ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: Daga Karshe Dai Tawagar Su Dogara Sun Mara Wa Atiku Baya

by Khalid Idris Doya
4 years ago
2023

Kungiyar jagororin kiristoci da musulmai ‘yan siyasa da suka fito daga jihohin arewa 19 da babban birnin tarayya Abuja sun ayyana goyon bayan dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP a zaben 2023 da ke tafe, Alhaji Atiku Abubakar a matsayin dan takarar da suka cimma matsayar mara wa baya.

Kungiyar wacce ta misalta goyon bayan tikitin takarar Atiku/Okowa a matsayin zabin da ya dace ga dukkanin masu neman adalci ga kowani bangare a kasar nan.

  • Dogara, Babachir Sun Gana Da Shugabannin Kiristoci Don Daukar Matsaya Kan Zaben 2023
  • Rayuwata Na Cikin Hatsari, Ana Kokarin Kashe Ni – Yakubu Dogara

Wannan matsayar na kunshe ne ta cikin wata sanarwar bayan taro da kungiyar jagororin suka yi a Abuja a ranar Juma’a dauke da sanya hannun tsohon shugaban marasa rinjaye na majalisar wakilai Hon. Mohammed Umara Kumalia da Barista Nunge Mele, (SAN) tare da raba kwafinta ga ‘yan jarida a Bauchi.

ADVERTISEMENT

Idan za ku iya tunawa dai, gungun kiristocin wadanda suke karkashin tawagar su tsohon Kakakin majalisar tarayya, Yakubu Dogara wadanda suka kasance mambobin jam’iyyar APC ne a baya, sun yi ta gwagwarmayar yaki da tikitin Musulmi da Musulmi wanda suka sha alwashin ba za su mara wa dan takarar jam’iyyar APC, Bola Ahmed Tinubu baya ba.

Sanarwar kungiyar ya nemi dukkanin al’ummar Nijeriya da su mara wa PDP baya domin bai wa kowani bangare dama a cikin mulki a maimakon nuna wariya ga kiristoci ta hanyar yin tikiri musulmai biyu da APC ta yi.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

Sun yi tilawar cewa, kungiyar jagororin kiristoci da musulmai a arewa ta kafa wani kwamiti a ranar 8 ga watan Oktoba domin ya yi nazarin dan takarar da ya dace a mara wa baya cikin manyan ‘yan takarar shugaban kasa a zaben 2023 da ke tafe.

Kungiyar ta ce, a bisa nazarinta da bincikenta, tikitin takarar Atiku Abubakar na PDP ne kawai ya fi zama a’ala ga dukkanin al’ummar Nijeriya, kuma shine wanda ya fi dacewa a duk cikin manyan ‘yan takarar shugaban kasa guda hudu da suke nema a halin yanzu.

Daga bisani kungiyar sun sha alwashin cewa za su kasa su tsare har sai sun tabbatar APC ba ta samu nasara a zaben 2023 ba, domin a cewarsu an kitsa rashin adalci ga al’ummar kiristoci a yadda aka fitar da tsarin tikitin jam’iyyar.

2023
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Yaro Ya Harbe Kansa Har Lahira Bayan Mafarauci Ya Yi Sakaci Da Bindigarsa A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    An Kama Mutane 5 Da Sassan Jikin Ɗan’Adam Za Su Yi Tsafi A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mai Neman Takarar Gwamnan Bauchi, Bala Jibrin, Ya Fice Daga APC Kan Zargin Ɗoki-ɗora
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ‘Yansanda Sun Cafke Tsoho Mai Shekara 70 Kan Zargin Yi Wa ‘Yar Shekara 8 Fyaɗe A Bauchi

MASU ALAKA

'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina
Labarai

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare
Labarai

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Next Post
Manoman Alkama Sun Koka A Kan Rashin Samun Iri 

Manoman Alkama Sun Koka A Kan Rashin Samun Iri 

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.