ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, September 18, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: Tashoshin Jiragen Ruwa Da Na Kasa Da Matatun Mai Duk ‘Yan Kasuwa Zan Ba —Atiku

by Sulaiman
4 years ago
Atiku

A ci gaba da bayyana manufofin gwamnatin da zai kafa idan ya yi nasara, ɗan takarar shugaban ƙasa a PDP, Atiku Abubakar, ya yi alƙawarin damƙa manyan ayyukan raya ƙasa a hannun kamfanoni masu zaman kan su, ta yadda zai sauƙaƙe wa Gwamnatin Tarayya nauyi da wahalhalun kashe maƙudan kuɗaɗe wajen gudanar da ayyukan raya ƙasa.

 

Atiku ya bayyana haka a taron ganawar da ya yi da Kungiyar Editocin Najeriya a Legas.

ADVERTISEMENT
  • Hadari Gabas…Yadda Tattaunawar Tinubu Da Atiku Lokacin Da Suka Hadu A Abuja Ya Gudana

“Idan ku ka kalli irin gagarimin ayyukan da ke gaban gwamnati a ƙasar nan, kamar gina tashoshi jiragen ruwa, gina hanyoyin jiragen ƙasa, to ana buƙatar maƙudan kuɗaɗe ne. Kuma kun dai san a yanzu gwamnati ba ta da waɗannan kuɗaɗen,” inji shi.

 

LABARAI MASU NASABA

Ban Taɓa Yi Wa Tinubu Alƙawarin Zan Koma APC Ba – Wike

An Gudanar Da Sallar Zana’idar Tsohon Gwamnan Gongola

“Har gara a damƙa waɗannan ayyuka ga kamfanoni masu zaman kan su, a zaftare ko a cire masu haraji. A gina manyan ayyukan da kuɗaɗen su, sannan su kula su karɓi kuɗaɗen da su ka kashe wajen gudanar da ayyukan. To ya haka ne za mu samu ci gaba, bunƙasa, samar da ayyukan yi da kuma samun yalwar arziki a faɗin ƙasar nan.”

Atiku

A wurin taron dai Atiku ya yi alƙawarin ɗaukar ‘yan sanda 500,000, sojoji 500,000.

 

Ɗan takarar shugaban ƙasa na PDP a zaɓen 2023 Atiku Abubakar, ya ƙudiri aniyar ɗaukar sojoji da ‘yan sanda milyan ɗaya idan ya zama shugaban ƙasa.

 

Sannan kuma ya ce za a wadatar da su da ingantattun kayan aiki tare da ba su horo, domin samar da tsaro, aikin yi da kuma bunƙasa tattalin arzikin ƙasa.

 

Atiku ya yi wannan alwashin a lokacin da ya ke ganawa da shugabannin Kungiyar Editoci ta Ƙasa (NGE), a Legas, a ranar Laraba.

 

Ya ce wannan ƙudiri na cikin ajandojin sa biyar muddin ya lashe zaɓen shugaban ƙasa a 2023.

 

Ajandar sa ta biyu kuwa cewa ya yi ita ce farfaɗo da tattalin arzikin ƙasa wanda kowa ya san ya taɓarɓare.

 

“Na ƙudiri aniyar ci gaba da irin tsarin da mu ka yi tsakanin 1999 zuwa 2007, lokacin ina mataimakin tsohon Shugaban Ƙasa Olusegun Obasanjo. Za mu bai wa kamfanoni masu zaman kan su damar samun sauƙin ayyukan bunƙasa tattalin arziki.”

 

Daga cikin abin da zai yi wa kamfanonin, Atiku ya ce zai rage masu haraji ta yadda za su riƙa yin manyan ayyukan raya ƙasa, kamar gina tashoshin ruwa, manyan titina, hanyoyin jiragen ƙasa da sauran manyan ayyuka masu cin kuɗaɗe sosai, “musamman tunda gwamnati ba irin waɗannan maƙudan kuɗaɗe gare ta ba.

 

“Saboda zan zaftare wa kamfanoni da masana’antu haraji, ta yadda su kuma za su riƙa gina manyan ayyukan raya ƙasa, waɗanda ke buƙatar kashe maƙudan kuɗaɗe kafin aikwatar da su.”

 

Atiku ya ce zai rungumi kowane yanki ba tare da nuna bambanci ko fifiko ba. Ya ce fifikon wani yanki da wannan gwamnatin ta riƙa bayarwa wajen raba muƙamai ba zai faru a gwamnatin sa ba, idan ya zama shugaban ƙasa.

Atiku

Cikin wata sanarwa da Kakakin Yaɗa Labarai na Gwamna Aminu Tambuwal, mai suna Mohammed Bello ya fitar bayan ganawar, Daraktan Kamfen ɗin Atiku/Yakuwa 2023, wato Gwamna Aminu Tambuwal na Sokoto, ya jinjina wa NGE da Ƙungiyar ‘Yan Jaridu ta Ƙasa (NUJ) wajen jajircewar su domin ganin dimokraɗiyya ta ɗore a ƙasar nan. Ya ce Atiku a shirye ya ke ya fara aiki wurjanjan da zaran an zaɓe ya zama shugaban ƙasa.

