• English
  • Business News
Saturday, July 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: PDP Ta Koka Bisa Matsin Lamba Da Ake Wa Mambobinta A Zamfara

by Hussein Yero
3 years ago
in Siyasa
0
2023: PDP Ta Koka Bisa Matsin Lamba Da Ake Wa Mambobinta A Zamfara
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jam’iyyar PDP a Jihar Zamfara, ta koka kan zargin muzgunawar da jami’an tsaro da Gwamnatin Jihar Zamfara ke wa ‘ya’yanta na daure su a gidajen yari bisa yarfen siyasa.

Shugaban riko na jam’iyyar a jihar Hon. Mukhtar Lugga, ne ya bayyana haka a taron manema labarai da aka gudanar a hedikwatar jam’iyyar da ke Gusau.

  • Abubuwan Lura Guda 6 Game Da Sabbin Dokokin CBN Na Mu’amalar Kudi
  • PDP A Kano: Kotu Ta Sanya Ranar Yanke Hukuncin Shari’ar Sadiq Wali Da Abacha

Lugga, ya zargi gwamnatin Jihar Zamfara tare da hadin gwiwar wasu jami’an tsaro da kame mambobinsu bisa zarge-zarge marasa tushe bare makama kawai bisa abin da ya misalta kokarin firgitarwa da razanar da mamboninsu

Ya kuma bayyana cewa dan takarar Sanatan Zamfara ta Tsakiya na jam’iyyar kuma tsohon ministan yada labarai, Alhaji Ikra Aliyu Bilbis, ya shafe tsawon mako guda a tsare a gidan yari tare da gurfanar da shi gaban kotu kan zargin daukar nauyin ‘yan bangar siyasa wajen lalata allunan tallan jam’iyyar APC a babban birnin jihar.

“Kuma tsauraran sharuddan da kotu ta sanya na belinsa sun saba wa tsarin mulki da rashin adalci na sai ya kawo manyan sakatare wanda ke bakin aiki a yanzu ne kafin a bayar da belin .inistan, wanda ya saba wa hankali da doka wanda ba shi da gwamnati ta yaya zai kawo ma’aikacin gwamnati ya yi belinsa? Shugaban ya tambaya.

Labarai Masu Nasaba

Kwankwaso Ya Soki Gwamnatin Tinubu Kan Ware Arewacin Nijeriya A Rabon Arzikin Ƙasa

Kotu Ta Umarci Gwamnatin Bauchi Ta Biya Tsohon Akanta-Janar Naira Miliyan 100

Lugga ya kuma koka da yadda aka kama tare da daure tsohon jakadan Kasar Guinea Conarcri, Mai Riga Muhammad a matsayin wanda bai yi laifin komai ba sai don yana jam’iyyar PDP.

“Tsohon jakadan ya kwashe sama da wata guda a gidan yari kuma shari’arsa tana tafiyar hawauniya, kuma har yanzu ana yi mana barazana daga gwamnatin APC karkashin jagorancin Gwamna Bello Muhammad Matawalle tare da hadin gwiwar wasu jami’an tsaro na kama duk wanda ya fito fili ya ayyana shi dan jam’iyyar PDP ne a Zamfara.”

Shugaban ya yi kira ga Gwamnatin Tarayya da Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) da jami’an tsaro na jihar da kuma babban Sufeton ‘yansanda a kan a taimake su kan halin da jam’iyyar PDP da mutanenta ke ciki na matsi da takurawa.

