• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: Dallinmu Na Wallafa Kuri’un Zaben Shugaban Kasa Miliyan 187 –INEC

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
2023: Dallinmu Na Wallafa Kuri’un Zaben Shugaban Kasa Miliyan 187 –INEC
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Yayin da ya rake kasa da kwanaki 100 a gudanar da babban zaben 2023, hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) ta bayyana cewa ta tanadi takardun jefa kuri’a na shugaban kasa guda miliyan 187, domin shirin zabe zagaye na biyu idan hakan ta kama.

Kakakin hukumar INEC, Festus Okoye shi ya bayyana hakan a wata ganawa da ya yi da manema labarai a Abuja.

  • Zamanintar Da Sha’anin Gona Da Kauyuka Ya Dogaro Da Halin Da Ake Ciki Da Muradun Jama’a
  • Nnamdi Kanu Ya Maka Gwamnatin Tarayya A Kotun Koli 

Oke ya ce ‘yan Nijeriya miliyan 93.5 ne za su yi zabe, amma INEC ta rubanya takardun jefa kuri’a har suka kai miliyan 187 ko da za a kai ga yin zabe zageye na biyu idan ba a samu wanda ya lashe zaben ba a farkon lokaci.

Ya ce a bisa al’adar hukumar INEC tana irin wannan shirin a duk lokacin da za a gudanar da zaben shugaban kasa tun daga shekarar 1999.

Okoye ya ce za a fara amfani da takardun jefa kuri’a miliyan 93.5 ne a ranar 25 ga watan Fabrairun 2023, lokacin da za a gudanar da zaben shugaban kasa, yayin da sauran takardun jefa kuri’a miliyan 93.5 an tanade su ne domin shirin gudunar da zabe zagaye na biyu idan har babu wanda ya yi nasara a zagayen farko.

Labarai Masu Nasaba

Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027

Amfani Da Karfin Gwamnati Kan ‘Yan Adawa Zai Jawo Wa Tinubu Illa A 2027 – Sule Lamido

Kakakin ya ce hukumar ta yanke hukuncin buga takardun jefa kuri’un miliyan 187 na shugaban kasa ne, domin zai yi mata wahala ta buga kuri’un cikin karamin lokaci.

Okoye ya ce, “A yanzu muna da jam’iyyun siyasa 18 da za su shiga cikin zaben 2023, sannan doka ta tanadi yadda za a tsayar da ‘yan takara har ma a samu wanda zai zama shugaban Nijeriya. Sakamakon karancin lokaci da doka ta bai wa hukumar INEC idan har ba a samu dan takarar da ya yi nasara a zagayen farko ba, sai hukumar ta dauki matakin buga kuri’un na zageye na biyu a lokacin da muke buga takardun zabe.

“Idan har ‘yan Nijeriya miliyan 93 za su yi zaben shugaban kasa, to za mu kara buga karin kuri’u miliyan 93 saboda zagaye na biyu idan har ba a samu wanda ya yi nasara ba.

“Daga karshe idan har ba a shiga zagaye na biyu ba, to hukumar INEC za ta lalata kuri’u miliyan 93 da ta buga saboda zagaye na biyu. Wannan yana faruwa ne saboda doka ya bai wa hukumar kwanaki 21 kacal wajen shirya zabe na biyu idan har babu wanda ya samu nasara a zagayen farko.”

Da yake bayyana yadda za a samu shugaban kasa da sharuddan da suka kamata na zabe zagaye na biyu, Okeye ya ce, “Sashi na 134 (2) na tsarin mulkin tarayyar Nijeriya wanda shi ne dokar kasa ya tilasta cewa wajibi ne duk wanda zai zama shugaban kasan Nijeriya ya fi sauran ‘yan takara yawan kuri’u. Kuma tilas ya samu akalla kashi 1/4 na kashi 2 bisa bisa 3 na kuri’un da aka kada a jihohi 36 ciki har da Abuja.

“Idan har babu dan takarar da ya samu yawan kuri’un da ake bukata, tsarin mulki ya tanadi cewa dole mu shirya zabe zagaye na biyu a cikin kwanaki 21. Ba dukkan ‘yan takara ba ne za su shiga zabe zagaye na biyu ba. ‘Yan takara 18 ne ke cikin takardun jefa kuri’a na zagaye na farko. Idan ba a samu wanda ya yi nasara a zagayen farko ba, ‘yan takara guda biyu ne kacal za su shiga zagaye na biyu.

