• English
  • Business News
Sunday, July 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: Kotu Ta Hana ‘Yan Takarar Majalisar APC 16 Yin Takara A Ribas 

by Sadiq
3 years ago
in Manyan Labarai
0
2023: Kotu Ta Kori ‘Yan Takarar Majalisar Wakilai 3 Na Jam’iyyar LP A Ribas
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wata babbar kotun tarayya da ke zamanta a garin Fatakwal na jihar Ribas, a ranar Juma’a, ta kori ‘yan takara 16 da ke neman kujerun majalisar dokokin jihar a karkashin jam’iyyar APC, daga tsayawa takara a zaben 2023. 

Jihar Ribas tana da mazabu 32 inda yankin Ribas ta Gabas ke da rinjaye.

  • Xi Jinping Zai Halarci Taron Kolin G20 Da Na APEC Tare Kuma Da Ziyara A Thailand
  • Wakilin Sin Ya Bukaci A Kara Kokarin Taimakawa Kasashen Afirka Yakar Ta’addanci

Jam’iyyar PDP ta maka Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) da wasu mutane 33 a kotu, inda ta nemi a haramta wa ‘yan takarar jam’iyyar APC takara bisa zargin hukumar zaben ba ta sanya ido a zaben jam’iyyarsu ba.

Da yake yanke hukunci a kan kara mai lamba: FHC/PH/CS/152/2022, alkalin kotun, mai shari’a Mohammed Turaki Adamu, ya yanke hukunci a kan wadanda suka shigar da kara.

Wadanda abin ya shafa sun hada da Andoni, Etche I da II, Tai, Gokana, Oyigbo, Eleme, da Fatakwal I, II da III, Khana I da II Okrika, Ahoada West da Obio/Akpor I da mazabar II.

Labarai Masu Nasaba

Ku Manta Da 2027, Tinubu Zai Ci Gaba Da Mulki Har 2031 — Fadar Shugaban Ƙasa Ga ADC

Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP

A halin da ake ciki, shugabancin jam’iyyar APC a jihar ta yi kira ga mambobinta da magoya bayanta da kada su yi kasa a gwiwa da hukuncin da babbar kotun tarayyar ta yanke.

Majalisar zartarwa jam’iyyar APC, a wata sanarwa da ta fitar a Fatakwal a ranar Juma’a ta hannun mai magana da yawun jam’iyyar, Sogbeye Eli, ta tabbatar da cewa jam’iyyar na yin wani yunkuri na daukaka kara kan hukuncin da kotun ta yanke.

Sanarwar ta ci gaba da cewa: “A halin da ake ciki, Majalisar zartarwa tana kira ga mambobin jam’iyyar da miliyoyin al’ummar Ribas da ke goyon bayan ‘yan takararmu a mazabar da abin ya shafa da kada su yanke kauna ko kuma su tayar da hankali yayin da muke shirin daukaka kara don sauya hukuncin kotun dom dawo da ‘yan takararmu kafin zabe.

“Idan za a tuna cewa INEC ita ce ta jagoranci tabbatar da cewa ta sanya ido a kan zaben fidda gwanin APC a gaban wani Alkalin Babbar Kotun Tarayya da ke Fatakwal a wani batu da ke kalubalantar cancantar ‘yan takararmu na Majalisar Tarayya.

“Makiyan dimokuradiyya a jiharmu da suke tsoron haduwa da mu a zabe, sun fito ne don karya lagonmu, do tilasta wa ’yan takararmu amma sun kasa.

“Za mu yi takara a zabukan da ke tafe a dukkan matakai kuma za mu yi nasara bayan ajiye wannan hukunci a gefe kamar yadda kundin tsarin mulki ya bai wa jam’iyyar APC dama.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'Yan TakaraHukunciKotuZabeZaben Fidda Gwani
ShareTweetSendShare
Previous Post

Jami’an Tsaro Sun Kashe Kasurgumin Dan Bindiga, Dogo Maikasuwa A Kaduna 

Next Post

Yanzu-Yanzu: G-5 Sun Gudanar Da Taron Sirri A Enugu 

Related

Ku Manta Da 2027, Tinubu Zai Ci Gaba Da Mulki Har 2031 — Fadar Shugaban Ƙasa Ga ADC
Manyan Labarai

