ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 7, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: PRP Tsagin Balarabe Musa Ta Tsayar Da Sani Salihu Takarar Shugaban Kasa

by Abubakar Abba and Muhammad
4 years ago
2023

Wakilai masu ikon zabe da suka fito daga shiyya shida na kasar nan a Jamiyyar PRP, sun zabi Dokta Sani Salhu Mustapha a matsayin dan takarar shugaban kasa a inuwar jamiyyar PRP a zaben shekarar 2023.

Deliget din Jam’iyyar PRP na bangaren marigayi tsohon shugaban jamiyyar na PRP kasa, Alhaji Balarabe Musa, wadanda ake yi wa lakabi da Gaskiya da Gaskiya ne suka gudanar da zaben a taron da suka yi a dakin taro na Arewa House da ke a jihar Kaduna.

  • 2023: Gwarazan Jam’iyyu A Karon Battar Zaben Shugaban Kasa
  • Burinmu Mata Da Matasa Su Fito A Dama Da Su A Harkokin Mulki Da Siyasa — CITAD

An bayyana Dokta Sani Salhu Mustapha a matsayin Wanda ya samu nasara ba tare da wata hamayya ba.

ADVERTISEMENT

Shugaban jamiyyar na kasa tsagin Balarabe Musa, Alhaji Abdulmajid Yakubu Dauda ya sanar da cewa, “Taron ya amince da Dakta Sani a matsayin dan takarar Kujerar Shugaban a jamiyyar PRP”.

Yakubu ya kuma bayyana cewa, akwai Shari’a a gaban kotun da INEC da tsagin Falalu Bello kan zargin yunkurin wargaza jamiyyar”.

LABARAI MASU NASABA

MURIC Ba Ta Gamsu Da Rahoton Lafiyar El-Rufai Da Aka Gabatar A Kotu Ba

Gwamnatin Neja Ta Sanya Dokar Hana Fita Bayan Mutane 80 Sun Rasu Sakamakon Rikicin Ƙabilanci

Abdulmajid ya ci gaba da da cewa, wannan yunkurin na wargaza PRP ba sabon abu bane, inda ya ce, kamar yadda kowa ya sani ne, an kafa PRP ne domin gwagwarmayar siyasa kuma duk wadanda suka yi yunkurin wargaza ta a baya, suma ba su samu nasara ba.

A nasa bangaren Shugaban jam’iyyar PRP na kasa, Dokta Falau Bello, ya ce, Kola Abiola dan Cif Moshood Abiola ne ya yi nasara a zaben fidda gwani na Jam’iyyar da aka gudanar da kuri’u 2097.

Kola ya doke babban abokin hamayyarsa, Alhaji Usman Bugaje wanda ya samu kuri’u 813 da Patience Ndidi da Gboluga Mosugu da suka kuri’u 329 da 263 bi da bi.

Falalu ya ce, an tattara sakamakon zaben ne daga jihohin da wakilan Jam’iyyar masu ikon zabe suka kada aka kuma mika su zuwa Abuja, inda sakamakon karshe da aka tattara a Sakatariyar jam’iyyar da ke Abuja ya nuna wakilai 3522 ne aka tantance inda suka kada kuri’u 3416 an kuma samu guda 141 da suka lalace.

Tun da farko a nasa jawabin, Bello ya ce jam’iyyar ta yi zabukan fitar da gwaninta daban-daban a Jihohi domin tana son a kusantar da zaben ga al’uma.

Kola dai da ne ga marigayi Cif Moshood Abiola, mai taimakon jama’a kuma wanda ake kyautata zaton shi ne ya lashe zaben shugaban kasa a shekarar 1993 da gwamnatin mulkin soja ta Shugaba Ibrahim Babangida ta soke. Babban Abiola ya tsaya takara a jam’iyyar Social Democratic Party (SDP).

