• Leadership Hausa
Sunday, June 4, 2023
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: Daga Karshe Dai Tawagar Su Dogara Sun Mara Wa Atiku Baya

by Khalid Idris Doya
6 months ago
in Labarai
0
2023: Daga Karshe Dai Tawagar Su Dogara Sun Mara Wa Atiku Baya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kungiyar jagororin kiristoci da musulmai ‘yan siyasa da suka fito daga jihohin arewa 19 da babban birnin tarayya Abuja sun ayyana goyon bayan dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP a zaben 2023 da ke tafe, Alhaji Atiku Abubakar a matsayin dan takarar da suka cimma matsayar mara wa baya.

Kungiyar wacce ta misalta goyon bayan tikitin takarar Atiku/Okowa a matsayin zabin da ya dace ga dukkanin masu neman adalci ga kowani bangare a kasar nan.

  • Dogara, Babachir Sun Gana Da Shugabannin Kiristoci Don Daukar Matsaya Kan Zaben 2023
  • Rayuwata Na Cikin Hatsari, Ana Kokarin Kashe Ni – Yakubu Dogara

Wannan matsayar na kunshe ne ta cikin wata sanarwar bayan taro da kungiyar jagororin suka yi a Abuja a ranar Juma’a dauke da sanya hannun tsohon shugaban marasa rinjaye na majalisar wakilai Hon. Mohammed Umara Kumalia da Barista Nunge Mele, (SAN) tare da raba kwafinta ga ‘yan jarida a Bauchi.

Idan za ku iya tunawa dai, gungun kiristocin wadanda suke karkashin tawagar su tsohon Kakakin majalisar tarayya, Yakubu Dogara wadanda suka kasance mambobin jam’iyyar APC ne a baya, sun yi ta gwagwarmayar yaki da tikitin Musulmi da Musulmi wanda suka sha alwashin ba za su mara wa dan takarar jam’iyyar APC, Bola Ahmed Tinubu baya ba.

Sanarwar kungiyar ya nemi dukkanin al’ummar Nijeriya da su mara wa PDP baya domin bai wa kowani bangare dama a cikin mulki a maimakon nuna wariya ga kiristoci ta hanyar yin tikiri musulmai biyu da APC ta yi.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Tarayya Na Ganawa Da TUC Kan Cire Tallafin Mai

Hajjin Bana: Adadin Alhazan Nijeriya A Saudiyya A Yanzun Ya kai 24,324 

Sun yi tilawar cewa, kungiyar jagororin kiristoci da musulmai a arewa ta kafa wani kwamiti a ranar 8 ga watan Oktoba domin ya yi nazarin dan takarar da ya dace a mara wa baya cikin manyan ‘yan takarar shugaban kasa a zaben 2023 da ke tafe.

Kungiyar ta ce, a bisa nazarinta da bincikenta, tikitin takarar Atiku Abubakar na PDP ne kawai ya fi zama a’ala ga dukkanin al’ummar Nijeriya, kuma shine wanda ya fi dacewa a duk cikin manyan ‘yan takarar shugaban kasa guda hudu da suke nema a halin yanzu.

Daga bisani kungiyar sun sha alwashin cewa za su kasa su tsare har sai sun tabbatar APC ba ta samu nasara a zaben 2023 ba, domin a cewarsu an kitsa rashin adalci ga al’ummar kiristoci a yadda aka fitar da tsarin tikitin jam’iyyar.

