ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, July 27, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: PRP Tsagin Balarabe Musa Ta Tsayar Da Sani Salihu Takarar Shugaban Kasa

by Abubakar Abba and Muhammad
4 years ago
2023

Wakilai masu ikon zabe da suka fito daga shiyya shida na kasar nan a Jamiyyar PRP, sun zabi Dokta Sani Salhu Mustapha a matsayin dan takarar shugaban kasa a inuwar jamiyyar PRP a zaben shekarar 2023.

Deliget din Jam’iyyar PRP na bangaren marigayi tsohon shugaban jamiyyar na PRP kasa, Alhaji Balarabe Musa, wadanda ake yi wa lakabi da Gaskiya da Gaskiya ne suka gudanar da zaben a taron da suka yi a dakin taro na Arewa House da ke a jihar Kaduna.

  • 2023: Gwarazan Jam’iyyu A Karon Battar Zaben Shugaban Kasa
  • Burinmu Mata Da Matasa Su Fito A Dama Da Su A Harkokin Mulki Da Siyasa — CITAD

An bayyana Dokta Sani Salhu Mustapha a matsayin Wanda ya samu nasara ba tare da wata hamayya ba.

ADVERTISEMENT

Shugaban jamiyyar na kasa tsagin Balarabe Musa, Alhaji Abdulmajid Yakubu Dauda ya sanar da cewa, “Taron ya amince da Dakta Sani a matsayin dan takarar Kujerar Shugaban a jamiyyar PRP”.

Yakubu ya kuma bayyana cewa, akwai Shari’a a gaban kotun da INEC da tsagin Falalu Bello kan zargin yunkurin wargaza jamiyyar”.

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Dangantakar Sin Da Afrika Na Taba Mutane Masu Rauni Da Karamin Karfi

NSCDC Ta Cafke Mutane 2 Da Ake Zargi Da Sace Kayan Titin Jirgin Kasa A Kano

Abdulmajid ya ci gaba da da cewa, wannan yunkurin na wargaza PRP ba sabon abu bane, inda ya ce, kamar yadda kowa ya sani ne, an kafa PRP ne domin gwagwarmayar siyasa kuma duk wadanda suka yi yunkurin wargaza ta a baya, suma ba su samu nasara ba.

A nasa bangaren Shugaban jam’iyyar PRP na kasa, Dokta Falau Bello, ya ce, Kola Abiola dan Cif Moshood Abiola ne ya yi nasara a zaben fidda gwani na Jam’iyyar da aka gudanar da kuri’u 2097.

Kola ya doke babban abokin hamayyarsa, Alhaji Usman Bugaje wanda ya samu kuri’u 813 da Patience Ndidi da Gboluga Mosugu da suka kuri’u 329 da 263 bi da bi.

Falalu ya ce, an tattara sakamakon zaben ne daga jihohin da wakilan Jam’iyyar masu ikon zabe suka kada aka kuma mika su zuwa Abuja, inda sakamakon karshe da aka tattara a Sakatariyar jam’iyyar da ke Abuja ya nuna wakilai 3522 ne aka tantance inda suka kada kuri’u 3416 an kuma samu guda 141 da suka lalace.

Tun da farko a nasa jawabin, Bello ya ce jam’iyyar ta yi zabukan fitar da gwaninta daban-daban a Jihohi domin tana son a kusantar da zaben ga al’uma.

Kola dai da ne ga marigayi Cif Moshood Abiola, mai taimakon jama’a kuma wanda ake kyautata zaton shi ne ya lashe zaben shugaban kasa a shekarar 1993 da gwamnatin mulkin soja ta Shugaba Ibrahim Babangida ta soke. Babban Abiola ya tsaya takara a jam’iyyar Social Democratic Party (SDP).

