ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Burinmu Mata Da Matasa Su Fito A Dama Da Su A Harkokin Mulki Da Siyasa — CITAD

by Muhammad
4 years ago
Burinmu

Cibiyar da ke shirya bita da wayar da kan al’uma kan fasahar sadarwa ta zamani (CITAD) tare da hadin guiwar cibiyar (Hope Action Progress), sun shirya wani taron bita da wayar da kan mata da matasa a Kano kan sha’anin mulki da siyasa da yadda ake gudanar da mulki da hulda da Jama’a.

Cibiyar ta gudanar da taron ranar Litinin a Otel din Tahir da ke Kano, ta kuma bayyana cewa ce a baya ta gudanar da irin wadannan bitoci ga mata da matasa don su fahimci muhimmancin shiga cikin harkokin mulki da sha’anin siyasa a dama da su wurin neman madafun iko.

  • Burinmu Mata Da Matasa Su Fito A Dama Da Su A Harkokin Mulki Da Siyasa — CITAD
  • Ana Rade-Radin APC Ta Tsayar Da Ahmad Lawan A Matsayin Dan Takarar Masalaha

Babbar daraktar shirye-shirye a cibiyar (AAN) kuma guda cikin masu gabatar da kasidu a taron, Suwaiba Muhammad Dankabo, ta bayyana cewa, idan zaka shiga cikin harkokin siyasa kana mai goyan baya ko kuma tsaya wa ka yi a zabe ka, kana da bukatar sanin wasu muhimman al’amura.

ADVERTISEMENT

Dankabo, ta ce wannan dalilin ne ma yasa suka shirya bita don ilimantar da mata da matasa idan sun samu mulki su san yadda za su tafiyar da shi da yadda za su yi mu’amala da Jama’a.

Da aka tambaye ta shin yanzu kwalliya na biyan kudin sabulu a irin wadannan taruka da suke shirya wa, sai ta kayara da baki ta ce,” Tabbas kwalliya ta fara biyan kudin sabulu don kuwa mun zauna da shugabannin Jam’iyyu a baya kan su ba mata da matasa damar shiga a dama da su a sha’anin mulki da siyasa, suma su tsaya takara a zabe su,”

LABARAI MASU NASABA

MURIC Ta Zargi Gwamnatin Tarayyar Nijeriya Da Fifita Kiristoci Fiye Da Musulmi

Majalisar Dattawa Ta Damu Kan Tsarin Yaki Da COVID-19 Bayan Sake Bullar Cutar A Nijeriya

“Yanzu haka wasu Jam’iyyun sun amsa wannan kiran namu don ko Jam’iyyar PRP a kasa ta ba kaso mai tsoka a matakai daban-daban a takara, haka takwararta Jam’iyyar YPP ta ba mata da matasa akalla 70 tikitin takara, ita ma Jam’iyyar PDP ta ba mata biyu damar tsayawa takara,” in ji Suwaiba.

“Babban Kudurinmu shi ne, a bawa mata da matasa damar su fito su tsaya takara kuma a zabe su a madafun iko daban-daban a Nijeriya ta yadda za su samar da aiyukan yi da tsakulo matsalolin al’uma da magance su, saboda mutumin da yake da damar mulki ya fi kowa kwazon kawo sauyi a cikin al’uma.” A Cewar Dankabo.

A nasa jawabin shugaban Jam’iyyar PRP na Jihar Kano, Abba Sule Namatazu, ya ce Jam’iyyarsu ta PRO tuni ta amsa wannan kiran don kuwa sun ba matasa kaso 75 cikin 100 damar tsayawa takara a kujeru daban-dabn kuma dan takararsu na Kano ma matashi ne mai karancin shekaru, kuma sun ba mata biyu kujerar wakilci a tarayya

Burinmu
Muhammad
+ postsBio
  • Muhammad
    Cikin Shekaru 28, Kudiri Ƙasa Da 10 Sanatocin Zamfara Ta Arewa Suka Gabatar A Majalisa – Shinkafi
  • Muhammad
    2027: NNPP Ta Yi Wa Korarrun Mambobinta Afuwa, Ta Yi Alƙawarin Basu Tikitin Kai-tsaye
  • Muhammad
    Musulunci Na Fuskantar Barazana A Karƙashin Mulkin Tinubu — Datti Baba-Ahmed
  • Muhammad
    Kwankwaso Tamkar Tsuntsu Ne A Siyasa Da Yake Sauya Sheƙa Daga Nan Zuwa Can – Ganduje

MASU ALAKA

MURIC Ta Zargi Gwamnatin Tarayyar Nijeriya Da Fifita Kiristoci Fiye Da Musulmi
Addini

MURIC Ta Zargi Gwamnatin Tarayyar Nijeriya Da Fifita Kiristoci Fiye Da Musulmi

May 2, 2026
Majalisar Dattawa Ta Damu Kan Tsarin Yaki Da COVID-19 Bayan Sake Bullar Cutar A Nijeriya
Kananan Labarai

Majalisar Dattawa Ta Damu Kan Tsarin Yaki Da COVID-19 Bayan Sake Bullar Cutar A Nijeriya

April 28, 2026
Wakili Ya Rasu Kwana 3 Da Karewar Wa’adinsa A Matsayin Dan Majalisar Dokokin Jihar Bauchi
Kananan Labarai

2027: Majalisar Dattawa Za Ta Ɗage Zaman Ta A Ranar Alhamis Saboda Zaɓen Fidda Gwani

April 28, 2026
Next Post
Sin Na Shan Yabo Kan Gudunmawarta Ga Kare Muhallin Duniya

Sin Na Shan Yabo Kan Gudunmawarta Ga Kare Muhallin Duniya

LABARAI MASU NASABA

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

June 25, 2026
EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.