• English
  • Business News
Saturday, September 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: Kotu Ta Hana ‘Yan Takarar Majalisar APC 16 Yin Takara A Ribas 

by Sadiq
3 years ago
in Manyan Labarai
0
2023: Kotu Ta Kori ‘Yan Takarar Majalisar Wakilai 3 Na Jam’iyyar LP A Ribas
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wata babbar kotun tarayya da ke zamanta a garin Fatakwal na jihar Ribas, a ranar Juma’a, ta kori ‘yan takara 16 da ke neman kujerun majalisar dokokin jihar a karkashin jam’iyyar APC, daga tsayawa takara a zaben 2023. 

Jihar Ribas tana da mazabu 32 inda yankin Ribas ta Gabas ke da rinjaye.

  • Xi Jinping Zai Halarci Taron Kolin G20 Da Na APEC Tare Kuma Da Ziyara A Thailand
  • Wakilin Sin Ya Bukaci A Kara Kokarin Taimakawa Kasashen Afirka Yakar Ta’addanci

Jam’iyyar PDP ta maka Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) da wasu mutane 33 a kotu, inda ta nemi a haramta wa ‘yan takarar jam’iyyar APC takara bisa zargin hukumar zaben ba ta sanya ido a zaben jam’iyyarsu ba.

Da yake yanke hukunci a kan kara mai lamba: FHC/PH/CS/152/2022, alkalin kotun, mai shari’a Mohammed Turaki Adamu, ya yanke hukunci a kan wadanda suka shigar da kara.

Wadanda abin ya shafa sun hada da Andoni, Etche I da II, Tai, Gokana, Oyigbo, Eleme, da Fatakwal I, II da III, Khana I da II Okrika, Ahoada West da Obio/Akpor I da mazabar II.

Labarai Masu Nasaba

DAPPMAN Ta Soki Matatar Dangote Kan Rage Farashin Man Fetur

An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

A halin da ake ciki, shugabancin jam’iyyar APC a jihar ta yi kira ga mambobinta da magoya bayanta da kada su yi kasa a gwiwa da hukuncin da babbar kotun tarayyar ta yanke.

Majalisar zartarwa jam’iyyar APC, a wata sanarwa da ta fitar a Fatakwal a ranar Juma’a ta hannun mai magana da yawun jam’iyyar, Sogbeye Eli, ta tabbatar da cewa jam’iyyar na yin wani yunkuri na daukaka kara kan hukuncin da kotun ta yanke.

Sanarwar ta ci gaba da cewa: “A halin da ake ciki, Majalisar zartarwa tana kira ga mambobin jam’iyyar da miliyoyin al’ummar Ribas da ke goyon bayan ‘yan takararmu a mazabar da abin ya shafa da kada su yanke kauna ko kuma su tayar da hankali yayin da muke shirin daukaka kara don sauya hukuncin kotun dom dawo da ‘yan takararmu kafin zabe.

“Idan za a tuna cewa INEC ita ce ta jagoranci tabbatar da cewa ta sanya ido a kan zaben fidda gwanin APC a gaban wani Alkalin Babbar Kotun Tarayya da ke Fatakwal a wani batu da ke kalubalantar cancantar ‘yan takararmu na Majalisar Tarayya.

“Makiyan dimokuradiyya a jiharmu da suke tsoron haduwa da mu a zabe, sun fito ne don karya lagonmu, do tilasta wa ’yan takararmu amma sun kasa.

“Za mu yi takara a zabukan da ke tafe a dukkan matakai kuma za mu yi nasara bayan ajiye wannan hukunci a gefe kamar yadda kundin tsarin mulki ya bai wa jam’iyyar APC dama.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'Yan TakaraHukunciKotuZabeZaben Fidda Gwani
ShareTweetSendShare
Previous Post

Jami’an Tsaro Sun Kashe Kasurgumin Dan Bindiga, Dogo Maikasuwa A Kaduna 

Next Post

Yanzu-Yanzu: G-5 Sun Gudanar Da Taron Sirri A Enugu 

Related

Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12
Manyan Labarai

DAPPMAN Ta Soki Matatar Dangote Kan Rage Farashin Man Fetur

22 minutes ago
An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta
Manyan Labarai

An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

5 hours ago
Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi

9 hours ago
An Shirya Haɗin Gwiwa Da Hukumomi Don Magance Matsalar Ambaliyar Ruwa
Manyan Labarai

An Shirya Haɗin Gwiwa Da Hukumomi Don Magance Matsalar Ambaliyar Ruwa

9 hours ago
Majalisar Tarayya Ta Magantu Kan Gawar Da Aka Samu A Harabarta
Manyan Labarai

Majalisar Tarayya Ta Magantu Kan Gawar Da Aka Samu A Harabarta

10 hours ago
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina
Manyan Labarai

Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

13 hours ago
Next Post
Yanzu-Yanzu: G-5 Sun Gudanar Da Taron Sirri A Enugu 

Yanzu-Yanzu: G-5 Sun Gudanar Da Taron Sirri A Enugu 

LABARAI MASU NASABA

Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12

DAPPMAN Ta Soki Matatar Dangote Kan Rage Farashin Man Fetur

September 13, 2025
Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

September 13, 2025
Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

September 13, 2025
An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

September 13, 2025
An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

September 13, 2025
An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

September 13, 2025
Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

September 13, 2025
Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

September 13, 2025
Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

September 13, 2025
Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

September 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.