Atiku
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Sin Ta Bukaci Japan Ta Fuskanci Tarihinta Na Mamayar Zalunci Tare Da Waiwaye Mai Zurfi A Kai
  • Sulaiman
    Kasar Sin Ta Samu Jarin Waje Kimanin Yuan Biliyan 479.95 A Watanni 8 Na FarkonBana
  • Sulaiman
    Sana’ar Aike Da Sakwanni a Sin Ta Ci Gaba Da Bunkasa Cikin Kwanciyar Hankali
  • Sulaiman
    Sin Da Amurka Na Ci Gaba Da Tuntubar Juna Game Da Shirye-shiryen Ganawar Shugabannin Kasashen Biyu Cikin Shekarar Nan

MASU ALAKA

2023: Me Ya Sa Ake Rububin Wike?
Siyasa

Ban Taɓa Yi Wa Tinubu Alƙawarin Zan Koma APC Ba – Wike

September 16, 2026
Atiku
Siyasa

An Gudanar Da Sallar Zana’idar Tsohon Gwamnan Gongola

September 13, 2026
jam'iyyu
Siyasa

An Buƙaci Ƴan Takara Su Sanya Tsare-tsaren Yaƙi Da Ɗumamar Yanayi A Jaddawalin Kamfen Ɗinsu

September 12, 2026
Next Post
Kotu Ta Dage Karar Da Hukumar Kasuwar Abubakar Rimi Ta Shigar

Kotu Ta Dage Karar Da Hukumar Kasuwar Abubakar Rimi Ta Shigar

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Bukaci Japan Ta Fuskanci Tarihinta Na Mamayar Zalunci Tare Da Waiwaye Mai Zurfi A Kai

Sin Ta Bukaci Japan Ta Fuskanci Tarihinta Na Mamayar Zalunci Tare Da Waiwaye Mai Zurfi A Kai

September 18, 2026
Atiku Ga Tinubu: Fada Wa ‘Yan Nijeriya Yadda Ka Samu Digiri Ba Tare Da Firamare Da Sakandare Ba

Atiku Ya Nemi Tinubu Ya Rage Farashin Man Fetur Don Sauƙaƙa Wa ’Yan Nijeriya Wahalar Da Suke Sha

September 18, 2026
Kasar Sin Ta Samu Jarin Waje Kimanin Yuan Biliyan 479.95 A Watanni 8 Na FarkonBana

Kasar Sin Ta Samu Jarin Waje Kimanin Yuan Biliyan 479.95 A Watanni 8 Na FarkonBana

September 18, 2026
Sana’ar Aike Da Sakwanni a Sin Ta Ci Gaba Da Bunkasa Cikin Kwanciyar Hankali

Sana’ar Aike Da Sakwanni a Sin Ta Ci Gaba Da Bunkasa Cikin Kwanciyar Hankali

September 18, 2026
‘Yan Bindiga Sun Harbi Fasinjoji 2 A Jihar Neja

Neja: An Fesa Wani Abu A Ɗakin Da Aka Tsare Mu – Matashin Da Ya Tsira

September 18, 2026
Sin Da Amurka Na Ci Gaba Da Tuntubar Juna Game Da Shirye-shiryen Ganawar Shugabannin Kasashen Biyu Cikin Shekarar Nan

Sin Da Amurka Na Ci Gaba Da Tuntubar Juna Game Da Shirye-shiryen Ganawar Shugabannin Kasashen Biyu Cikin Shekarar Nan

September 18, 2026
Samun Ci Gaba Shi Ne Abu Mai Tushe Wajen Tabbatar Da Hakkin Dan Adam

Samun Ci Gaba Shi Ne Abu Mai Tushe Wajen Tabbatar Da Hakkin Dan Adam

September 18, 2026
Gwamnatin Najeriya Na Daukar Darasi Daga Salon Da Kasar Sin Ke Amfani Da Shi Na Kulla Alakar Diflomasiyya Ta Hanyar Jan Hankali Da Kyakkyawar Mu’amala

Gwamnatin Najeriya Na Daukar Darasi Daga Salon Da Kasar Sin Ke Amfani Da Shi Na Kulla Alakar Diflomasiyya Ta Hanyar Jan Hankali Da Kyakkyawar Mu’amala

September 18, 2026
ASUU Ta Janye Yajin Aiki A Jami’ar Kaduna

ASUU Ta Janye Yajin Aiki A Jami’ar Kaduna

September 18, 2026
Babban Jami’in Kasar Burundi: Ci Gaban Kasar Sin Abu Ne Mai Karfafa Wa Sauran Kasashe Gwiwa

Babban Jami’in Kasar Burundi: Ci Gaban Kasar Sin Abu Ne Mai Karfafa Wa Sauran Kasashe Gwiwa

September 18, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.