Tags: 2023Dogara
ShareTweetSendShare
Previous Post

Alfanun Noman Gyada Wajen Habaka Tattalin Arzikin Kasa 

Next Post

Manoman Alkama Sun Koka A Kan Rashin Samun Iri 

Related

Gwamnatin Tarayya Na Ganawa Da TUC Kan Cire Tallafin Mai
Labarai

Gwamnatin Tarayya Na Ganawa Da TUC Kan Cire Tallafin Mai

12 mins ago
Hajjin Bana: Adadin Alhazan Nijeriya A Saudiyya A Yanzun Ya kai 24,324 
Labarai

Hajjin Bana: Adadin Alhazan Nijeriya A Saudiyya A Yanzun Ya kai 24,324 

1 hour ago
Ana Bin Jihar Kano Bashin Sama Da Naira Biliyan 240, Inji Abba Gida-gida 
Labarai

Gwamna Yusuf Ya Kori Jami’an Cibiyar Alhazan Kananan Hukumomi 44 Na Jihar Kano

3 hours ago
Ranar Muhalli Ta Duniya: Kwanturolan NIS Na Jihar Ribas Ya Gargadi Jami’ai Kan Gurbata Muhalli
Labarai

Ranar Muhalli Ta Duniya: Kwanturolan NIS Na Jihar Ribas Ya Gargadi Jami’ai Kan Gurbata Muhalli

5 hours ago
Mutane 18 Sun Mutu A Wani Hatsarin Mota A Kano
Manyan Labarai

Mutane 18 Sun Mutu A Wani Hatsarin Mota A Kano

6 hours ago
Shanun Buhari Sun Ragu Saboda Yawan Kyautarsa — Garba Shehu
Manyan Labarai

Shanun Buhari Sun Ragu Saboda Yawan Kyautarsa — Garba Shehu

12 hours ago
Next Post
Manoman Alkama Sun Koka A Kan Rashin Samun Iri 

Manoman Alkama Sun Koka A Kan Rashin Samun Iri 

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Na Ganawa Da TUC Kan Cire Tallafin Mai

Gwamnatin Tarayya Na Ganawa Da TUC Kan Cire Tallafin Mai

June 4, 2023
‘Yan Sama Jannati Na Kumbon Shenzhou-15 Sun Dawo Beijing

‘Yan Sama Jannati Na Kumbon Shenzhou-15 Sun Dawo Beijing

June 4, 2023
Hajjin Bana: Adadin Alhazan Nijeriya A Saudiyya A Yanzun Ya kai 24,324 

Hajjin Bana: Adadin Alhazan Nijeriya A Saudiyya A Yanzun Ya kai 24,324 

June 4, 2023
Tawagar Sojin Injiniya Ta Wanzar Da Zaman Lafiya Ta Kasar Sin Ta Tallafawa Kongo Kinshasa Ta Fuskar Aikin Ceto

Tawagar Sojin Injiniya Ta Wanzar Da Zaman Lafiya Ta Kasar Sin Ta Tallafawa Kongo Kinshasa Ta Fuskar Aikin Ceto

June 4, 2023
Ana Bin Jihar Kano Bashin Sama Da Naira Biliyan 240, Inji Abba Gida-gida 

Gwamna Yusuf Ya Kori Jami’an Cibiyar Alhazan Kananan Hukumomi 44 Na Jihar Kano

June 4, 2023
Me Ya Sa BRICS Ke Kara Samun Karbuwa Daga Kasashen Duniya

Me Ya Sa BRICS Ke Kara Samun Karbuwa Daga Kasashen Duniya

June 4, 2023
Sana’ar Kwalliya

Sana’ar Kwalliya

June 4, 2023
Ranar Muhalli Ta Duniya: Kwanturolan NIS Na Jihar Ribas Ya Gargadi Jami’ai Kan Gurbata Muhalli

Ranar Muhalli Ta Duniya: Kwanturolan NIS Na Jihar Ribas Ya Gargadi Jami’ai Kan Gurbata Muhalli

June 4, 2023
Mutane 18 Sun Mutu A Wani Hatsarin Mota A Kano

Mutane 18 Sun Mutu A Wani Hatsarin Mota A Kano

June 4, 2023
Takaitaccen Tarihin Ka’idojin Rubutun Hausa (II)

Takaitaccen Tarihin Ka’idojin Rubutun Hausa (II)

June 4, 2023
Advertise with us

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.