ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, November 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: Tashoshin Jiragen Ruwa Da Na Kasa Da Matatun Mai Duk ‘Yan Kasuwa Zan Ba —Atiku

by Sulaiman
3 years ago
Atiku

A ci gaba da bayyana manufofin gwamnatin da zai kafa idan ya yi nasara, ɗan takarar shugaban ƙasa a PDP, Atiku Abubakar, ya yi alƙawarin damƙa manyan ayyukan raya ƙasa a hannun kamfanoni masu zaman kan su, ta yadda zai sauƙaƙe wa Gwamnatin Tarayya nauyi da wahalhalun kashe maƙudan kuɗaɗe wajen gudanar da ayyukan raya ƙasa.

 

Atiku ya bayyana haka a taron ganawar da ya yi da Kungiyar Editocin Najeriya a Legas.

ADVERTISEMENT
  • Hadari Gabas…Yadda Tattaunawar Tinubu Da Atiku Lokacin Da Suka Hadu A Abuja Ya Gudana

“Idan ku ka kalli irin gagarimin ayyukan da ke gaban gwamnati a ƙasar nan, kamar gina tashoshi jiragen ruwa, gina hanyoyin jiragen ƙasa, to ana buƙatar maƙudan kuɗaɗe ne. Kuma kun dai san a yanzu gwamnati ba ta da waɗannan kuɗaɗen,” inji shi.

 

LABARAI MASU NASABA

Kakakin Majalisar Taraba Da Ƴan Majalisa 15 Sun Fice Daga PDP Zuwa APC

Sanusi II Kaɗai Muka Sani A Matsayin Halataccen Sarkin Kano – Kwankwaso

“Har gara a damƙa waɗannan ayyuka ga kamfanoni masu zaman kan su, a zaftare ko a cire masu haraji. A gina manyan ayyukan da kuɗaɗen su, sannan su kula su karɓi kuɗaɗen da su ka kashe wajen gudanar da ayyukan. To ya haka ne za mu samu ci gaba, bunƙasa, samar da ayyukan yi da kuma samun yalwar arziki a faɗin ƙasar nan.”

Atiku

A wurin taron dai Atiku ya yi alƙawarin ɗaukar ‘yan sanda 500,000, sojoji 500,000.

 

Ɗan takarar shugaban ƙasa na PDP a zaɓen 2023 Atiku Abubakar, ya ƙudiri aniyar ɗaukar sojoji da ‘yan sanda milyan ɗaya idan ya zama shugaban ƙasa.

 

Sannan kuma ya ce za a wadatar da su da ingantattun kayan aiki tare da ba su horo, domin samar da tsaro, aikin yi da kuma bunƙasa tattalin arzikin ƙasa.

 

Atiku ya yi wannan alwashin a lokacin da ya ke ganawa da shugabannin Kungiyar Editoci ta Ƙasa (NGE), a Legas, a ranar Laraba.

 

Ya ce wannan ƙudiri na cikin ajandojin sa biyar muddin ya lashe zaɓen shugaban ƙasa a 2023.

 

Ajandar sa ta biyu kuwa cewa ya yi ita ce farfaɗo da tattalin arzikin ƙasa wanda kowa ya san ya taɓarɓare.

 

“Na ƙudiri aniyar ci gaba da irin tsarin da mu ka yi tsakanin 1999 zuwa 2007, lokacin ina mataimakin tsohon Shugaban Ƙasa Olusegun Obasanjo. Za mu bai wa kamfanoni masu zaman kan su damar samun sauƙin ayyukan bunƙasa tattalin arziki.”

 

Daga cikin abin da zai yi wa kamfanonin, Atiku ya ce zai rage masu haraji ta yadda za su riƙa yin manyan ayyukan raya ƙasa, kamar gina tashoshin ruwa, manyan titina, hanyoyin jiragen ƙasa da sauran manyan ayyuka masu cin kuɗaɗe sosai, “musamman tunda gwamnati ba irin waɗannan maƙudan kuɗaɗe gare ta ba.

 

“Saboda zan zaftare wa kamfanoni da masana’antu haraji, ta yadda su kuma za su riƙa gina manyan ayyukan raya ƙasa, waɗanda ke buƙatar kashe maƙudan kuɗaɗe kafin aikwatar da su.”

 

Atiku ya ce zai rungumi kowane yanki ba tare da nuna bambanci ko fifiko ba. Ya ce fifikon wani yanki da wannan gwamnatin ta riƙa bayarwa wajen raba muƙamai ba zai faru a gwamnatin sa ba, idan ya zama shugaban ƙasa.

