ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 17, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2027: An Buga Gangar Neman Tazarcen Tinubu A Arewa

by Yusuf Shuaibu and Sulaiman
1 year ago
Tinubu

Kasa da shekaru biyu da mulkin Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu, wasu jiga-jigan jam’iyyar APC sun fara yakin neman sake zabensa a 2027 a yankin arewa.

Duk da cewa jam’iyyar APC ko shugaban kasa a hukumance ba su kaddamar da yakin neman zaben ba, manyan jiga-jigan jam’iyyar APC da suka hada da shugaban jam’iyyar na kasa, Abdullahi Ganduje da sakataren gwamnatin tarayya, George Akume, sun yi kira ga shugaban kasa ya sake tsayawa takara a karo na biyu.

  • Me Ya Sa Jama’ar Turai Ke Adawa Da Sayen Kayayyaki Kirar Amurka?
  • Kasar Sin Ce Ke Kan Gaba A Matsayin Kasar Da Ta Fi Samun Jari Daga Ketare

A kwanakin baya, Ganduje, yayin da yake karbar bakuncin kungiyoyin magoya bayan jam’iyyar APC a shalkwatan jam’iyyar da ke Abuja, ya bukaci ‘yan siyasar arewa masu rubibin tsayawa takarar shugaban kasa a zaben 2027 da su kawar da burinsu har zuwa 2031, domin Tinubu zai kammala wa’adinsa na biyu.

ADVERTISEMENT

Akume, yayin da yake magana a wani shirin gidan talabijin na TBC, ya kuma shawarci tsohon mataimakin shugaban kasa kuma dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP a zaben da ya gabata, Atiku Abubakar da sauran ’yan arewa da kada su nemi kujerar takarar shugaban kasa a 2027.

An kuma lura cewa an fara yakin neman zaben shugaban kasa a jihohin Kaduna, Kebbi da Kwara, yayin da aka kuma ga allunan sake zaben shugaban kasa a wurare daban-daban a Abuja.

LABARAI MASU NASABA

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

Wannan lamari ci gaban da haifar da zazzafar martani daga jam’iyyun adawa da manazarta siyasa wadanda suka yi zargin cewa hakan ya saba wa dokar zabe da kundin tsarin mulkin 1999 wanda aka yi wa kwaskwarima.

Masana harkokin shari’a da masu sharhi kan harkokin siyasa na ganin cewa irin wannan kamfen da ba a kai ba, yana kawo cikas ga dimokuradiyya, da bin doka da oda da kuma tsarin zabe.

A watan da ya gabata ne jam’iyyar APC ta kaddamar da yakin neman zaben shugaban kasa, Tinubu da Gwamna Nasir Idris a Jihar Kebbi as zaben 2027.

Taron wanda aka gudanar a babban filin wasa na garin Birnin Kebbi, ya samu halartar ministan kasafi da tsare-tsare na tattalin arziki, Sanata Atiku Bagudu da Gwamna Nasir Idris da dan majalisar wakilai kuma abokin Tinubu, James Abiodun Faleke da karamin ministan ilimi, Yusuf Tanko Sununu da sauran shugabannin APC.

Bayan taron na Kebbi, shugabannin jam’iyyar APC, da suka hada da mataimakin shugaban majalisar dattawa, Barau I. Jibrin da sakataren jam’iyyar na kasa, Sanata Ajibola Basiru da ministan noma, Abubakar Kyari da wasu da dama sun lalubo yadda Tinubu zai sake tsayawa takara a yayin wani shirin bunkasa noma da jarin Dan’adam wanda Sanata Saliu Mustapha ya shirya a Ilorin na Jihar Kwara.

Makonnin da suka gabata, masu ruwa da tsaki na jam’iyyar APC a Jihar Kaduna sun amince tare da gamsuwa ga Shugaba Tinubu da Gwamna Uba Sani, “Saboda jagorancinsu da manufofin da suka dace da jama’a.”

