• English
  • Business News
Saturday, June 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: Tashoshin Jiragen Ruwa Da Na Kasa Da Matatun Mai Duk ‘Yan Kasuwa Zan Ba —Atiku

by Sulaiman
3 years ago
in Siyasa
0
2023: Tashoshin Jiragen Ruwa Da Na Kasa Da Matatun Mai Duk ‘Yan Kasuwa Zan Ba —Atiku
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A ci gaba da bayyana manufofin gwamnatin da zai kafa idan ya yi nasara, ɗan takarar shugaban ƙasa a PDP, Atiku Abubakar, ya yi alƙawarin damƙa manyan ayyukan raya ƙasa a hannun kamfanoni masu zaman kan su, ta yadda zai sauƙaƙe wa Gwamnatin Tarayya nauyi da wahalhalun kashe maƙudan kuɗaɗe wajen gudanar da ayyukan raya ƙasa.

 

Atiku ya bayyana haka a taron ganawar da ya yi da Kungiyar Editocin Najeriya a Legas.

  • Hadari Gabas…Yadda Tattaunawar Tinubu Da Atiku Lokacin Da Suka Hadu A Abuja Ya Gudana

“Idan ku ka kalli irin gagarimin ayyukan da ke gaban gwamnati a ƙasar nan, kamar gina tashoshi jiragen ruwa, gina hanyoyin jiragen ƙasa, to ana buƙatar maƙudan kuɗaɗe ne. Kuma kun dai san a yanzu gwamnati ba ta da waɗannan kuɗaɗen,” inji shi.

 

Labarai Masu Nasaba

Leicester City Ta Sallami Ruud van Nistelrooy A Matsayin Kocinta

Ganduje Ya Ajiye Shugabancin Jam’iyyar APC

“Har gara a damƙa waɗannan ayyuka ga kamfanoni masu zaman kan su, a zaftare ko a cire masu haraji. A gina manyan ayyukan da kuɗaɗen su, sannan su kula su karɓi kuɗaɗen da su ka kashe wajen gudanar da ayyukan. To ya haka ne za mu samu ci gaba, bunƙasa, samar da ayyukan yi da kuma samun yalwar arziki a faɗin ƙasar nan.”

Atiku

A wurin taron dai Atiku ya yi alƙawarin ɗaukar ‘yan sanda 500,000, sojoji 500,000.

 

Ɗan takarar shugaban ƙasa na PDP a zaɓen 2023 Atiku Abubakar, ya ƙudiri aniyar ɗaukar sojoji da ‘yan sanda milyan ɗaya idan ya zama shugaban ƙasa.

 

Sannan kuma ya ce za a wadatar da su da ingantattun kayan aiki tare da ba su horo, domin samar da tsaro, aikin yi da kuma bunƙasa tattalin arzikin ƙasa.

 

Atiku ya yi wannan alwashin a lokacin da ya ke ganawa da shugabannin Kungiyar Editoci ta Ƙasa (NGE), a Legas, a ranar Laraba.

 

Ya ce wannan ƙudiri na cikin ajandojin sa biyar muddin ya lashe zaɓen shugaban ƙasa a 2023.

 

Ajandar sa ta biyu kuwa cewa ya yi ita ce farfaɗo da tattalin arzikin ƙasa wanda kowa ya san ya taɓarɓare.

 

“Na ƙudiri aniyar ci gaba da irin tsarin da mu ka yi tsakanin 1999 zuwa 2007, lokacin ina mataimakin tsohon Shugaban Ƙasa Olusegun Obasanjo. Za mu bai wa kamfanoni masu zaman kan su damar samun sauƙin ayyukan bunƙasa tattalin arziki.”

 

Daga cikin abin da zai yi wa kamfanonin, Atiku ya ce zai rage masu haraji ta yadda za su riƙa yin manyan ayyukan raya ƙasa, kamar gina tashoshin ruwa, manyan titina, hanyoyin jiragen ƙasa da sauran manyan ayyuka masu cin kuɗaɗe sosai, “musamman tunda gwamnati ba irin waɗannan maƙudan kuɗaɗe gare ta ba.

 

“Saboda zan zaftare wa kamfanoni da masana’antu haraji, ta yadda su kuma za su riƙa gina manyan ayyukan raya ƙasa, waɗanda ke buƙatar kashe maƙudan kuɗaɗe kafin aikwatar da su.”

 

Atiku ya ce zai rungumi kowane yanki ba tare da nuna bambanci ko fifiko ba. Ya ce fifikon wani yanki da wannan gwamnatin ta riƙa bayarwa wajen raba muƙamai ba zai faru a gwamnatin sa ba, idan ya zama shugaban ƙasa.

Atiku

Cikin wata sanarwa da Kakakin Yaɗa Labarai na Gwamna Aminu Tambuwal, mai suna Mohammed Bello ya fitar bayan ganawar, Daraktan Kamfen ɗin Atiku/Yakuwa 2023, wato Gwamna Aminu Tambuwal na Sokoto, ya jinjina wa NGE da Ƙungiyar ‘Yan Jaridu ta Ƙasa (NUJ) wajen jajircewar su domin ganin dimokraɗiyya ta ɗore a ƙasar nan. Ya ce Atiku a shirye ya ke ya fara aiki wurjanjan da zaran an zaɓe ya zama shugaban ƙasa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ra’ayoyinku A Kan Shigowar Hunturu

Next Post

Kotu Ta Dage Karar Da Hukumar Kasuwar Abubakar Rimi Ta Shigar

Related

Leicester City Ta Sallami Ruud van Nistelrooy A Matsayin Kocinta
Siyasa

Leicester City Ta Sallami Ruud van Nistelrooy A Matsayin Kocinta

23 hours ago
Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka
Manyan Labarai

Ganduje Ya Ajiye Shugabancin Jam’iyyar APC

1 day ago
Zaɓen 2027 Ya Fi Damun Tinubu Fiye Da Gudanar Da Shugabanci – Sanata Dickson
Siyasa

Zaɓen 2027 Ya Fi Damun Tinubu Fiye Da Gudanar Da Shugabanci – Sanata Dickson

1 day ago
Gwamnatin APC Ta Kara Ingiza ‘Yan NIjeriya Cikin Bakin Talauci – PDP
Manyan Labarai

PDP Ta Soke Babban Taronta, Ta Dawo Da Anyanwu A Matsayin Sakatarenta

3 days ago
Tinubu Ya Haƙura Da Tsayawa Takara A 2027 – Jigo A APC
Manyan Labarai

Tinubu Ya Haƙura Da Tsayawa Takara A 2027 – Jigo A APC

4 days ago
An Fara Kiraye-Kirayen Tinubu Ya Zaɓi Barau Jibrin A Mataimakinsa Na 2027
Siyasa

An Fara Kiraye-Kirayen Tinubu Ya Zaɓi Barau Jibrin A Mataimakinsa Na 2027

5 days ago
Next Post
Kotu Ta Dage Karar Da Hukumar Kasuwar Abubakar Rimi Ta Shigar

Kotu Ta Dage Karar Da Hukumar Kasuwar Abubakar Rimi Ta Shigar

LABARAI MASU NASABA

An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

June 28, 2025
Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

June 28, 2025
Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

June 28, 2025
Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

June 28, 2025
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

June 28, 2025
Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

June 28, 2025
An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

June 28, 2025
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

June 28, 2025
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

June 28, 2025
Sin Ta Samu Nasarorin A Zo A Gani Wajen Yaki Da Miyagun Kwayoyi

Sin Ta Samu Nasarorin A Zo A Gani Wajen Yaki Da Miyagun Kwayoyi

June 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.