Atiku

Cikin wata sanarwa da Kakakin Yaɗa Labarai na Gwamna Aminu Tambuwal, mai suna Mohammed Bello ya fitar bayan ganawar, Daraktan Kamfen ɗin Atiku/Yakuwa 2023, wato Gwamna Aminu Tambuwal na Sokoto, ya jinjina wa NGE da Ƙungiyar ‘Yan Jaridu ta Ƙasa (NUJ) wajen jajircewar su domin ganin dimokraɗiyya ta ɗore a ƙasar nan. Ya ce Atiku a shirye ya ke ya fara aiki wurjanjan da zaran an zaɓe ya zama shugaban ƙasa.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kakakin Majalisar Taraba Da Ƴan Majalisa 15 Sun Fice Daga PDP Zuwa APC
Manyan Labarai

Kakakin Majalisar Taraba Da Ƴan Majalisa 15 Sun Fice Daga PDP Zuwa APC

November 17, 2025
Yanzu Satar Da Kuka Yi Ba Ta Da Amfani: Kwankwaso Ga Gwamnonin APC
Manyan Labarai

Sanusi II Kaɗai Muka Sani A Matsayin Halataccen Sarkin Kano – Kwankwaso

November 15, 2025
Wakilai Daga Jihohi 19 Sun Isa Ibadan Don Taron PDP Na Ƙasa
Siyasa

Wakilai Daga Jihohi 19 Sun Isa Ibadan Don Taron PDP Na Ƙasa

November 15, 2025
Next Post
Kotu Ta Dage Karar Da Hukumar Kasuwar Abubakar Rimi Ta Shigar

Kotu Ta Dage Karar Da Hukumar Kasuwar Abubakar Rimi Ta Shigar

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Sin Ba Ta Taba Bukatar Kamfanoni Su Tattara Ko Adana Bayanai Ba Bisa Ka’ida Ba Kuma Ba Za Ta Yi Hakan Ba 

Gwamnatin Sin Ba Ta Taba Bukatar Kamfanoni Su Tattara Ko Adana Bayanai Ba Bisa Ka’ida Ba Kuma Ba Za Ta Yi Hakan Ba 

November 17, 2025
Adadin Motocin Da Sin Ke Fitarwa Waje Ya Karu Da Kashi 15.7 Cikin Watanni 10 Na Farkon Bana

Adadin Motocin Da Sin Ke Fitarwa Waje Ya Karu Da Kashi 15.7 Cikin Watanni 10 Na Farkon Bana

November 17, 2025
Farashin Kayan Abinci Na Cigaba Da Sauka A Jihohin Arewa Maso Gabas

Farashin Kayan Abinci Na Cigaba Da Sauka A Jihohin Arewa Maso Gabas

November 17, 2025
An Bude Taron Tattaunawa Kan Wayewar Kai Tsakanin Sin Da Kasashen Larabawa Karo Na 11 A Beijing

An Bude Taron Tattaunawa Kan Wayewar Kai Tsakanin Sin Da Kasashen Larabawa Karo Na 11 A Beijing

November 17, 2025
NBS

Hauhawar Farashin Kayayyaki A Nijeriya Ta Ragu Zuwa Kashi 16.065%

November 17, 2025
Firaministan Sin Ya Isa Rasha Domin Halartar Taron SCO

Firaministan Sin Ya Isa Rasha Domin Halartar Taron SCO

November 17, 2025
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

November 17, 2025
Kudaden Kasafin Kudin Sin Sun Karu Da Kashi 0.8 Cikin Watanni 10 Na Farkon Bana

Kudaden Kasafin Kudin Sin Sun Karu Da Kashi 0.8 Cikin Watanni 10 Na Farkon Bana

November 17, 2025
Rashin Tsaro: Atiku Ya Yi Allah-wadai Da Harin Makarantar ‘Yan Mata Ta Kebbi

Rashin Tsaro: Atiku Ya Yi Allah-wadai Da Harin Makarantar ‘Yan Mata Ta Kebbi

November 17, 2025
An Sanya Hannu Kan Yarjejeniyoyin Cinikayya Na Biliyoyin Kudi Yayin Baje Kolin CHTF Na Kasar Sin

An Sanya Hannu Kan Yarjejeniyoyin Cinikayya Na Biliyoyin Kudi Yayin Baje Kolin CHTF Na Kasar Sin

November 17, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.