• English
  • Business News
Saturday, July 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: Dallinmu Na Wallafa Kuri’un Zaben Shugaban Kasa Miliyan 187 –INEC

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
2023: Dallinmu Na Wallafa Kuri’un Zaben Shugaban Kasa Miliyan 187 –INEC
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Yayin da ya rake kasa da kwanaki 100 a gudanar da babban zaben 2023, hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) ta bayyana cewa ta tanadi takardun jefa kuri’a na shugaban kasa guda miliyan 187, domin shirin zabe zagaye na biyu idan hakan ta kama.

Kakakin hukumar INEC, Festus Okoye shi ya bayyana hakan a wata ganawa da ya yi da manema labarai a Abuja.

  • Zamanintar Da Sha’anin Gona Da Kauyuka Ya Dogaro Da Halin Da Ake Ciki Da Muradun Jama’a
  • Nnamdi Kanu Ya Maka Gwamnatin Tarayya A Kotun Koli 

Oke ya ce ‘yan Nijeriya miliyan 93.5 ne za su yi zabe, amma INEC ta rubanya takardun jefa kuri’a har suka kai miliyan 187 ko da za a kai ga yin zabe zageye na biyu idan ba a samu wanda ya lashe zaben ba a farkon lokaci.

Ya ce a bisa al’adar hukumar INEC tana irin wannan shirin a duk lokacin da za a gudanar da zaben shugaban kasa tun daga shekarar 1999.

Okoye ya ce za a fara amfani da takardun jefa kuri’a miliyan 93.5 ne a ranar 25 ga watan Fabrairun 2023, lokacin da za a gudanar da zaben shugaban kasa, yayin da sauran takardun jefa kuri’a miliyan 93.5 an tanade su ne domin shirin gudunar da zabe zagaye na biyu idan har babu wanda ya yi nasara a zagayen farko.

Labarai Masu Nasaba

2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

Kirkirar Sabbin Jihohi Da Kananan Hukumomi Sun Dabaibaye Sauraron Jin Ra’ayoyin Gyaran Tsarin Mulki

Kakakin ya ce hukumar ta yanke hukuncin buga takardun jefa kuri’un miliyan 187 na shugaban kasa ne, domin zai yi mata wahala ta buga kuri’un cikin karamin lokaci.

Okoye ya ce, “A yanzu muna da jam’iyyun siyasa 18 da za su shiga cikin zaben 2023, sannan doka ta tanadi yadda za a tsayar da ‘yan takara har ma a samu wanda zai zama shugaban Nijeriya. Sakamakon karancin lokaci da doka ta bai wa hukumar INEC idan har ba a samu dan takarar da ya yi nasara a zagayen farko ba, sai hukumar ta dauki matakin buga kuri’un na zageye na biyu a lokacin da muke buga takardun zabe.

“Idan har ‘yan Nijeriya miliyan 93 za su yi zaben shugaban kasa, to za mu kara buga karin kuri’u miliyan 93 saboda zagaye na biyu idan har ba a samu wanda ya yi nasara ba.

“Daga karshe idan har ba a shiga zagaye na biyu ba, to hukumar INEC za ta lalata kuri’u miliyan 93 da ta buga saboda zagaye na biyu. Wannan yana faruwa ne saboda doka ya bai wa hukumar kwanaki 21 kacal wajen shirya zabe na biyu idan har babu wanda ya samu nasara a zagayen farko.”

Da yake bayyana yadda za a samu shugaban kasa da sharuddan da suka kamata na zabe zagaye na biyu, Okeye ya ce, “Sashi na 134 (2) na tsarin mulkin tarayyar Nijeriya wanda shi ne dokar kasa ya tilasta cewa wajibi ne duk wanda zai zama shugaban kasan Nijeriya ya fi sauran ‘yan takara yawan kuri’u. Kuma tilas ya samu akalla kashi 1/4 na kashi 2 bisa bisa 3 na kuri’un da aka kada a jihohi 36 ciki har da Abuja.