Ya kuma yi kira ga kasashen duniya da gwamnatin tarayya karkashin jagorancin Shugaban Kasa Muhammadu Buhari da su sa baki a cikin lamarin domin samun zaman lafiya don a halin yanzu dimokradiyya na fuskantar barazana a Jihar Zamfara.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: APCPDPZamfara
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Ta Yi Nasarar Harba Tauraron Dan Adam Na Tattara Bayanan Kasa

Next Post

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 3, Sun Kone Gidaje 22 A Gombe 

Related

Kwankwaso Ya Soki Gwamnatin Tinubu Kan Ware Arewacin Nijeriya A Rabon Arzikin Ƙasa
Da ɗumi-ɗuminsa

Kwankwaso Ya Soki Gwamnatin Tinubu Kan Ware Arewacin Nijeriya A Rabon Arzikin Ƙasa

15 hours ago
Kotu Ta Umarci Gwamnatin Bauchi Ta Biya Tsohon Akanta-Janar Naira Miliyan 100
Manyan Labarai

Kotu Ta Umarci Gwamnatin Bauchi Ta Biya Tsohon Akanta-Janar Naira Miliyan 100

3 days ago
Majalisar Dattawa Za Ta Yi Zama Na Musamman Don Karrama Buhari 
Siyasa

Majalisar Dattawa Za Ta Yi Zama Na Musamman Don Karrama Buhari 

3 days ago
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP
Manyan Labarai

Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP

4 days ago
Tsohon Sakataren Gwamnatin Bauchi, Ibrahim Kashim, Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP
Manyan Labarai

Tsohon Sakataren Gwamnatin Bauchi, Ibrahim Kashim, Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP

4 days ago
Mutumin El-Rufai, Baloni, Ya Fice Daga APC A Kaduna
Siyasa

Mutumin El-Rufai, Baloni, Ya Fice Daga APC A Kaduna

4 days ago
Next Post
‘Yan Bindiga Sun Yi Awon Gaba Da Mutane A Masallaci A Delta

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 3, Sun Kone Gidaje 22 A Gombe 

LABARAI MASU NASABA

Sin Da EU Suna Kokarin Samun Moriyar Juna A Shekaru 50 Masu Zuwa

Sin Da EU Suna Kokarin Samun Moriyar Juna A Shekaru 50 Masu Zuwa

July 25, 2025
Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 

Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 

July 25, 2025
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12

Dangote Ya Ajiye Muƙamin Shugabancin Kamfaninsa Na Siminti

July 25, 2025
Binciken Jin Raayoyi Na CGTN: Duniya Ta Saba Da “Kauracewar” Amurka

Binciken Jin Raayoyi Na CGTN: Duniya Ta Saba Da “Kauracewar” Amurka

July 25, 2025
Jam’iyyar PDP Ta Janye Daga Shiga Zaɓen Ƙananan Hukumomi A Kebbi

2027: Masu Neman Takarar Shugaban Kasa A PDP Sun Kara Matsa Kaimi Bayan Ficewar Atiku

July 25, 2025
Xi Jinping Ya Karbi Takardun Nadi Daga Sabbin Jakadun Kasashen Waje

Xi Jinping Ya Karbi Takardun Nadi Daga Sabbin Jakadun Kasashen Waje

July 25, 2025
Rayuwar Aso Rock: Shugabannin Nijeriya 4 Da Suka Mutu Bayan Kammala Wa’adin Mulki

Rayuwar Aso Rock: Shugabannin Nijeriya 4 Da Suka Mutu Bayan Kammala Wa’adin Mulki

July 25, 2025
Wakilin Sin Ya Karyata Amurka Game Da Batun Yankin Xinjiang Na Sin a Taron Kwamitin Sulhun MDD

Wakilin Sin Ya Karyata Amurka Game Da Batun Yankin Xinjiang Na Sin a Taron Kwamitin Sulhun MDD

July 25, 2025
Gwamnan Jigawa Ya Rattaba Hannu Kan Kudirin Dokar Tabbatar Da Hisbah

Gwamnan Jigawa Ya Rattaba Hannu Kan Kudirin Dokar Tabbatar Da Hisbah

July 25, 2025
Kamfanin Sinotruk Na Kasar Sin Ya Kaddamar Da Sabbin Motocin Dakon Kaya A Kenya

Kamfanin Sinotruk Na Kasar Sin Ya Kaddamar Da Sabbin Motocin Dakon Kaya A Kenya

July 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.