• English
  • Business News
Saturday, September 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

by Rabi'u Ali Indabawa and Sulaiman
4 months ago
in Rahotonni
0
Mulki

vector illustration of Nigeria flag and map

Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Masana sun ce maimakon su rika maida hankalinsu kan yadda Nijeriya za ta koma kan tafarkinta kamar yadda aka dade da saninta, mai tarkin jam’iyya daya, an yi kira da su ‘yan siyasa su maida hankalinsu kan yadda za su yi maganin matsananciyar fatara wadda take damun ‘yan Nijeriya.

Hakanan ma an yi kira da su maida hankalinsu yadda za ayi maganin matsalolin tsaro da sauran matsalolin wadanda suke damun Nijeriya.

  • Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu
  • Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Wadannan shawarwarin sun fito ne daga manyan Lauyoyi na kasa da masana harkokin siyasa wadanda suka yi tunani kan damuwarsu ta yadda Nijeriya za ta kasance kasa mai amfani da tafarkin jam’iyyar siyasa daya, suka ce duk da abin ba wani aikata laifi bane sai dai halin da ake ciki yanzu yana da kamar wuya.

Sun ce yadda abubuwa suke tafiya da irin halin da su ‘yan siyasar suke zai sa lamarin tafarkin jam’iyya daya a matsayin abinda zai wahalar cimmawa,duk da yake dai tsarin mulki ya bada damar mu’amala da duk wata kungiya.

A wata ganawa ta musamman da Jaridar LEADERSHIP, ta ranar Lahadi,tayi dasu sun nuna damuwarsu akan irin kwamacalar siyasar da ake yi a Nijeriya,suka kara yin bayani cewa ai yanzu babu jajircewa da tsayawa kan lamarin da aka san mutum cikin jam’iyya,wanda ya kamata ace shi ne ake sa ran zai yi ma jam’iyya siyasa, Shugabannin majalisar yanzu abin babu ya dade da kwanta dama.

Labarai Masu Nasaba

Masana Sun Dora Alhakin Rashin Cika Alkawuran ‘Yan Siyasa Kan Jam’iyyu

Rashin Aikin Yi: A Halin Yanzu Masu Digiri Na Sayar Da Fiya Wata Da Aikin Achaba

Sun dora alhakin haka kan Shugabannin majalisar kasa wadanda sune suka yarda,da irin yadda lamuraran ke tafiya a majalisar.

Shugabnnin jam’iyyun adawa (PDP) da kuma (LP) sun zargi jam’iyya (APC) wadda take samar da matsala a jam’iyyun domin ta maida Nijeriya mai bin tafarkin jam’iyya daya.

Wannan ya bullo ne bayan da aka samu komawa ita jam’iyyar APC daga jam’iyyun adawa,ba domin komai ba sai saboda irin rigingimun cikin gida wadanda suka faru.

Wasu kafofin yada labarai sun bada rahoton cewa akwai ‘yan adawa fiye da 300 suka bar jam’iyyar PDP da sauran wasu jam’iyyun adawa zuwa APC tun dga shekarar 2023.

Yayin da dukkan sauya shekar siyasa abin ya faru ne a majalisun gwamnatin tarayya dana Jihohi, rushewar jam’yyar PDP da dukkannin abubuwanta zuwa APC a Jihar Delta,karkashin jagorancin gwamna Sheriff Oborebwori,wannan shi ne babban barin wata jam’iyyar siyasa zuwa wata wanda ana iya cewar ita ce ficewa daga jam’iyya da ta fi tayar da hankali.

Gwamann Jihar Akwa Ibom Umo Eno shi ma ana ta rade- raden cewar nan bada jimawa ba zai koma APC ,yayin dai lamarin ya kara kamari domin da akwai wsu manyan jiga- jigan da ake sa ran za su koma jam’iyya mai mulki.

Sai dai kuma maganganun da Shugaban jam’iyyar APC, Dakta Abdullahi Ganduje’ sun jawo ma shi caccaka dangane da hakan.

Shi ma Shugaban kasa Bola Tinubu bada dadewa ba a wani taron jam’iyyar,yace tsarin jam’iyya daya bai da kyau ga mulkin farar hula;amma kuma ba hawan ba saukar a wani babin na shi yace ana maraba da dk wanda yake son dawowa jam’iyyar, saboda ai tsarin mulki ne ya bada damar ‘yancin yin hakan.

