• Leadership Hausa
Sunday, August 7, 2022
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result
Home Labarai

2023: PRP Tsagin Balarabe Musa Ta Tsayar Da Sani Salihu Takarar Shugaban Kasa

by Abubakar Abba and Muhammad
2 months ago
in Labarai
0
2023: PRP Tsagin Balarabe Musa Ta Tsayar Da Sani Salihu Takarar Shugaban Kasa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wakilai masu ikon zabe da suka fito daga shiyya shida na kasar nan a Jamiyyar PRP, sun zabi Dokta Sani Salhu Mustapha a matsayin dan takarar shugaban kasa a inuwar jamiyyar PRP a zaben shekarar 2023.

Deliget din Jam’iyyar PRP na bangaren marigayi tsohon shugaban jamiyyar na PRP kasa, Alhaji Balarabe Musa, wadanda ake yi wa lakabi da Gaskiya da Gaskiya ne suka gudanar da zaben a taron da suka yi a dakin taro na Arewa House da ke a jihar Kaduna.

  • 2023: Gwarazan Jam’iyyu A Karon Battar Zaben Shugaban Kasa
  • Burinmu Mata Da Matasa Su Fito A Dama Da Su A Harkokin Mulki Da Siyasa — CITAD

An bayyana Dokta Sani Salhu Mustapha a matsayin Wanda ya samu nasara ba tare da wata hamayya ba.

Shugaban jamiyyar na kasa tsagin Balarabe Musa, Alhaji Abdulmajid Yakubu Dauda ya sanar da cewa, “Taron ya amince da Dakta Sani a matsayin dan takarar Kujerar Shugaban a jamiyyar PRP”.

Yakubu ya kuma bayyana cewa, akwai Shari’a a gaban kotun da INEC da tsagin Falalu Bello kan zargin yunkurin wargaza jamiyyar”.

Labarai Masu Nasaba

Hukumar NIS Ta Cafke Masu Safaran Makamai 3 A Kurus Ribas

Naira Miliyan 5 Nake Nema Don Fansar Mahaifiyata – Mace Mai Safarar Kwayoyi

Abdulmajid ya ci gaba da da cewa, wannan yunkurin na wargaza PRP ba sabon abu bane, inda ya ce, kamar yadda kowa ya sani ne, an kafa PRP ne domin gwagwarmayar siyasa kuma duk wadanda suka yi yunkurin wargaza ta a baya, suma ba su samu nasara ba.

A nasa bangaren Shugaban jam’iyyar PRP na kasa, Dokta Falau Bello, ya ce, Kola Abiola dan Cif Moshood Abiola ne ya yi nasara a zaben fidda gwani na Jam’iyyar da aka gudanar da kuri’u 2097.

Kola ya doke babban abokin hamayyarsa, Alhaji Usman Bugaje wanda ya samu kuri’u 813 da Patience Ndidi da Gboluga Mosugu da suka kuri’u 329 da 263 bi da bi.

Falalu ya ce, an tattara sakamakon zaben ne daga jihohin da wakilan Jam’iyyar masu ikon zabe suka kada aka kuma mika su zuwa Abuja, inda sakamakon karshe da aka tattara a Sakatariyar jam’iyyar da ke Abuja ya nuna wakilai 3522 ne aka tantance inda suka kada kuri’u 3416 an kuma samu guda 141 da suka lalace.

Tun da farko a nasa jawabin, Bello ya ce jam’iyyar ta yi zabukan fitar da gwaninta daban-daban a Jihohi domin tana son a kusantar da zaben ga al’uma.

Kola dai da ne ga marigayi Cif Moshood Abiola, mai taimakon jama’a kuma wanda ake kyautata zaton shi ne ya lashe zaben shugaban kasa a shekarar 1993 da gwamnatin mulkin soja ta Shugaba Ibrahim Babangida ta soke. Babban Abiola ya tsaya takara a jam’iyyar Social Democratic Party (SDP).

