aka gudanar da zaben fitar da gwani a kasar inda ya ce daya daga cikin abin da ya birge shi da zaben shi ne yadda mata da matasa a kusan duka jam’iyyun suka fito neman takara, “wannan alama ce da ke nuna dimokuradiyyar Nijeriya ta kara bunkasa a cikin shekara 23 da aka shafe.

“Yayin da muke shiga kakar yakin neman zabe da kuma zabe na gama gari, kada mu taba daukansa a matsayin wani alamrari na a mutu ko a yi rai, dole ne mu tuna cewa dimokuradiyya ta yi tanadin abin da mafi rinjayen kaso na alumma suke so, saboda haka dole za a samu masu nasara da masu faduwa.

Shugaban ya bayyana cewa a shekara bakwai da ya shafe kan mulki, gwamnatinsa ta yi kokari wurin gyara Dokokin Zabe da yanayin gudanar da zaben domin kare kuri’un al’umma.

Kan dai batun zaben, Shugaba Buhari ya bayyana cewa bangaren Zartarwa da Dokoki da kuma Shari’a na da kudirin ganin sun aiwatar da wadannan sauye-sauye na Dokokin zabe a yayin zaben 2023.

Shugaba Buhari ya kuma bukaci duk ’yan Nijeriya su saka wadanda rikicin ta’addanci ya rutsa da su cikin addu’a, yana mai cewa a kullum yana kwana yana tashi da bakin cikin wadanda aka yi garkuwa da su.

Ya bayar da tabbacin cewa duk hukumomin tsaron kasar na yin duk mai yiwuwa domin ceto wadanda aka sace.

“Na san cewa muna cike da damuwa kan yadda ake fama da kalubale na matsalar tsaro a sakamakon ayyukan ta’addanci, a matsayinmu na gwamnati muna aiki tukuru don shawo kan wadannan kalubale.

“Don ganin an samu biyan wannan bukata, dole kowa ya bayar da gudunmawa. Ba aikin gwamnati ba ne ita kadai, akwai bukatar dukkan yan kasa su ba rika bai wa jamian tsaro hadin kai ta hanyar mika musu rahoton duk wani mutum da ake zargi da aikata laifi ko wani motsi da basu yarda da shi ba.

“Zan karkare wannan jawabi na Ranar Dimokuradiyya, wanda kuma shi na karshe da zan yi a matsayina na Shugaban kasa, ta hanyar tabbatar muku da kudirin da na dauka na kare Najeriya da ‘yan Nijeriya daga dukkan makiya daga ciki da waje.”

Buhari ya rufe jawabansa da Yi Wa Nijeriya Addu’a.

ShareTweetSendShare
Previous Post

2023: An Bukaci Tinubu Ya Dora Kan Irin Salon Mulkin Buhari Kwabo Da Kwabo

Next Post

12 Ga Yuni Sam Ba Ta Dace Da Ranar Dimokradiyya Ba A Nijeriya —Ra’ayin Najib Sani

Related

Buhari Ya Ci Alwashin Kawo Karshen Lalacewar Layin Samar Da Wutar Lantarki Na Kasa
Labarai

Gwamnatin Nijeriya Na Kashe Naira Biliyan N18.397 Kullum A Bangaren Tallafin Mai

25 seconds ago
Yadda Aka Sace Kwamishina A Nasarawa
Kananan Labarai

Yadda Aka Sace Kwamishina A Nasarawa

44 mins ago
srilanka
Rahotonni

Darussa Daga Gwagwarmayar Kasar Sri Lanka (Nazari)

2 hours ago
Nunez Ya Jika Wa Liverpool Aiki
Labarai

Nunez Ya Jika Wa Liverpool Aiki

3 hours ago
Kamata Ya Yi Dalibai Su Maka Kungiyar ASUU A Kotu Kan Bata Musu Lokaci—Adamu Adamu
Labarai

Kamata Ya Yi Dalibai Su Maka Kungiyar ASUU A Kotu Kan Bata Musu Lokaci—Adamu Adamu

4 hours ago
Kusan Shekara 100 Da Kafa Asibitin Kutare Na Kano, Amma…
Rahotonni

Kusan Shekara 100 Da Kafa Asibitin Kutare Na Kano, Amma…

5 hours ago
Next Post
12 Ga Yuni Sam Ba Ta Dace Da Ranar Dimokradiyya Ba A Nijeriya —Ra’ayin Najib Sani

12 Ga Yuni Sam Ba Ta Dace Da Ranar Dimokradiyya Ba A Nijeriya —Ra'ayin Najib Sani

LABARAI MASU NASABA

Buhari Ya Ci Alwashin Kawo Karshen Lalacewar Layin Samar Da Wutar Lantarki Na Kasa

Gwamnatin Nijeriya Na Kashe Naira Biliyan N18.397 Kullum A Bangaren Tallafin Mai

August 19, 2022
Yadda Aka Sace Kwamishina A Nasarawa

Yadda Aka Sace Kwamishina A Nasarawa

August 19, 2022
Nadin Kwamishinoni A Kano: Kar A Yi Kitso Da Kwarkwata

Nadin Kwamishinoni A Kano: Kar A Yi Kitso Da Kwarkwata

August 19, 2022
Da Dumi-Duminsa: NBC Ta Soke Lasisin Tashoshin AIT, Silverbird TV Da Wasu 50

Da Dumi-Duminsa: NBC Ta Soke Lasisin Tashoshin AIT, Silverbird TV Da Wasu 50

August 19, 2022
srilanka

Darussa Daga Gwagwarmayar Kasar Sri Lanka (Nazari)

August 19, 2022
Goro

Goron Jumu’a

August 19, 2022
Nunez Ya Jika Wa Liverpool Aiki

Nunez Ya Jika Wa Liverpool Aiki

August 19, 2022
Kamata Ya Yi Dalibai Su Maka Kungiyar ASUU A Kotu Kan Bata Musu Lokaci—Adamu Adamu

Kamata Ya Yi Dalibai Su Maka Kungiyar ASUU A Kotu Kan Bata Musu Lokaci—Adamu Adamu

August 19, 2022
Kusan Shekara 100 Da Kafa Asibitin Kutare Na Kano, Amma…

Kusan Shekara 100 Da Kafa Asibitin Kutare Na Kano, Amma…

August 19, 2022
Son Zuciyar Wasu Tsiraru Ya Haddasa Rashin Tsaro A NIjeriya – Alhaji Ibrahim

Son Zuciyar Wasu Tsiraru Ya Haddasa Rashin Tsaro A NIjeriya – Alhaji Ibrahim

August 19, 2022
ADVERTISEMENT
Advertise with us

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.