ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: PRP Tsagin Balarabe Musa Ta Tsayar Da Sani Salihu Takarar Shugaban Kasa

by Abubakar Abba and Muhammad
4 years ago
2023

Wakilai masu ikon zabe da suka fito daga shiyya shida na kasar nan a Jamiyyar PRP, sun zabi Dokta Sani Salhu Mustapha a matsayin dan takarar shugaban kasa a inuwar jamiyyar PRP a zaben shekarar 2023.

Deliget din Jam’iyyar PRP na bangaren marigayi tsohon shugaban jamiyyar na PRP kasa, Alhaji Balarabe Musa, wadanda ake yi wa lakabi da Gaskiya da Gaskiya ne suka gudanar da zaben a taron da suka yi a dakin taro na Arewa House da ke a jihar Kaduna.

  • 2023: Gwarazan Jam’iyyu A Karon Battar Zaben Shugaban Kasa
  • Burinmu Mata Da Matasa Su Fito A Dama Da Su A Harkokin Mulki Da Siyasa — CITAD

An bayyana Dokta Sani Salhu Mustapha a matsayin Wanda ya samu nasara ba tare da wata hamayya ba.

ADVERTISEMENT

Shugaban jamiyyar na kasa tsagin Balarabe Musa, Alhaji Abdulmajid Yakubu Dauda ya sanar da cewa, “Taron ya amince da Dakta Sani a matsayin dan takarar Kujerar Shugaban a jamiyyar PRP”.

Yakubu ya kuma bayyana cewa, akwai Shari’a a gaban kotun da INEC da tsagin Falalu Bello kan zargin yunkurin wargaza jamiyyar”.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

Abdulmajid ya ci gaba da da cewa, wannan yunkurin na wargaza PRP ba sabon abu bane, inda ya ce, kamar yadda kowa ya sani ne, an kafa PRP ne domin gwagwarmayar siyasa kuma duk wadanda suka yi yunkurin wargaza ta a baya, suma ba su samu nasara ba.

A nasa bangaren Shugaban jam’iyyar PRP na kasa, Dokta Falau Bello, ya ce, Kola Abiola dan Cif Moshood Abiola ne ya yi nasara a zaben fidda gwani na Jam’iyyar da aka gudanar da kuri’u 2097.

Kola ya doke babban abokin hamayyarsa, Alhaji Usman Bugaje wanda ya samu kuri’u 813 da Patience Ndidi da Gboluga Mosugu da suka kuri’u 329 da 263 bi da bi.

Falalu ya ce, an tattara sakamakon zaben ne daga jihohin da wakilan Jam’iyyar masu ikon zabe suka kada aka kuma mika su zuwa Abuja, inda sakamakon karshe da aka tattara a Sakatariyar jam’iyyar da ke Abuja ya nuna wakilai 3522 ne aka tantance inda suka kada kuri’u 3416 an kuma samu guda 141 da suka lalace.

Tun da farko a nasa jawabin, Bello ya ce jam’iyyar ta yi zabukan fitar da gwaninta daban-daban a Jihohi domin tana son a kusantar da zaben ga al’uma.

Kola dai da ne ga marigayi Cif Moshood Abiola, mai taimakon jama’a kuma wanda ake kyautata zaton shi ne ya lashe zaben shugaban kasa a shekarar 1993 da gwamnatin mulkin soja ta Shugaba Ibrahim Babangida ta soke. Babban Abiola ya tsaya takara a jam’iyyar Social Democratic Party (SDP).

2023
Abubakar Abba
+ posts Bio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Tun Ina Karama Marigayi Tumbuleke Ke Sa Ni Dariya —Hannatu Musawa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    NPA Ta Bayyana Cewa Kirkiro Da Sabuwar Hukumar NPERA Ba Zai Zame Mata Tarnaki Ba
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Yadda Bikin Girke-girke Ya Karfafa Alaka Tsakanin Musulmai Da Kiristoci A Kaduna
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari Kan Wasu Dalilan Da Ke Haddasa Sabanin Abotakar Jarumi Ko Jaruma A Kannywood
2023
Muhammad
+ posts Bio
  • Muhammad
    Yadda Na Tsira Daga Cutar Mashaƙo A Katsina: “Na Fara Da Tsartuwar Jini Tare Da Yawu”
  • Muhammad
    An Naɗa Yusuf Nasidi Nasir A Matsayin Talban Barayan Kano
  • Muhammad
    Wani Kamfani Ya Tallafa Wa Masu Sana’ar Shayi A Kano
  • Muhammad
    Kosan Waka Ya Rasu, Gwamnan Kano Ya Jajanta Wa Iyalansa

MASU ALAKA

'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina
Labarai

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare
Labarai

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Next Post
Sabon Rikici Ya Kunno Kai A Shugabancin Jam’iyyar APC Ta Kasa

Mutane 11 Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Harin Jirgin Kasan Kaduna Sun Shaki Iskar ‘Yanci

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.