ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: PDP Ta Koka Bisa Matsin Lamba Da Ake Wa Mambobinta A Zamfara

by Hussein Yero
3 years ago
PDP

Jam’iyyar PDP a Jihar Zamfara, ta koka kan zargin muzgunawar da jami’an tsaro da Gwamnatin Jihar Zamfara ke wa ‘ya’yanta na daure su a gidajen yari bisa yarfen siyasa.

Shugaban riko na jam’iyyar a jihar Hon. Mukhtar Lugga, ne ya bayyana haka a taron manema labarai da aka gudanar a hedikwatar jam’iyyar da ke Gusau.

  • Abubuwan Lura Guda 6 Game Da Sabbin Dokokin CBN Na Mu’amalar Kudi
  • PDP A Kano: Kotu Ta Sanya Ranar Yanke Hukuncin Shari’ar Sadiq Wali Da Abacha

Lugga, ya zargi gwamnatin Jihar Zamfara tare da hadin gwiwar wasu jami’an tsaro da kame mambobinsu bisa zarge-zarge marasa tushe bare makama kawai bisa abin da ya misalta kokarin firgitarwa da razanar da mamboninsu

ADVERTISEMENT

Ya kuma bayyana cewa dan takarar Sanatan Zamfara ta Tsakiya na jam’iyyar kuma tsohon ministan yada labarai, Alhaji Ikra Aliyu Bilbis, ya shafe tsawon mako guda a tsare a gidan yari tare da gurfanar da shi gaban kotu kan zargin daukar nauyin ‘yan bangar siyasa wajen lalata allunan tallan jam’iyyar APC a babban birnin jihar.

“Kuma tsauraran sharuddan da kotu ta sanya na belinsa sun saba wa tsarin mulki da rashin adalci na sai ya kawo manyan sakatare wanda ke bakin aiki a yanzu ne kafin a bayar da belin .inistan, wanda ya saba wa hankali da doka wanda ba shi da gwamnati ta yaya zai kawo ma’aikacin gwamnati ya yi belinsa? Shugaban ya tambaya.

LABARAI MASU NASABA

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM

Lugga ya kuma koka da yadda aka kama tare da daure tsohon jakadan Kasar Guinea Conarcri, Mai Riga Muhammad a matsayin wanda bai yi laifin komai ba sai don yana jam’iyyar PDP.

“Tsohon jakadan ya kwashe sama da wata guda a gidan yari kuma shari’arsa tana tafiyar hawauniya, kuma har yanzu ana yi mana barazana daga gwamnatin APC karkashin jagorancin Gwamna Bello Muhammad Matawalle tare da hadin gwiwar wasu jami’an tsaro na kama duk wanda ya fito fili ya ayyana shi dan jam’iyyar PDP ne a Zamfara.”

Shugaban ya yi kira ga Gwamnatin Tarayya da Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) da jami’an tsaro na jihar da kuma babban Sufeton ‘yansanda a kan a taimake su kan halin da jam’iyyar PDP da mutanenta ke ciki na matsi da takurawa.

Ya kuma yi kira ga kasashen duniya da gwamnatin tarayya karkashin jagorancin Shugaban Kasa Muhammadu Buhari da su sa baki a cikin lamarin domin samun zaman lafiya don a halin yanzu dimokradiyya na fuskantar barazana a Jihar Zamfara.

PDP
Hussein Yero
+ postsBio
  • Hussein Yero
    https://hausa.leadership.ng/author/hussein-yero/
    Ɗan Takarar Sanata A Zamfara Ya Koka Kan Yi Wa Rayuwarsa Barazana
  • Hussein Yero
    https://hausa.leadership.ng/author/hussein-yero/
    Abdulaziz Yari Ya Bukaci Limamai Su Ƙara Addu’a Kan Yaƙi Da Ƴan Bindiga A Zamfara
  • Hussein Yero
    https://hausa.leadership.ng/author/hussein-yero/
    Matawalle Ya Buƙaci Magoya Bayansa Su Mara Wa Shugaba Tinubu, Gwamna Lawal Baya
  • Hussein Yero
    https://hausa.leadership.ng/author/hussein-yero/
    Majalisar Zamfara Ta Dakatar Da Shugabannin Kananan Hukumomi Biyu Kan Zargin Almundahanar Kuɗaɗe

MASU ALAKA

Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe
Siyasa

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM
Siyasa

‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM

June 3, 2026
Gwamnatina Za Ta Mayar Da Hankali Kan Buƙatun Al’ummar Nasarawa – Wadada
Siyasa

Gwamnatina Za Ta Mayar Da Hankali Kan Buƙatun Al’ummar Nasarawa – Wadada

June 1, 2026
Next Post
‘Yan Bindiga Sun Yi Awon Gaba Da Mutane A Masallaci A Delta

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 3, Sun Kone Gidaje 22 A Gombe 

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.