A wata sanarwa da ya fitar, sakataren jam’iyyar a jihar, Yahaya Baba Pate, ya ce masu ruwa da tsaki sun ba da goyon baya ne a taron da aka gudanar a ofishin kula da Jihar Kaduna da ke Abuja. Wannan ya biyo bayan goyon bayan shugabannin biyu na kara yin wa’adin mulki a karo na da daukacin kansiloli 255 na jihar suka amince da shi.

A karshen mako, a lokacin biki da Ganduje da Sanata Barau Jibrin suka tsara, wasu daga cikin kungiyoyin masu goyon bayan Atiku Abubakar, daga jihohi 19 na arewa, yayin da suke sanar da sauya shekarsu zuwa APC sun yi alkawarin aiki don ci gaban gwamnatin Tinubu a 2027.

Tinubu
Yusuf Shuaibu
+ posts Bio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Hukuncin Kotu Na Barazana Ga Zaben 2027 —INEC
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Matsalar Tsaro Da Tsadar Kayan Noma Na Barazana Ga Samar Da Abinci A Daminar Bana
Tinubu
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
  • Sulaiman
    Mata Ta Hallaka Mijinta Da Wuƙa Watanni Biyu Bayan Aure A Kano
  • Sulaiman
    An Kaddamar Da Wani Kwas Na Horar Da Kwararru Kan Killace Kananan Makamai Na Sin Da MDD Da Afirka 
  • Sulaiman
    Mataimakin Firaministan Sin Zai Halarci Babban Taron Shugabanni Game Da Barkewar Cutar Ebola

MASU ALAKA

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

June 12, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
Tambarin Dimokuradiyya

Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

June 12, 2026
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP
Tambarin Dimokuradiyya

Zaben Fitar Da Gwani Na APC: Tinubu Zai Shiga Tsakani Wajen Warware Rikicin Jam’iyyar

June 5, 2026
Next Post
Manchester United Ta Kai Zagayen Gaba Na Gasar Europa League 

Manchester United Ta Kai Zagayen Gaba Na Gasar Europa League 

LABARAI MASU NASABA

Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

June 17, 2026
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

Mata Ta Hallaka Mijinta Da Wuƙa Watanni Biyu Bayan Aure A Kano

June 17, 2026
An Kaddamar Da Wani Kwas Na Horar Da Kwararru Kan Killace Kananan Makamai Na Sin Da MDD Da Afirka 

An Kaddamar Da Wani Kwas Na Horar Da Kwararru Kan Killace Kananan Makamai Na Sin Da MDD Da Afirka 

June 16, 2026
Mataimakin Firaministan Sin Zai Halarci Babban Taron Shugabanni Game Da Barkewar Cutar Ebola

Mataimakin Firaministan Sin Zai Halarci Babban Taron Shugabanni Game Da Barkewar Cutar Ebola

June 16, 2026
Kotun Ɗaukaka Ƙara Ta Dakatar Da INEC Game Da Soke Rajistar ADC Da Wasu Jam’iyyu

Kotun Ɗaukaka Ƙara Ta Dakatar Da INEC Game Da Soke Rajistar ADC Da Wasu Jam’iyyu

June 16, 2026
Tattalin Arzikin Sin Ya Tafiya Cikin Kwanciyar Hankali

Tattalin Arzikin Sin Ya Tafiya Cikin Kwanciyar Hankali

June 16, 2026
Gaza

Farashin Mai Ya Faɗi Ƙasa Da Dala 80 Bayan cimma Yarjejeniyar Amurka Da Iran

June 16, 2026
Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Myanmar

Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Myanmar

June 16, 2026
Tinubu Ya Kaddamar Da Katafaren Gidajen Alƙalan Kotun Ɗaukaka Ƙara A Abuja

Tinubu Ya Kaddamar Da Katafaren Gidajen Alƙalan Kotun Ɗaukaka Ƙara A Abuja

June 16, 2026
Kasar Sin Na Samar Da Managarcin Yanayi Na Bunkasa Kirkire-kirkire Ga Masana’antun Kasa Da Kasa

Kasar Sin Na Samar Da Managarcin Yanayi Na Bunkasa Kirkire-kirkire Ga Masana’antun Kasa Da Kasa

June 16, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.