Halin da ake ciki yanzu Nijeriya tafiyar da mulkin farar hula mai jam’iyyun siyasa da aka yi wa rajista 18.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

Next Post

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

Related

Masana Sun Dora Alhakin Rashin Cika Alkawuran ‘Yan Siyasa Kan Jam’iyyu
Rahotonni

Masana Sun Dora Alhakin Rashin Cika Alkawuran ‘Yan Siyasa Kan Jam’iyyu

5 hours ago
Rashin Aikin Yi: A Halin Yanzu Masu Digiri Na Sayar Da Fiya Wata Da Aikin Achaba
Rahotonni

Rashin Aikin Yi: A Halin Yanzu Masu Digiri Na Sayar Da Fiya Wata Da Aikin Achaba

8 hours ago
2027: Abubuwan Da Jam’iyyun Siyasar Nijeriya Ke Tsammanin Samu Daga Sabon Shugaban INEC
Rahotonni

2027: Abubuwan Da Jam’iyyun Siyasar Nijeriya Ke Tsammanin Samu Daga Sabon Shugaban INEC

22 hours ago
Maulud 1,500: Yadda Zawiyar Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Ta Yi Maulidin Takutaha A Kaduna 
Rahotonni

Maulud 1,500: Yadda Zawiyar Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Ta Yi Maulidin Takutaha A Kaduna 

1 week ago
Ahlul Faidhati Mai Diwani Group
Rahotonni

Yadda Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Suka Yi Maulidin Cikar Annabi (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa 

2 weeks ago
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace
Rahotonni

Abin Fargaba Ne Yadda Bashin Nijeriya Ya Haura Tiriliyan 149 – Shugaban Majalisar Wakilai 

3 weeks ago
Next Post
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

LABARAI MASU NASABA

Matsalar Tasgadewar Kashin Baya

Matsalar Tasgadewar Kashin Baya

September 27, 2025
Firaministan Sin: Adalci Shi Ne Abu Mafi Daraja A Wurin Kasashen Duniya 

Firaministan Sin: Adalci Shi Ne Abu Mafi Daraja A Wurin Kasashen Duniya 

September 27, 2025
Yadda Ake Hada Sushi

Yadda Ake Hada Sushi

September 27, 2025
Ribar Da Manyan Kamfanonin Kasar Sin Ke Samu Ta Dawo Turbar Karuwa A Watanni 8 Na Farkon Bana

Ribar Da Manyan Kamfanonin Kasar Sin Ke Samu Ta Dawo Turbar Karuwa A Watanni 8 Na Farkon Bana

September 27, 2025
Atletico Madrid Ta Zazzaga Wa Real Madrid Ƙwallaye 5 A Metropolitano

Atletico Madrid Ta Zazzaga Wa Real Madrid Ƙwallaye 5 A Metropolitano

September 27, 2025
Tawagar Gwamnatin Tsakiya Na Ci Gaba Da Ziyartar Jami’ai Da Mazauna Yankuna Da Dama Na Jihar Xinjiang

Tawagar Gwamnatin Tsakiya Na Ci Gaba Da Ziyartar Jami’ai Da Mazauna Yankuna Da Dama Na Jihar Xinjiang

September 27, 2025
Wannan Bishiya Ta Bayyana Sirrin Ci Gaban Jihar Xinjiang

Wannan Bishiya Ta Bayyana Sirrin Ci Gaban Jihar Xinjiang

September 27, 2025
Hadin Tsumin Baure

Hadin Tsumin Baure

September 27, 2025
Masana Sun Dora Alhakin Rashin Cika Alkawuran ‘Yan Siyasa Kan Jam’iyyu

Masana Sun Dora Alhakin Rashin Cika Alkawuran ‘Yan Siyasa Kan Jam’iyyu

September 27, 2025
Ana Hasashen Tashin Fetur Idan Matatar Dangote Ta Daina Karɓar Naira

Ana Hasashen Tashin Fetur Idan Matatar Dangote Ta Daina Karɓar Naira

September 27, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.