Ku Manta Da 2027, Tinubu Zai Ci Gaba Da Mulki Har 2031 — Fadar Shugaban Ƙasa Ga ADC

11 hours ago
Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP
Manyan Labarai

Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP

18 hours ago
Gwamna Ademola Adeleke Ya Ƙaryata Jita-Jitar Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC
Manyan Labarai

Gwamna Ademola Adeleke Ya Ƙaryata Jita-Jitar Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC

22 hours ago
‘Yansanda Sun Kama Barayi 15, Sun Kwato Motocin Sata 20 A Kano
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama ’Yan Bindiga 17 Tare Da Kashe 3 A Abuja

2 days ago
Kotu Ta Umarci Majalisar Dattijan Nijeriya Da Ta Gaggauta Janye Dakatarwar Da Ta Yi Wa Natasha
Manyan Labarai

Kotu Ta Umarci Majalisar Dattijan Nijeriya Da Ta Gaggauta Janye Dakatarwar Da Ta Yi Wa Natasha

2 days ago
Zanga-zangar ‘Yan Gudun Hijira Na Yelewata ‘Yar Manuniya Ce Ga Daukar Matakan Da Suka Dace
Manyan Labarai

Zanga-zangar ‘Yan Gudun Hijira Na Yelewata ‘Yar Manuniya Ce Ga Daukar Matakan Da Suka Dace

2 days ago
Next Post
Yanzu-Yanzu: G-5 Sun Gudanar Da Taron Sirri A Enugu 

Yanzu-Yanzu: G-5 Sun Gudanar Da Taron Sirri A Enugu 

LABARAI MASU NASABA

Bayern Munich Ta Fara Zawarcin Marcus Rashford

Bayern Munich Ta Fara Zawarcin Marcus Rashford

July 6, 2025
Gobe Za A Fara Wasannin Kofin Afirka Na Mata

Gobe Za A Fara Wasannin Kofin Afirka Na Mata

July 6, 2025
Wang Yi: Amfani Da Karfin Soji Ba Bisa Ka’ida Ba Na Ingiza Karuwar Tashin Hankali

Wang Yi: Amfani Da Karfin Soji Ba Bisa Ka’ida Ba Na Ingiza Karuwar Tashin Hankali

July 5, 2025
Shawarar Ziri Daya Da Hanya Daya Na Cike Da Hangen Nesa Da Burikan Samar Da Ci Gaba In Ji Firaministan Kasar Senegal

Shawarar Ziri Daya Da Hanya Daya Na Cike Da Hangen Nesa Da Burikan Samar Da Ci Gaba In Ji Firaministan Kasar Senegal

July 5, 2025
‘Yan Adawa Sun Dunkule A ADC Don Tunkarar Tinubu A 2027

‘Yan Adawa Sun Dunkule A ADC Don Tunkarar Tinubu A 2027

July 5, 2025
Wakilin Sin Ya Yi Jawabi Game Da Raya Hidimomi Ga Nakasassu Ta Hanyar Fasahar AI A Madadin Wakilan Kasashe Fiye Da 70

Wakilin Sin Ya Yi Jawabi Game Da Raya Hidimomi Ga Nakasassu Ta Hanyar Fasahar AI A Madadin Wakilan Kasashe Fiye Da 70

July 5, 2025
Ku Manta Da 2027, Tinubu Zai Ci Gaba Da Mulki Har 2031 — Fadar Shugaban Ƙasa Ga ADC

Ku Manta Da 2027, Tinubu Zai Ci Gaba Da Mulki Har 2031 — Fadar Shugaban Ƙasa Ga ADC

July 5, 2025
Zan Dade Ban Manta Da Mahaifinmu Ba -Abba Sadau

Zan Dade Ban Manta Da Mahaifinmu Ba -Abba Sadau

July 5, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN Ta Nuna Goyon Baya Ga Fadadar Kungiyar BRICS A Matsayin Hanyar Bunkasa Hadin Gwiwa

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN Ta Nuna Goyon Baya Ga Fadadar Kungiyar BRICS A Matsayin Hanyar Bunkasa Hadin Gwiwa

July 5, 2025
Gidajen Gala Ne Kadai Mafita Ga Masana’antar Kannywood – Falalu Dorayi

Gidajen Gala Ne Kadai Mafita Ga Masana’antar Kannywood – Falalu Dorayi

July 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.