“Na farko shi ne wanda ya fi kowa yawan kuri’u, amma ya kasa samun akalla kashi 1/4 daga kashi 2 bisa 3 na yawan kuri’un jihohi ciki har da Abuja. Sai kuma na biyun wanda zai yi zagaye na biyun shi ne, ya zo na biyu wajen samun kashi 1/4 na kashi 3 bisa 4 na kuri’un da aka kada a jihohi da ciki har da Abuja.

“Dole ne mu buga kuri’un babban zabe da na zagaye na biyu a lokaci guda, domin haka hukumar INEC ta saba yi.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: INECKuri'u.Mahmoud
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Shirya Bikin Tunawa Da Iyali Kan Kisan Kiyashin Da Aka Yi Nanjing

Next Post

2023: Ba Zan Taba Janye Wa Kowa Ba –Kwankwaso

Related

Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027
Tambarin Dimokuradiyya

Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027

2 weeks ago
Wallafa
Tambarin Dimokuradiyya

Amfani Da Karfin Gwamnati Kan ‘Yan Adawa Zai Jawo Wa Tinubu Illa A 2027 – Sule Lamido

2 weeks ago
‘Yan Siyasa Na Gwagwarmaya Ne Kadai Wajen Neman Mukami Ba Wai Don Talakawa Ba — Bafarawa
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Siyasa Na Gwagwarmaya Ne Kadai Wajen Neman Mukami Ba Wai Don Talakawa Ba — Bafarawa

2 weeks ago
Gwamnoni 9 Da Har Yanzu Ba Su Babe Da Iyayen Gidansu Ba
Tambarin Dimokuradiyya

Jihohi Sun Samu Naira Tiriliyan 1 Na Kudaden Kananan Hukumomi A Zango Na Daya

3 weeks ago
2027: Baba-Ahmed Ya Bukaci Tinubu Ya Janye, Ya Bar Matasa Su Yi Takara 
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Babu Dan Takarar Da Zai Iya Cin Zabe Ba Tare Da Goyon Bayan Arewa Ba – Baba Ahmed

3 weeks ago
arewa
Tambarin Dimokuradiyya

Kawunan Shugabannin Arewa Sun Rabu Kan Siyasar 2027

3 weeks ago
Next Post
2023: Ba Zan Taba Janye Wa Kowa Ba –Kwankwaso

2023: Ba Zan Taba Janye Wa Kowa Ba –Kwankwaso

LABARAI MASU NASABA

Shugaba Xi Ya Amsa Wasikar Da Jagoran Da Ya Kafa Majalisar Cinikayya Ta Denmark A Sin Ya Aike Masa

Shugaba Xi Ya Amsa Wasikar Da Jagoran Da Ya Kafa Majalisar Cinikayya Ta Denmark A Sin Ya Aike Masa

May 15, 2025
An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi

An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi

May 15, 2025
NNPP Ta Tafka Asara, Ƴan Majalisa 2 Daga Kano Sun Koma APC

NNPP Ta Tafka Asara, Ƴan Majalisa 2 Daga Kano Sun Koma APC

May 15, 2025
Ya Kamata A Kori Ministan Ilimi – Aisha Yesufu

Ya Kamata A Kori Ministan Ilimi – Aisha Yesufu

May 15, 2025
Lassa Da Shawara Sun Kashe Mutum 183 A Jihohi 36 Da Abuja

Lassa: Mutane 138 Sun Rasu, 717 Sun Kamu A Jihohi 18 – NCDC

May 15, 2025
Wa Suka Fi Cancanta A Nada Ministocin Tinubu?

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Dakarun Da Za Suke Tsaron Daji Don Yaƙar ‘Yan Ta’adda

May 15, 2025
ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

May 15, 2025
‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

May 15, 2025
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

’Yan Bindiga Sun Sace Mutane 200 A Mazaɓa Ta A Zamfara – Ɗan Majalisar Tarayya

May 15, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutane 9 Kan Kisan Jigon Jam’iyyar PDP A Adamawa

May 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.