• English
  • Business News
Sunday, October 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: Dallinmu Na Wallafa Kuri’un Zaben Shugaban Kasa Miliyan 187 –INEC

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
Wallafa

Yayin da ya rake kasa da kwanaki 100 a gudanar da babban zaben 2023, hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) ta bayyana cewa ta tanadi takardun jefa kuri’a na shugaban kasa guda miliyan 187, domin shirin zabe zagaye na biyu idan hakan ta kama.

Kakakin hukumar INEC, Festus Okoye shi ya bayyana hakan a wata ganawa da ya yi da manema labarai a Abuja.

  • Zamanintar Da Sha’anin Gona Da Kauyuka Ya Dogaro Da Halin Da Ake Ciki Da Muradun Jama’a
  • Nnamdi Kanu Ya Maka Gwamnatin Tarayya A Kotun Koli 

Oke ya ce ‘yan Nijeriya miliyan 93.5 ne za su yi zabe, amma INEC ta rubanya takardun jefa kuri’a har suka kai miliyan 187 ko da za a kai ga yin zabe zageye na biyu idan ba a samu wanda ya lashe zaben ba a farkon lokaci.

Ya ce a bisa al’adar hukumar INEC tana irin wannan shirin a duk lokacin da za a gudanar da zaben shugaban kasa tun daga shekarar 1999.

Okoye ya ce za a fara amfani da takardun jefa kuri’a miliyan 93.5 ne a ranar 25 ga watan Fabrairun 2023, lokacin da za a gudanar da zaben shugaban kasa, yayin da sauran takardun jefa kuri’a miliyan 93.5 an tanade su ne domin shirin gudunar da zabe zagaye na biyu idan har babu wanda ya yi nasara a zagayen farko.

LABARAI MASU NASABA

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta

2027: Peter Obi Ya Shiga Rudani Kan Jam’iyyar Da Zai Tsaya Takara

Kakakin ya ce hukumar ta yanke hukuncin buga takardun jefa kuri’un miliyan 187 na shugaban kasa ne, domin zai yi mata wahala ta buga kuri’un cikin karamin lokaci.

Okoye ya ce, “A yanzu muna da jam’iyyun siyasa 18 da za su shiga cikin zaben 2023, sannan doka ta tanadi yadda za a tsayar da ‘yan takara har ma a samu wanda zai zama shugaban Nijeriya. Sakamakon karancin lokaci da doka ta bai wa hukumar INEC idan har ba a samu dan takarar da ya yi nasara a zagayen farko ba, sai hukumar ta dauki matakin buga kuri’un na zageye na biyu a lokacin da muke buga takardun zabe.

“Idan har ‘yan Nijeriya miliyan 93 za su yi zaben shugaban kasa, to za mu kara buga karin kuri’u miliyan 93 saboda zagaye na biyu idan har ba a samu wanda ya yi nasara ba.

“Daga karshe idan har ba a shiga zagaye na biyu ba, to hukumar INEC za ta lalata kuri’u miliyan 93 da ta buga saboda zagaye na biyu. Wannan yana faruwa ne saboda doka ya bai wa hukumar kwanaki 21 kacal wajen shirya zabe na biyu idan har babu wanda ya samu nasara a zagayen farko.”

Da yake bayyana yadda za a samu shugaban kasa da sharuddan da suka kamata na zabe zagaye na biyu, Okeye ya ce, “Sashi na 134 (2) na tsarin mulkin tarayyar Nijeriya wanda shi ne dokar kasa ya tilasta cewa wajibi ne duk wanda zai zama shugaban kasan Nijeriya ya fi sauran ‘yan takara yawan kuri’u. Kuma tilas ya samu akalla kashi 1/4 na kashi 2 bisa bisa 3 na kuri’un da aka kada a jihohi 36 ciki har da Abuja.

“Idan har babu dan takarar da ya samu yawan kuri’un da ake bukata, tsarin mulki ya tanadi cewa dole mu shirya zabe zagaye na biyu a cikin kwanaki 21. Ba dukkan ‘yan takara ba ne za su shiga zabe zagaye na biyu ba. ‘Yan takara 18 ne ke cikin takardun jefa kuri’a na zagaye na farko. Idan ba a samu wanda ya yi nasara a zagayen farko ba, ‘yan takara guda biyu ne kacal za su shiga zagaye na biyu.

“Na farko shi ne wanda ya fi kowa yawan kuri’u, amma ya kasa samun akalla kashi 1/4 daga kashi 2 bisa 3 na yawan kuri’un jihohi ciki har da Abuja. Sai kuma na biyun wanda zai yi zagaye na biyun shi ne, ya zo na biyu wajen samun kashi 1/4 na kashi 3 bisa 4 na kuri’un da aka kada a jihohi da ciki har da Abuja.

“Dole ne mu buga kuri’un babban zabe da na zagaye na biyu a lokaci guda, domin haka hukumar INEC ta saba yi.”

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta
Tambarin Dimokuradiyya

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta

October 17, 2025
peter
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Peter Obi Ya Shiga Rudani Kan Jam’iyyar Da Zai Tsaya Takara

October 17, 2025
peter
Tambarin Dimokuradiyya

Peter Obi Ya Bukaci INEC Ta Tabbatar Da Shaidar Karatun Dan Takara Kafin Shiga Zabe

October 10, 2025
Next Post
2023: Ba Zan Taba Janye Wa Kowa Ba –Kwankwaso

2023: Ba Zan Taba Janye Wa Kowa Ba –Kwankwaso

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Raba Wa Masu Ƙananan Sana’o’i Biliyan 75 Domin Bunƙasa Kasuwancinsu

October 26, 2025
Ɗan Majalisa Ya Ce Ba Zai Sake Takara Ba, Ya Sadaukar Da Ita Ga Matasa

Ɗan Majalisa Ya Ce Ba Zai Sake Takara Ba, Ya Sadaukar Da Ita Ga Matasa

October 26, 2025
Abin Da Ya Sa Aka Yi Watsi Da Tashar Jiragen Ruwa Ta Kan Tudu Da Ke Jihar Kaduna

Abin Da Ya Sa Aka Yi Watsi Da Tashar Jiragen Ruwa Ta Kan Tudu Da Ke Jihar Kaduna

October 26, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

‘Yansanda Sun Kama Wasu Mutum Biyu Da Ake Zargi Da Haɗa Baki Da ‘Yan Bindiga A Kano

October 26, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Gwamnatin Kaduna Tare Da  AUDA–NEPAD Sun Tallafa Wa Manoma 400 Da Kayan Noma

October 26, 2025
Tornadoes Ta Doke Pillars A Wasan Farko Na Babaganaru

Tornadoes Ta Doke Pillars A Wasan Farko Na Babaganaru

October 26, 2025
Gwarzon Kamfanin Samar Da Kayayyakin Gida Na Mai Da Gas Na Shekarar 2025 Kamfanin GEIL

Gwarzon Kamfanin Samar Da Kayayyakin Gida Na Mai Da Gas Na Shekarar 2025 Kamfanin GEIL

October 26, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Gwarzon Ɗan Majalisa Na Shekarar 2025: Benjamin Okezie Kalu

October 26, 2025
An Yi Liyafar Murnar Kebe Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

An Yi Liyafar Murnar Kebe Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

October 25, 2025

Nafisa Abdullahi Aminu: Yarinyar Da Ta Ɗaukaka Darajar Nijeriya A Idon Duniya

October 25, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.