Tags: 2023Jam'iyyar PRP
ShareTweetSendShare
Previous Post

Marawa Kamfanoni Masu Zaman Kansu Baya Zai Amfani Kasar Sin Da Ma Duniya Baki Daya

Next Post

Mutane 11 Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Harin Jirgin Kasan Kaduna Sun Shaki Iskar ‘Yanci

Related

Hukumar NIS Ta Cafke Masu Safaran Makamai 3 A Kurus Ribas
Labarai

Hukumar NIS Ta Cafke Masu Safaran Makamai 3 A Kurus Ribas

2 hours ago
Naira Miliyan 5 Nake Nema Don Fansar Mahaifiyata – Mace Mai Safarar Kwayoyi
Labarai

Naira Miliyan 5 Nake Nema Don Fansar Mahaifiyata – Mace Mai Safarar Kwayoyi

3 hours ago
NDLEA Ta Cafke Tsohon Sojan Da Ke Wa ‘Yan Bindiga Safarar Miyagun Kwayoyi
Labarai

NDLEA Ta Cafke Tsohon Sojan Da Ke Wa ‘Yan Bindiga Safarar Miyagun Kwayoyi

4 hours ago
Matsalar Tsaro: An Gudanar Da Addi’oi Na Musamman A Yankin Funtuwa
Labarai

Matsalar Tsaro: An Gudanar Da Addi’oi Na Musamman A Yankin Funtuwa

5 hours ago
NBC Ta Ci Tarar Trust TV Tarar Miliyan 5 Kan Yada Ayyukan ‘Yan Bindiga 
Labarai

CDD Ta Soki NBC Kan Cin Tarar Trust TV Da Wasu Miliyan 20

7 hours ago
Kashi 70% Na Jariran Nijeriya Ba Su Samun Nonon Shayarwa –UNICEF, WHO
Labarai

Kashi 70% Na Jariran Nijeriya Ba Su Samun Nonon Shayarwa –UNICEF, WHO

7 hours ago
Next Post
Sabon Rikici Ya Kunno Kai A Shugabancin Jam’iyyar APC Ta Kasa

Mutane 11 Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Harin Jirgin Kasan Kaduna Sun Shaki Iskar ‘Yanci

LABARAI MASU NASABA

Peter Obi Ba Zaiyi Nasarar Lashe Koda Rabin Jihar Nasarawa Ba – Inji Deji Adeyanju

Peter Obi Ba Zaiyi Nasarar Lashe Koda Rabin Jihar Nasarawa Ba – Inji Deji Adeyanju

August 7, 2022
Hukumar NIS Ta Cafke Masu Safaran Makamai 3 A Kurus Ribas

Hukumar NIS Ta Cafke Masu Safaran Makamai 3 A Kurus Ribas

August 7, 2022
MDD Da Gwamnatocin Kasashe Daban-Daban Sun Sake Jaddada Tsayawa Ga Manufar Kasancewar Kasar Sin Daya Tak A Duniya

MDD Da Gwamnatocin Kasashe Daban-Daban Sun Sake Jaddada Tsayawa Ga Manufar Kasancewar Kasar Sin Daya Tak A Duniya

August 7, 2022
Naira Miliyan 5 Nake Nema Don Fansar Mahaifiyata – Mace Mai Safarar Kwayoyi

Naira Miliyan 5 Nake Nema Don Fansar Mahaifiyata – Mace Mai Safarar Kwayoyi

August 7, 2022
Wakilin Sin Ya Ki Amincewa Da Zargin Da Amurka Ta Yi Kan Manufofin Makamashin Nukiliyar Kasar Sin

Wakilin Sin Ya Ki Amincewa Da Zargin Da Amurka Ta Yi Kan Manufofin Makamashin Nukiliyar Kasar Sin

August 7, 2022
NDLEA Ta Cafke Tsohon Sojan Da Ke Wa ‘Yan Bindiga Safarar Miyagun Kwayoyi

NDLEA Ta Cafke Tsohon Sojan Da Ke Wa ‘Yan Bindiga Safarar Miyagun Kwayoyi

August 7, 2022
Sharhi: Yadda Kasar Amurka Ta Nuna Fuska Biyu A Kan Batun Taiwan

Sharhi: Yadda Kasar Amurka Ta Nuna Fuska Biyu A Kan Batun Taiwan

August 7, 2022
Matsalar Tsaro: An Gudanar Da Addi’oi Na Musamman A Yankin Funtuwa

Matsalar Tsaro: An Gudanar Da Addi’oi Na Musamman A Yankin Funtuwa

August 7, 2022
Cinikayyar Waje Ta Hajojin Sin Ta Bunkasa Da Kaso 10.4 Bisa Dari Cikin Watanni 7 Na Bana

Cinikayyar Waje Ta Hajojin Sin Ta Bunkasa Da Kaso 10.4 Bisa Dari Cikin Watanni 7 Na Bana

August 7, 2022
An Nemi Jam’iyyar APC Ta kara kaimi Wajen Biyan Bukatun ‘Yan Nijeriya

An Nemi Jam’iyyar APC Ta kara kaimi Wajen Biyan Bukatun ‘Yan Nijeriya

August 7, 2022
ADVERTISEMENT
Advertise with us

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.