2023
Abubakar Abba
+ posts Bio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Sabon Rahoton Bankin Duniya Ya Yaba Da Yadda Tattalin Arzkin Nijeriya Ke Bunkasa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nijeriya Ta Tabka Asarar Naira Biliyan 2.61 A Samar Da Wuta A Zangon Farko Na 2026 —NERC
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    NPA Ta Goyi Bayan Yarjejeniyar Shirin Bayar Da Horo Na Musamman Domin Tafiyar Da Tashoshin Jiragen Ruwa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya
2023
Muhammad
+ posts Bio
  • Muhammad
    Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100
  • Muhammad
    ‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan
  • Muhammad
    Cikin Shekaru 28, Kudiri Ƙasa Da 10 Sanatocin Zamfara Ta Arewa Suka Gabatar A Majalisa – Shinkafi
  • Muhammad
    2027: NNPP Ta Yi Wa Korarrun Mambobinta Afuwa, Ta Yi Alƙawarin Basu Tikitin Kai-tsaye

MASU ALAKA

Sakamakon Dangantakar Sin Da Afrika Na Taba Mutane Masu Rauni Da Karamin Karfi
Ra'ayi Riga

Sakamakon Dangantakar Sin Da Afrika Na Taba Mutane Masu Rauni Da Karamin Karfi

July 27, 2026
2023
Manyan Labarai

NSCDC Ta Cafke Mutane 2 Da Ake Zargi Da Sace Kayan Titin Jirgin Kasa A Kano

July 27, 2026
2023
Labarai

Obi-Kwankwaso Obasanjo Yake Goyon Baya, Amma Atiku Zai Iya Lashe Zabe – Momodu

July 27, 2026
Next Post
Sabon Rikici Ya Kunno Kai A Shugabancin Jam’iyyar APC Ta Kasa

Mutane 11 Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Harin Jirgin Kasan Kaduna Sun Shaki Iskar ‘Yanci

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Dangantakar Sin Da Afrika Na Taba Mutane Masu Rauni Da Karamin Karfi

Sakamakon Dangantakar Sin Da Afrika Na Taba Mutane Masu Rauni Da Karamin Karfi

July 27, 2026
2023

WAFU B 2026: Nijeriya Ta Doke Ghana Da Ci 4-2 A Wasan Farko

July 27, 2026
An Samu Karin Sabbin Abubuwa Da Sin Ke Fitar Wa Waje Da Ake Wa Lakabi Da “New New Three”

An Samu Karin Sabbin Abubuwa Da Sin Ke Fitar Wa Waje Da Ake Wa Lakabi Da “New New Three”

July 27, 2026
2023

NSCDC Ta Cafke Mutane 2 Da Ake Zargi Da Sace Kayan Titin Jirgin Kasa A Kano

July 27, 2026
Saura Kwanaki 100 A Bude CIIE Karo Na 9

Saura Kwanaki 100 A Bude CIIE Karo Na 9

July 27, 2026
2023

Obi-Kwankwaso Obasanjo Yake Goyon Baya, Amma Atiku Zai Iya Lashe Zabe – Momodu

July 27, 2026
Ribar Manyan Kamfanonin Sarrafa Kayayyaki Na Sin Ta Karu Da Kaso 18.7 A Rabin Farkon Bana

Ribar Manyan Kamfanonin Sarrafa Kayayyaki Na Sin Ta Karu Da Kaso 18.7 A Rabin Farkon Bana

July 27, 2026
Xi: Sin Ta Shirya Kara Karfafa Dangantaka Da Brazil

Xi: Sin Ta Shirya Kara Karfafa Dangantaka Da Brazil

July 27, 2026
Tinubu Ya Goyi Bayan Kafa Sabon Asibitin Koyarwa A Bichi — Ɗan Majalisar Kano

Tinubu Ya Goyi Bayan Kafa Sabon Asibitin Koyarwa A Bichi — Ɗan Majalisar Kano

July 27, 2026
‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 30, Sun Ƙone Gidaje Da Shaguna A Kaduna 

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 30, Sun Ƙone Gidaje Da Shaguna A Kaduna 

July 27, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.