“Idan har babu dan takarar da ya samu yawan kuri’un da ake bukata, tsarin mulki ya tanadi cewa dole mu shirya zabe zagaye na biyu a cikin kwanaki 21. Ba dukkan ‘yan takara ba ne za su shiga zabe zagaye na biyu ba. ‘Yan takara 18 ne ke cikin takardun jefa kuri’a na zagaye na farko. Idan ba a samu wanda ya yi nasara a zagayen farko ba, ‘yan takara guda biyu ne kacal za su shiga zagaye na biyu.

“Na farko shi ne wanda ya fi kowa yawan kuri’u, amma ya kasa samun akalla kashi 1/4 daga kashi 2 bisa 3 na yawan kuri’un jihohi ciki har da Abuja. Sai kuma na biyun wanda zai yi zagaye na biyun shi ne, ya zo na biyu wajen samun kashi 1/4 na kashi 3 bisa 4 na kuri’un da aka kada a jihohi da ciki har da Abuja.

“Dole ne mu buga kuri’un babban zabe da na zagaye na biyu a lokaci guda, domin haka hukumar INEC ta saba yi.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: INECKuri'u.Mahmoud
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Shirya Bikin Tunawa Da Iyali Kan Kisan Kiyashin Da Aka Yi Nanjing

Next Post

2023: Ba Zan Taba Janye Wa Kowa Ba –Kwankwaso

Related

2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

6 hours ago
majalisar kasa
Tambarin Dimokuradiyya

Kirkirar Sabbin Jihohi Da Kananan Hukumomi Sun Dabaibaye Sauraron Jin Ra’ayoyin Gyaran Tsarin Mulki

7 hours ago
Ko Yanzu Tinubu Ya Yi Rawar Gani, Kuma Yana Ƙoƙari Sosai – Buhari
Rahotonni

Muhimman Abubuwa 10 Da Kowa Zai So Ya Sani Game Da Marigayi Shugaban Ƙasa Buhari

5 days ago
Kashim Shettima Ya Mayar Da Martani Kan Tsadar Rayuwa
Tambarin Dimokuradiyya

Rashin Ganin Shugabannin APC Yayin Ziyarar Shettima A Kano Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

7 days ago
Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya
Tambarin Dimokuradiyya

Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya

1 week ago
Nijeriya Na Fuskantar Siyasa Mara Tabbas —  Peter Obi
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Takarar Shugaban Kasa Zan Yi Ba Mataimaki Ba – Peter Obi

1 week ago
Next Post
2023: Ba Zan Taba Janye Wa Kowa Ba –Kwankwaso

2023: Ba Zan Taba Janye Wa Kowa Ba –Kwankwaso

LABARAI MASU NASABA

Dangote

Dalilin Da Ya Sa Dangote Ya Jinjina Wa Hukumar NPA

July 18, 2025
Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin

Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin

July 18, 2025
2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

July 18, 2025
Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi

Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi

July 18, 2025
majalisar kasa

Kirkirar Sabbin Jihohi Da Kananan Hukumomi Sun Dabaibaye Sauraron Jin Ra’ayoyin Gyaran Tsarin Mulki

July 18, 2025
Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Zambia Da Ci 5-0

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Zambia Da Ci 5-0

July 18, 2025
Yawan Jarin Waje Da Sin Ta Samu Ya Haura Dalar Amurka Biliyan 700

Yawan Jarin Waje Da Sin Ta Samu Ya Haura Dalar Amurka Biliyan 700

July 18, 2025
A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya

A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya

July 18, 2025
Biyan Tukuici: Gwamna Yusuf Ya Ƙaddamar Da Tallafin Naira 50,000 Ga Mata 5,200 Duk Wata A Kano

Biyan ‘Yan Fansho Naira Biliyan 22: NUP Da NLC Sun Bukaci A Yi Koyi Da Gwamna Abba

July 18, 2025
Sin Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ta Kai Syria

Sin Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ta Kai Syria

July 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.