• English
  • Business News
Thursday, October 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2027: An Buga Gangar Neman Tazarcen Tinubu A Arewa

by Yusuf Shuaibu and Sulaiman
7 months ago
Tinubu

Kasa da shekaru biyu da mulkin Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu, wasu jiga-jigan jam’iyyar APC sun fara yakin neman sake zabensa a 2027 a yankin arewa.

Duk da cewa jam’iyyar APC ko shugaban kasa a hukumance ba su kaddamar da yakin neman zaben ba, manyan jiga-jigan jam’iyyar APC da suka hada da shugaban jam’iyyar na kasa, Abdullahi Ganduje da sakataren gwamnatin tarayya, George Akume, sun yi kira ga shugaban kasa ya sake tsayawa takara a karo na biyu.

  • Me Ya Sa Jama’ar Turai Ke Adawa Da Sayen Kayayyaki Kirar Amurka?
  • Kasar Sin Ce Ke Kan Gaba A Matsayin Kasar Da Ta Fi Samun Jari Daga Ketare

A kwanakin baya, Ganduje, yayin da yake karbar bakuncin kungiyoyin magoya bayan jam’iyyar APC a shalkwatan jam’iyyar da ke Abuja, ya bukaci ‘yan siyasar arewa masu rubibin tsayawa takarar shugaban kasa a zaben 2027 da su kawar da burinsu har zuwa 2031, domin Tinubu zai kammala wa’adinsa na biyu.

Akume, yayin da yake magana a wani shirin gidan talabijin na TBC, ya kuma shawarci tsohon mataimakin shugaban kasa kuma dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP a zaben da ya gabata, Atiku Abubakar da sauran ’yan arewa da kada su nemi kujerar takarar shugaban kasa a 2027.

An kuma lura cewa an fara yakin neman zaben shugaban kasa a jihohin Kaduna, Kebbi da Kwara, yayin da aka kuma ga allunan sake zaben shugaban kasa a wurare daban-daban a Abuja.

LABARAI MASU NASABA

Peter Obi Ya Bukaci INEC Ta Tabbatar Da Shaidar Karatun Dan Takara Kafin Shiga Zabe

Maƙiyan Jonathan Ne Kaɗai Za Su Zuga Shi Ya Fito Takara A 2027 – Oshiomhole

Wannan lamari ci gaban da haifar da zazzafar martani daga jam’iyyun adawa da manazarta siyasa wadanda suka yi zargin cewa hakan ya saba wa dokar zabe da kundin tsarin mulkin 1999 wanda aka yi wa kwaskwarima.

Masana harkokin shari’a da masu sharhi kan harkokin siyasa na ganin cewa irin wannan kamfen da ba a kai ba, yana kawo cikas ga dimokuradiyya, da bin doka da oda da kuma tsarin zabe.

A watan da ya gabata ne jam’iyyar APC ta kaddamar da yakin neman zaben shugaban kasa, Tinubu da Gwamna Nasir Idris a Jihar Kebbi as zaben 2027.

Taron wanda aka gudanar a babban filin wasa na garin Birnin Kebbi, ya samu halartar ministan kasafi da tsare-tsare na tattalin arziki, Sanata Atiku Bagudu da Gwamna Nasir Idris da dan majalisar wakilai kuma abokin Tinubu, James Abiodun Faleke da karamin ministan ilimi, Yusuf Tanko Sununu da sauran shugabannin APC.

Bayan taron na Kebbi, shugabannin jam’iyyar APC, da suka hada da mataimakin shugaban majalisar dattawa, Barau I. Jibrin da sakataren jam’iyyar na kasa, Sanata Ajibola Basiru da ministan noma, Abubakar Kyari da wasu da dama sun lalubo yadda Tinubu zai sake tsayawa takara a yayin wani shirin bunkasa noma da jarin Dan’adam wanda Sanata Saliu Mustapha ya shirya a Ilorin na Jihar Kwara.

Makonnin da suka gabata, masu ruwa da tsaki na jam’iyyar APC a Jihar Kaduna sun amince tare da gamsuwa ga Shugaba Tinubu da Gwamna Uba Sani, “Saboda jagorancinsu da manufofin da suka dace da jama’a.”

A wata sanarwa da ya fitar, sakataren jam’iyyar a jihar, Yahaya Baba Pate, ya ce masu ruwa da tsaki sun ba da goyon baya ne a taron da aka gudanar a ofishin kula da Jihar Kaduna da ke Abuja. Wannan ya biyo bayan goyon bayan shugabannin biyu na kara yin wa’adin mulki a karo na da daukacin kansiloli 255 na jihar suka amince da shi.

A karshen mako, a lokacin biki da Ganduje da Sanata Barau Jibrin suka tsara, wasu daga cikin kungiyoyin masu goyon bayan Atiku Abubakar, daga jihohi 19 na arewa, yayin da suke sanar da sauya shekarsu zuwa APC sun yi alkawarin aiki don ci gaban gwamnatin Tinubu a 2027.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

peter
Tambarin Dimokuradiyya

Peter Obi Ya Bukaci INEC Ta Tabbatar Da Shaidar Karatun Dan Takara Kafin Shiga Zabe

October 10, 2025
Jonathan
Tambarin Dimokuradiyya

Maƙiyan Jonathan Ne Kaɗai Za Su Zuga Shi Ya Fito Takara A 2027 – Oshiomhole

October 10, 2025
Majalisa Na Duba Yiwuwar Amincewa Da Gudanar Da Zaɓen 2027 A Rana Ɗaya
Tambarin Dimokuradiyya

Majalisa Na Duba Yiwuwar Amincewa Da Gudanar Da Zaɓen 2027 A Rana Ɗaya

October 10, 2025
Next Post
Manchester United Ta Kai Zagayen Gaba Na Gasar Europa League 

Manchester United Ta Kai Zagayen Gaba Na Gasar Europa League 

LABARAI MASU NASABA

An Kashe Mutum 13 A Wasu Sabbin Hare-Hare A Ƙauyukan Filato

An Kashe Mutum 13 A Wasu Sabbin Hare-Hare A Ƙauyukan Filato

October 16, 2025
Sauya Sheƙa: Diri Da Wasu Na Guje Wa Matsalolin Da Suka Ƙirƙiro – Dickson

Sauya Sheƙa: Diri Da Wasu Na Guje Wa Matsalolin Da Suka Ƙirƙiro – Dickson

October 16, 2025
Sashen Cinikayyar Kamfanonin Sarrafa Hajoji Na Sin Ya Bunkasa Da Kaso 4.7 Bisa Dari Cikin Watanni Tara Na Farkon Shekarar Nan

Sashen Cinikayyar Kamfanonin Sarrafa Hajoji Na Sin Ya Bunkasa Da Kaso 4.7 Bisa Dari Cikin Watanni Tara Na Farkon Shekarar Nan

October 15, 2025
Kafafen Sada Zumunta Na Zamani Suna Taimakawa Wajen Ta’azzara Matsalar Tsaro A Arewa – Yari 

Kafafen Sada Zumunta Na Zamani Suna Taimakawa Wajen Ta’azzara Matsalar Tsaro A Arewa – Yari 

October 15, 2025
Nazarin CGTN: Jamaar Duniya Sun Yi Ammana Amurka Za Ta Fi Jin Jiki Daga Yakin Haraji 

Nazarin CGTN: Jamaar Duniya Sun Yi Ammana Amurka Za Ta Fi Jin Jiki Daga Yakin Haraji 

October 15, 2025
Kotu Ta Ɗaure Mai Horas Da ‘Yan Wasa Shekaru 8 Sakamakon Zargin Luwaɗi Da Ƙaramin Yaro A Kano

Kotu Ta Ɗaure Mai Horas Da ‘Yan Wasa Shekaru 8 Sakamakon Zargin Luwaɗi Da Ƙaramin Yaro A Kano

October 15, 2025
Sojoji Sun Yi Juyin Mulki A Ƙasar Madagascar

Sojoji Sun Yi Juyin Mulki A Ƙasar Madagascar

October 15, 2025
Shugaban Zaunannen Kwamitin Majalisar Wakilan Jama’ar Sin Ya Gana Da Mukaddashin Shugaban Majalisar Dattawan Kasar Liberia

Shugaban Zaunannen Kwamitin Majalisar Wakilan Jama’ar Sin Ya Gana Da Mukaddashin Shugaban Majalisar Dattawan Kasar Liberia

October 15, 2025
Gwamnan Kaduna Ya Taya Al’Amin Murnar Nasarar Lashe Gasar Ƙirƙirar Fasaha Ta Duniya A Ƙasar Birtaniya 

Gwamnan Kaduna Ya Taya Al’Amin Murnar Nasarar Lashe Gasar Ƙirƙirar Fasaha Ta Duniya A Ƙasar Birtaniya 

October 15, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Ladan Bosso Ya Ajiye Aikin Horar Da Barau Fc 

Da Ɗumi-ɗumi: Ladan Bosso Ya Ajiye Aikin Horar Da Barau Fc 

October 15, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.