2023
Abubakar Abba
+ posts Bio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    NPA Ta Ɗaura Ɗamarar Magance Matsalolin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Abin Da Ya Sa Matatar Ɗangote Ta Ƙaryata Iƙirarin Dillalan Man Fetur 
2023
Muhammad
+ posts Bio
  • Muhammad
    Cikin Shekaru 28, Kudiri Ƙasa Da 10 Sanatocin Zamfara Ta Arewa Suka Gabatar A Majalisa – Shinkafi
  • Muhammad
    2027: NNPP Ta Yi Wa Korarrun Mambobinta Afuwa, Ta Yi Alƙawarin Basu Tikitin Kai-tsaye
  • Muhammad
    Musulunci Na Fuskantar Barazana A Karƙashin Mulkin Tinubu — Datti Baba-Ahmed
  • Muhammad
    Kwankwaso Tamkar Tsuntsu Ne A Siyasa Da Yake Sauya Sheƙa Daga Nan Zuwa Can – Ganduje

MASU ALAKA

Kotu Ta Umarci A Kamo Mata Dogarin Gwamna El-Rufa’i
Labarai

MURIC Ba Ta Gamsu Da Rahoton Lafiyar El-Rufai Da Aka Gabatar A Kotu Ba

July 7, 2026
Gwamnatin Neja Ta Sanya Dokar Hana Fita Bayan Mutane 80 Sun Rasu Sakamakon Rikicin Ƙabilanci
Manyan Labarai

Gwamnatin Neja Ta Sanya Dokar Hana Fita Bayan Mutane 80 Sun Rasu Sakamakon Rikicin Ƙabilanci

July 7, 2026
Iran Ta Harba Wa Jiragen Ruwa Makamai Masu Linzami A Mashigar Hormuz
Manyan Labarai

Iran Ta Harba Wa Jiragen Ruwa Makamai Masu Linzami A Mashigar Hormuz

July 7, 2026
Next Post
Sabon Rikici Ya Kunno Kai A Shugabancin Jam’iyyar APC Ta Kasa

Mutane 11 Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Harin Jirgin Kasan Kaduna Sun Shaki Iskar ‘Yanci

LABARAI MASU NASABA

Kotu Ta Umarci A Kamo Mata Dogarin Gwamna El-Rufa’i

MURIC Ba Ta Gamsu Da Rahoton Lafiyar El-Rufai Da Aka Gabatar A Kotu Ba

July 7, 2026
Gwamnatin Neja Ta Sanya Dokar Hana Fita Bayan Mutane 80 Sun Rasu Sakamakon Rikicin Ƙabilanci

Gwamnatin Neja Ta Sanya Dokar Hana Fita Bayan Mutane 80 Sun Rasu Sakamakon Rikicin Ƙabilanci

July 7, 2026
Iran Ta Harba Wa Jiragen Ruwa Makamai Masu Linzami A Mashigar Hormuz

Iran Ta Harba Wa Jiragen Ruwa Makamai Masu Linzami A Mashigar Hormuz

July 7, 2026
Hukuma Ta Tilasta Wa Alƙali Yin Ritaya Saboda Karɓar Cin Hanci A Kano

Hukuma Ta Tilasta Wa Alƙali Yin Ritaya Saboda Karɓar Cin Hanci A Kano

July 7, 2026
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya

ADC Ta Zargi Gwamnatin Tinubu Da Jefa ‘Yan Nijeriya Miliyan 17 Cikin Yunwa

July 7, 2026
Kasuwa Ce Ke Saita Tsarin Cinikayyar Sin Da EU In Ji Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin

Kasuwa Ce Ke Saita Tsarin Cinikayyar Sin Da EU In Ji Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin

July 6, 2026
Dukkan Kabilun Kasar Sin Na Zaman Tsintsiya Madaurinki Daya

Dukkan Kabilun Kasar Sin Na Zaman Tsintsiya Madaurinki Daya

July 6, 2026
Mutane 15 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Jihar Kwara

Mutane 15 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Jihar Kwara

July 6, 2026
Gwamnatin Sin Ta Fara Aika Zagayen Farko Na Kayakin Agajin Gaggawa Ga Venezuela

Gwamnatin Sin Ta Fara Aika Zagayen Farko Na Kayakin Agajin Gaggawa Ga Venezuela

July 6, 2026
FIFA Ta Tsallake Iyakarta Dangane Da Batun Dakatarwar Balogun – UEFA

FIFA Ta Tsallake Iyakarta Dangane Da Batun Dakatarwar Balogun – UEFA

July 6, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.