Masana sun ce maimakon su rika maida hankalinsu kan yadda Nijeriya za ta koma kan tafarkinta kamar yadda aka dade da saninta, mai tarkin jam’iyya daya, an yi kira da su ‘yan siyasa su maida hankalinsu kan yadda za su yi maganin matsananciyar fatara wadda take damun ‘yan Nijeriya.
Hakanan ma an yi kira da su maida hankalinsu yadda za ayi maganin matsalolin tsaro da sauran matsalolin wadanda suke damun Nijeriya.
- Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu
- Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya
Wadannan shawarwarin sun fito ne daga manyan Lauyoyi na kasa da masana harkokin siyasa wadanda suka yi tunani kan damuwarsu ta yadda Nijeriya za ta kasance kasa mai amfani da tafarkin jam’iyyar siyasa daya, suka ce duk da abin ba wani aikata laifi bane sai dai halin da ake ciki yanzu yana da kamar wuya.
Sun ce yadda abubuwa suke tafiya da irin halin da su ‘yan siyasar suke zai sa lamarin tafarkin jam’iyya daya a matsayin abinda zai wahalar cimmawa,duk da yake dai tsarin mulki ya bada damar mu’amala da duk wata kungiya.
A wata ganawa ta musamman da Jaridar LEADERSHIP, ta ranar Lahadi,tayi dasu sun nuna damuwarsu akan irin kwamacalar siyasar da ake yi a Nijeriya,suka kara yin bayani cewa ai yanzu babu jajircewa da tsayawa kan lamarin da aka san mutum cikin jam’iyya,wanda ya kamata ace shi ne ake sa ran zai yi ma jam’iyya siyasa, Shugabannin majalisar yanzu abin babu ya dade da kwanta dama.
Sun dora alhakin haka kan Shugabannin majalisar kasa wadanda sune suka yarda,da irin yadda lamuraran ke tafiya a majalisar.
Shugabnnin jam’iyyun adawa (PDP) da kuma (LP) sun zargi jam’iyya (APC) wadda take samar da matsala a jam’iyyun domin ta maida Nijeriya mai bin tafarkin jam’iyya daya.
Wannan ya bullo ne bayan da aka samu komawa ita jam’iyyar APC daga jam’iyyun adawa,ba domin komai ba sai saboda irin rigingimun cikin gida wadanda suka faru.
Wasu kafofin yada labarai sun bada rahoton cewa akwai ‘yan adawa fiye da 300 suka bar jam’iyyar PDP da sauran wasu jam’iyyun adawa zuwa APC tun dga shekarar 2023.
Yayin da dukkan sauya shekar siyasa abin ya faru ne a majalisun gwamnatin tarayya dana Jihohi, rushewar jam’yyar PDP da dukkannin abubuwanta zuwa APC a Jihar Delta,karkashin jagorancin gwamna Sheriff Oborebwori,wannan shi ne babban barin wata jam’iyyar siyasa zuwa wata wanda ana iya cewar ita ce ficewa daga jam’iyya da ta fi tayar da hankali.
Gwamann Jihar Akwa Ibom Umo Eno shi ma ana ta rade- raden cewar nan bada jimawa ba zai koma APC ,yayin dai lamarin ya kara kamari domin da akwai wsu manyan jiga- jigan da ake sa ran za su koma jam’iyya mai mulki.
Sai dai kuma maganganun da Shugaban jam’iyyar APC, Dakta Abdullahi Ganduje’ sun jawo ma shi caccaka dangane da hakan.
Shi ma Shugaban kasa Bola Tinubu bada dadewa ba a wani taron jam’iyyar,yace tsarin jam’iyya daya bai da kyau ga mulkin farar hula;amma kuma ba hawan ba saukar a wani babin na shi yace ana maraba da dk wanda yake son dawowa jam’iyyar, saboda ai tsarin mulki ne ya bada damar ‘yancin yin hakan.
Halin da ake ciki yanzu Nijeriya tafiyar da mulkin farar hula mai jam’iyyun siyasa da aka yi wa rajista 18.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp