ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Alfanun Noman Gyada Wajen Habaka Tattalin Arzikin Kasa 

by Abubakar Abba
4 years ago
Gyada

Nijeriya na daga cikin kasashen da kan gaba wajen noman gyada a nahiyar Afirka, kuma ta hudu a cikin jeren kasashen dunya da ake noman gyadar.

Kasar na noma kimain tan miliyan 1.5 na gyadar a duk shekara, inda kuma ake sarrafa man da ake samu daga cikinta,don amfanin yau da kullum.

  • An Yi Atisayen Karshe Na Dukkan Fannoni Don Share Fagen Karbar Kumbon Shenzhou-14
  • An Shiga Firgici: ’Yan Bindiga Sun Cinna Wa Fadar Iree Wuta A Osun

Kiyasin da aka yi, shi ne, idan ka noma gyada a Nijeriya, a kadada daya, idan aka matse ta, za a iya samun mai daga gyadar gydadar da zai kai kimanin lita 500.

ADVERTISEMENT

Ta fuskan tattalin arzikin kasa, noman na samar da ayyukan yi ga dimbin al’ummar kasa da habaka tattalin arzikin kasa.

Ana samun kudi mai yawa daga man da aka tatsa na gyada kuma sannan kuma ana samun kudaden shiga daga gyadar da aka noma. A shekarun da suka wuce, gwamnatin kasar nan, na bai wa fannin na sarrafa gyadar mahimmanci sosai.

LABARAI MASU NASABA

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu

Abubuwan Da Ake Bukata Ka Tanada Kafin Fara Tatsar Man Gyada:

Da farko dai, ana bukatar tabbatar da ka yi rijista da hukumar kula da ingancin abinci ta kasa (NAFDAC), za ka kuma dinga tuntubar kamfanin da ke cikin wannana sana’a, domin su dinga ba ka shawara.

Zuba Jari:

Bayan ka yi wa kamfanin rijista da hukumar ta (NAFDAC), hakan ya nuna a zahiri cewa, ka shirya shiga cikin aiji ke nan gadan-gadan ta hanyar zuba jarin naka. Za ka iya sayo kayan da za ka yi wannan aiki.

Mallakar Gyadar:

Abin farko da za ka fara tanada shi ne, gyadar, an fi yin nomanta, a Areawacin kasar nan da yankin Afirka maso yamma.

A Nijeiya, jihohin da aka fi yin noman gyada sun hada da,Kano da Kaduna da Taraba da Bauchi da Borno da Adamawa, inda wadannan jihohin, ke noman da yawan ta ya kai kimanin kashi 83 a cikin dari zuwa kashi 88.

Kayan Da Aka Fi Aikin Da Su: Kayan da ake fi yin aikin na tatsar man gyadan sun hada da, injin yin aikin.

Jarin Da Za Ka Zuba A Fannin: Ga wanda yake karamin dan kasuwa zai iya fara wa da kimanin naira miliyan 10.5 zuwa naira miliyan 15, amma ga wanda yake yana da kudi da yawa don shiga fannin, zai iya fara wa da naira miliyan 25 zuwa naira miliayan 65.

Yawan Ribar Da Ake Samu A Fannin: Ga wanda yake karami a fannin, zai iya samun ribar da ta kai ta naira miliyan 15 zuwa naira miliyan 22; inda kuma wanda shi mai karfi ne a fannin, zai iya samun kudaden shiga da su kai kimanin daga naira miliyan 35 zuwa naora miliyan 70.

Gyada
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari A Kan Wasu Cututtuka Da Ke Shafar Dabbobi Lokacin Damina
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ɗantsoho Ya Jinjina Wa Hukumar FCC Kan Sabbin Sauye-Sauyen Da Ta Samar
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    “Mutunta Ƴancin Addinai Ita Ce Hanyar Wanzar Da Zaman Lafiya A Kaduna”

MASU ALAKA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Noma Da Kiwo

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

July 11, 2026
Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu
Noma Da Kiwo

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu

July 4, 2026
Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana
Noma Da Kiwo

Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana

July 3, 2026
Next Post
2023: Daga Karshe Dai Tawagar Su Dogara Sun Mara Wa Atiku Baya

2023: Daga Karshe Dai Tawagar Su Dogara Sun Mara Wa Atiku Baya

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.