ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Manoman Alkama Sun Koka A Kan Rashin Samun Iri 

by Abubakar Abba
4 years ago
Alkama

A yayain da ake shirye-shiryen fara shukar alkama daga yanzu zuwa tsakiyar watan Dismba, manoman alkama a kasar nan, sun koka kan rashin samun iri.

A duk watan Dimsambar kowace shekara ce, manoman ke fara shirye-shiryen shukar alkamar, inda suka yi nuni da cewa, matsalar za ta iya shafar burin da suke da shi na samun amfani mai yawa, inda kuma hakan, zai kara janyo a samu wawagegen gibi na bukatar da ake da ita ta alkamar a kasar nan da ta kai fiye da tan miliayn 4.1.

  • Yadda Ake Cin Gajiyar ‘Google Drive’ Wajen Amfani Da Kwanfuta
  • Dalibin Da Ya Tsokani Aisha, Zai Gana Da Buhari A Villa

Wasu daga cikin maoman alkamar da aka tattauna da su a jihar Katsina sun bayyana cewa, duk da irin tsadar farashin takin zamani don yin noman na alkamar, sun nuna aniyarsu ta fara shukar alkamar a kan lokaci, domin su cike gibin da suka samu bara.

ADVERTISEMENT

Daya daga cikin manoman na alkamar a jihar Katsaina Malam Murtala Mairuwa, ya koka kan rashin tallafin da manoman alkamar ba sa samu daga gwamnati, inda ya yi nuni da cewa, koda za su samu tallafin daga gun gwamnatin, ya an zuwa ne a makare

Sai dai, Mairuwa, ya ci gaba da cewa, kakar alkama a shekarar da ta wuce, gwamnatin ta samar wa da manoman dauki ta hanyar babban bankin Nijeriya CBN, musamman ta hanyar samar da takin zamani da sauran kayan aikin alkamar.

LABARAI MASU NASABA

Kha’amuna Khadi Ta Karɓi Jagorancin Gudanarwa Ta Bankin Noma

Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya

A cewarsa, kamata ya yi a fara shuka Alkamar akalla daga cikin watan Nuwamba, inda hakan zai baiwa manomin ta damar samun yin girbin ta da dama, inda ya kara da cewa, ko a shekarar da ta wuce, an rabawar da manomanta da kayan aikin ne a cikin watan Disamba.

Mairuwa ya kara da cewa, wata matsalar da manoman ta ke fuskanta shine yadda ake samun wasu marsa kishi kuma wadanda suka kasance ba manonta ba, ke dakile zuwan daukin na gwamnatin ga ainahin manoman da ke yin nomanta.

Har ila yau, a cikin karamar hukumar Bakori da ke a cikin jihar Katsina, akasarin manomanta sun dogara ne akan samun ruwa daga kogin Jare domin yin noman ranin ta, inda daya daga cikin manoman nata Abdurrahman Kabir ya sanar da cewa, a kakar noman ta a wannan shekarra, ba a samu yawan ruwan sama da ake bukata ba

A cewar Kabir, manoman na alkamar a wannan shekarar, na fusntar kalubalen tsadar farashin kayan aikin na Alkamar, musamman idan aka yi la’akari da kudaden da suke kashewa wajen sayen man fetur domin yin ban ruwa.

An ce yanzu haka, farshin buhu day na alkamar mai nauyin kilo 100, ana sayar da shi kan naira 48,500 a kasuwar ta Bakori, inda kuma wasu sun ce, farshin ya kai sama da naira 50,000.

Har ila yau, a jihar Kano kuwa an ce, tuni wasu manoman alkamar suka fara koma wa gona domin fara yin aiki gadn-gadan, amma sai dai, abin takaici har yanzu ba su iya samun iri ba da kuma samun sauran dauki a fannin.

Biyo bayan wani bincike da aka gudanar sama da shekarun da suka wuce, alkasrin namoman na Alkamar sun fi dogara ne da samun Irin daga gun kafanonin da ke samar da irin domin sayawar da manoman.

A cewar wasu daga cikin manoman, tun lokacin da hukumar gudanar da bincike aikin noma da ke tabkin Chadi ta dakatar da raba da ingantaccen irin, an bar manoman da fafutukar nemo irin da ya dace.

Wani manominta a jihar Kano Alhaji Surajo Bello ya bayyana cewa, duk da karancin da ake fuskanta na alkamar a fadin duniya, a wannan shekarar, ba su samu daukin gwamnatin tarayya ta hanyar shirin noma na Anchor Borrower ba.

Ya ce, abin takaice ne ganin cewa duk da an sa manoman na Alkamar a cikin jeren manoman da za su amfana da daukin na babban bankin Nijeriya CBN, amma ba sa samun daukin.

Shi ma wani manoman na alkamar, Alhaji Musa Mu’azu Garun Babba ya sanar da cewa, shekaru da dama da suka wuce, an bar manoman na alkamar ne kawai suna sayen irin daga gun kamfanin da ke samar da irin.

Alkama
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Tun Ina Karama Marigayi Tumbuleke Ke Sa Ni Dariya —Hannatu Musawa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    NPA Ta Bayyana Cewa Kirkiro Da Sabuwar Hukumar NPERA Ba Zai Zame Mata Tarnaki Ba
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Yadda Bikin Girke-girke Ya Karfafa Alaka Tsakanin Musulmai Da Kiristoci A Kaduna
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari Kan Wasu Dalilan Da Ke Haddasa Sabanin Abotakar Jarumi Ko Jaruma A Kannywood

MASU ALAKA

Abin Da Ya Sa Gidauniyar NADF Da Bankin Manoma Suka Yi Haḍaka
Noma Da Kiwo

Kha’amuna Khadi Ta Karɓi Jagorancin Gudanarwa Ta Bankin Noma

August 1, 2026
Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya
Noma Da Kiwo

Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya

July 18, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Noma Da Kiwo

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

July 11, 2026
Next Post
Tsaron Iyakoki: NIS Ta Yaye  Zaratan Jami’ai Mata Masu Ɗaukar Makami A Karon Farko

Tsaron Iyakoki: NIS Ta Yaye  Zaratan Jami’ai Mata Masu Ɗaukar Makami A Karon Farko

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.