ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: Kotu Ta Hana ‘Yan Takarar Majalisar APC 16 Yin Takara A Ribas 

by Sadiq
4 years ago
Kotu

Wata babbar kotun tarayya da ke zamanta a garin Fatakwal na jihar Ribas, a ranar Juma’a, ta kori ‘yan takara 16 da ke neman kujerun majalisar dokokin jihar a karkashin jam’iyyar APC, daga tsayawa takara a zaben 2023. 

Jihar Ribas tana da mazabu 32 inda yankin Ribas ta Gabas ke da rinjaye.

  • Xi Jinping Zai Halarci Taron Kolin G20 Da Na APEC Tare Kuma Da Ziyara A Thailand
  • Wakilin Sin Ya Bukaci A Kara Kokarin Taimakawa Kasashen Afirka Yakar Ta’addanci

Jam’iyyar PDP ta maka Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) da wasu mutane 33 a kotu, inda ta nemi a haramta wa ‘yan takarar jam’iyyar APC takara bisa zargin hukumar zaben ba ta sanya ido a zaben jam’iyyarsu ba.

ADVERTISEMENT

Da yake yanke hukunci a kan kara mai lamba: FHC/PH/CS/152/2022, alkalin kotun, mai shari’a Mohammed Turaki Adamu, ya yanke hukunci a kan wadanda suka shigar da kara.

Wadanda abin ya shafa sun hada da Andoni, Etche I da II, Tai, Gokana, Oyigbo, Eleme, da Fatakwal I, II da III, Khana I da II Okrika, Ahoada West da Obio/Akpor I da mazabar II.

LABARAI MASU NASABA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

A halin da ake ciki, shugabancin jam’iyyar APC a jihar ta yi kira ga mambobinta da magoya bayanta da kada su yi kasa a gwiwa da hukuncin da babbar kotun tarayyar ta yanke.

Majalisar zartarwa jam’iyyar APC, a wata sanarwa da ta fitar a Fatakwal a ranar Juma’a ta hannun mai magana da yawun jam’iyyar, Sogbeye Eli, ta tabbatar da cewa jam’iyyar na yin wani yunkuri na daukaka kara kan hukuncin da kotun ta yanke.

Sanarwar ta ci gaba da cewa: “A halin da ake ciki, Majalisar zartarwa tana kira ga mambobin jam’iyyar da miliyoyin al’ummar Ribas da ke goyon bayan ‘yan takararmu a mazabar da abin ya shafa da kada su yanke kauna ko kuma su tayar da hankali yayin da muke shirin daukaka kara don sauya hukuncin kotun dom dawo da ‘yan takararmu kafin zabe.

“Idan za a tuna cewa INEC ita ce ta jagoranci tabbatar da cewa ta sanya ido a kan zaben fidda gwanin APC a gaban wani Alkalin Babbar Kotun Tarayya da ke Fatakwal a wani batu da ke kalubalantar cancantar ‘yan takararmu na Majalisar Tarayya.

“Makiyan dimokuradiyya a jiharmu da suke tsoron haduwa da mu a zabe, sun fito ne don karya lagonmu, do tilasta wa ’yan takararmu amma sun kasa.

“Za mu yi takara a zabukan da ke tafe a dukkan matakai kuma za mu yi nasara bayan ajiye wannan hukunci a gefe kamar yadda kundin tsarin mulki ya bai wa jam’iyyar APC dama.”

MASU ALAKA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Next Post
Yanzu-Yanzu: G-5 Sun Gudanar Da Taron Sirri A Enugu 

Yanzu-Yanzu: G-5 Sun Gudanar Da Taron Sirri A Enugu 

LABARAI MASU NASABA

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.