• English
  • Business News
Thursday, October 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: Tashoshin Jiragen Ruwa Da Na Kasa Da Matatun Mai Duk ‘Yan Kasuwa Zan Ba —Atiku

by Sulaiman
3 years ago
Atiku

A ci gaba da bayyana manufofin gwamnatin da zai kafa idan ya yi nasara, ɗan takarar shugaban ƙasa a PDP, Atiku Abubakar, ya yi alƙawarin damƙa manyan ayyukan raya ƙasa a hannun kamfanoni masu zaman kan su, ta yadda zai sauƙaƙe wa Gwamnatin Tarayya nauyi da wahalhalun kashe maƙudan kuɗaɗe wajen gudanar da ayyukan raya ƙasa.

 

Atiku ya bayyana haka a taron ganawar da ya yi da Kungiyar Editocin Najeriya a Legas.

  • Hadari Gabas…Yadda Tattaunawar Tinubu Da Atiku Lokacin Da Suka Hadu A Abuja Ya Gudana

“Idan ku ka kalli irin gagarimin ayyukan da ke gaban gwamnati a ƙasar nan, kamar gina tashoshi jiragen ruwa, gina hanyoyin jiragen ƙasa, to ana buƙatar maƙudan kuɗaɗe ne. Kuma kun dai san a yanzu gwamnati ba ta da waɗannan kuɗaɗen,” inji shi.

 

LABARAI MASU NASABA

Sauya Sheƙa: Diri Da Wasu Na Guje Wa Matsalolin Da Suka Ƙirƙiro – Dickson

Gwamna Diri Da ’Yan Majalisa 23 Na Bayelsa Sun Fice Daga PDP

“Har gara a damƙa waɗannan ayyuka ga kamfanoni masu zaman kan su, a zaftare ko a cire masu haraji. A gina manyan ayyukan da kuɗaɗen su, sannan su kula su karɓi kuɗaɗen da su ka kashe wajen gudanar da ayyukan. To ya haka ne za mu samu ci gaba, bunƙasa, samar da ayyukan yi da kuma samun yalwar arziki a faɗin ƙasar nan.”

Atiku

A wurin taron dai Atiku ya yi alƙawarin ɗaukar ‘yan sanda 500,000, sojoji 500,000.

 

Ɗan takarar shugaban ƙasa na PDP a zaɓen 2023 Atiku Abubakar, ya ƙudiri aniyar ɗaukar sojoji da ‘yan sanda milyan ɗaya idan ya zama shugaban ƙasa.

 

Sannan kuma ya ce za a wadatar da su da ingantattun kayan aiki tare da ba su horo, domin samar da tsaro, aikin yi da kuma bunƙasa tattalin arzikin ƙasa.

 

Atiku ya yi wannan alwashin a lokacin da ya ke ganawa da shugabannin Kungiyar Editoci ta Ƙasa (NGE), a Legas, a ranar Laraba.

 

Ya ce wannan ƙudiri na cikin ajandojin sa biyar muddin ya lashe zaɓen shugaban ƙasa a 2023.

 

Ajandar sa ta biyu kuwa cewa ya yi ita ce farfaɗo da tattalin arzikin ƙasa wanda kowa ya san ya taɓarɓare.

 

“Na ƙudiri aniyar ci gaba da irin tsarin da mu ka yi tsakanin 1999 zuwa 2007, lokacin ina mataimakin tsohon Shugaban Ƙasa Olusegun Obasanjo. Za mu bai wa kamfanoni masu zaman kan su damar samun sauƙin ayyukan bunƙasa tattalin arziki.”

 

Daga cikin abin da zai yi wa kamfanonin, Atiku ya ce zai rage masu haraji ta yadda za su riƙa yin manyan ayyukan raya ƙasa, kamar gina tashoshin ruwa, manyan titina, hanyoyin jiragen ƙasa da sauran manyan ayyuka masu cin kuɗaɗe sosai, “musamman tunda gwamnati ba irin waɗannan maƙudan kuɗaɗe gare ta ba.

 

“Saboda zan zaftare wa kamfanoni da masana’antu haraji, ta yadda su kuma za su riƙa gina manyan ayyukan raya ƙasa, waɗanda ke buƙatar kashe maƙudan kuɗaɗe kafin aikwatar da su.”

 

Atiku ya ce zai rungumi kowane yanki ba tare da nuna bambanci ko fifiko ba. Ya ce fifikon wani yanki da wannan gwamnatin ta riƙa bayarwa wajen raba muƙamai ba zai faru a gwamnatin sa ba, idan ya zama shugaban ƙasa.

Atiku

Cikin wata sanarwa da Kakakin Yaɗa Labarai na Gwamna Aminu Tambuwal, mai suna Mohammed Bello ya fitar bayan ganawar, Daraktan Kamfen ɗin Atiku/Yakuwa 2023, wato Gwamna Aminu Tambuwal na Sokoto, ya jinjina wa NGE da Ƙungiyar ‘Yan Jaridu ta Ƙasa (NUJ) wajen jajircewar su domin ganin dimokraɗiyya ta ɗore a ƙasar nan. Ya ce Atiku a shirye ya ke ya fara aiki wurjanjan da zaran an zaɓe ya zama shugaban ƙasa.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Sauya Sheƙa: Diri Da Wasu Na Guje Wa Matsalolin Da Suka Ƙirƙiro – Dickson
Manyan Labarai

Sauya Sheƙa: Diri Da Wasu Na Guje Wa Matsalolin Da Suka Ƙirƙiro – Dickson

October 16, 2025
Gwamna Diri Da ’Yan Majalisa 23 Na Bayelsa Sun Fice Daga PDP
Da ɗumi-ɗuminsa

Gwamna Diri Da ’Yan Majalisa 23 Na Bayelsa Sun Fice Daga PDP

October 15, 2025
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista
Manyan Labarai

2027: Babu Ɗan Siyasar Da Zai Iya Ƙalubalantar Tinubu — Fadar Shugaban Ƙasa

October 15, 2025
Next Post
Kotu Ta Dage Karar Da Hukumar Kasuwar Abubakar Rimi Ta Shigar

Kotu Ta Dage Karar Da Hukumar Kasuwar Abubakar Rimi Ta Shigar

LABARAI MASU NASABA

Sauya Sheƙa: Diri Da Wasu Na Guje Wa Matsalolin Da Suka Ƙirƙiro – Dickson

Sauya Sheƙa: Diri Da Wasu Na Guje Wa Matsalolin Da Suka Ƙirƙiro – Dickson

October 16, 2025
Sashen Cinikayyar Kamfanonin Sarrafa Hajoji Na Sin Ya Bunkasa Da Kaso 4.7 Bisa Dari Cikin Watanni Tara Na Farkon Shekarar Nan

Sashen Cinikayyar Kamfanonin Sarrafa Hajoji Na Sin Ya Bunkasa Da Kaso 4.7 Bisa Dari Cikin Watanni Tara Na Farkon Shekarar Nan

October 15, 2025
Kafafen Sada Zumunta Na Zamani Suna Taimakawa Wajen Ta’azzara Matsalar Tsaro A Arewa – Yari 

Kafafen Sada Zumunta Na Zamani Suna Taimakawa Wajen Ta’azzara Matsalar Tsaro A Arewa – Yari 

October 15, 2025
Nazarin CGTN: Jamaar Duniya Sun Yi Ammana Amurka Za Ta Fi Jin Jiki Daga Yakin Haraji 

Nazarin CGTN: Jamaar Duniya Sun Yi Ammana Amurka Za Ta Fi Jin Jiki Daga Yakin Haraji 

October 15, 2025
Kotu Ta Ɗaure Mai Horas Da ‘Yan Wasa Shekaru 8 Sakamakon Zargin Luwaɗi Da Ƙaramin Yaro A Kano

Kotu Ta Ɗaure Mai Horas Da ‘Yan Wasa Shekaru 8 Sakamakon Zargin Luwaɗi Da Ƙaramin Yaro A Kano

October 15, 2025
Sojoji Sun Yi Juyin Mulki A Ƙasar Madagascar

Sojoji Sun Yi Juyin Mulki A Ƙasar Madagascar

October 15, 2025
Shugaban Zaunannen Kwamitin Majalisar Wakilan Jama’ar Sin Ya Gana Da Mukaddashin Shugaban Majalisar Dattawan Kasar Liberia

Shugaban Zaunannen Kwamitin Majalisar Wakilan Jama’ar Sin Ya Gana Da Mukaddashin Shugaban Majalisar Dattawan Kasar Liberia

October 15, 2025
Gwamnan Kaduna Ya Taya Al’Amin Murnar Nasarar Lashe Gasar Ƙirƙirar Fasaha Ta Duniya A Ƙasar Birtaniya 

Gwamnan Kaduna Ya Taya Al’Amin Murnar Nasarar Lashe Gasar Ƙirƙirar Fasaha Ta Duniya A Ƙasar Birtaniya 

October 15, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Ladan Bosso Ya Ajiye Aikin Horar Da Barau Fc 

Da Ɗumi-ɗumi: Ladan Bosso Ya Ajiye Aikin Horar Da Barau Fc 

October 15, 2025
An Bude Bikin Baje Kolin Kasuwanci Na Kasa Da Kasa Na 138 A Guangzhou

An Bude Bikin Baje Kolin Kasuwanci Na Kasa Da Kasa Na 138 A Guangzhou

October 15, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.