ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, November 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

by Rabi'u Ali Indabawa and Sulaiman
5 months ago
vector illustration of Nigeria flag and map

vector illustration of Nigeria flag and map

Masana sun ce maimakon su rika maida hankalinsu kan yadda Nijeriya za ta koma kan tafarkinta kamar yadda aka dade da saninta, mai tarkin jam’iyya daya, an yi kira da su ‘yan siyasa su maida hankalinsu kan yadda za su yi maganin matsananciyar fatara wadda take damun ‘yan Nijeriya.

Hakanan ma an yi kira da su maida hankalinsu yadda za ayi maganin matsalolin tsaro da sauran matsalolin wadanda suke damun Nijeriya.

  • Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu
  • Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Wadannan shawarwarin sun fito ne daga manyan Lauyoyi na kasa da masana harkokin siyasa wadanda suka yi tunani kan damuwarsu ta yadda Nijeriya za ta kasance kasa mai amfani da tafarkin jam’iyyar siyasa daya, suka ce duk da abin ba wani aikata laifi bane sai dai halin da ake ciki yanzu yana da kamar wuya.

ADVERTISEMENT

Sun ce yadda abubuwa suke tafiya da irin halin da su ‘yan siyasar suke zai sa lamarin tafarkin jam’iyya daya a matsayin abinda zai wahalar cimmawa,duk da yake dai tsarin mulki ya bada damar mu’amala da duk wata kungiya.

A wata ganawa ta musamman da Jaridar LEADERSHIP, ta ranar Lahadi,tayi dasu sun nuna damuwarsu akan irin kwamacalar siyasar da ake yi a Nijeriya,suka kara yin bayani cewa ai yanzu babu jajircewa da tsayawa kan lamarin da aka san mutum cikin jam’iyya,wanda ya kamata ace shi ne ake sa ran zai yi ma jam’iyya siyasa, Shugabannin majalisar yanzu abin babu ya dade da kwanta dama.

LABARAI MASU NASABA

Rundunar Sojin Nijeriya Ta Bayyana Dalilan Hana Jami’anta Auren ‘Yan Kasashen Waje

Zargin Kisan Kiristoci: Dalilan Da Ya Sa Trump Ba Zai Iya Kai Wa Nijeriya Hari Ba

Sun dora alhakin haka kan Shugabannin majalisar kasa wadanda sune suka yarda,da irin yadda lamuraran ke tafiya a majalisar.

Shugabnnin jam’iyyun adawa (PDP) da kuma (LP) sun zargi jam’iyya (APC) wadda take samar da matsala a jam’iyyun domin ta maida Nijeriya mai bin tafarkin jam’iyya daya.

Wannan ya bullo ne bayan da aka samu komawa ita jam’iyyar APC daga jam’iyyun adawa,ba domin komai ba sai saboda irin rigingimun cikin gida wadanda suka faru.

Wasu kafofin yada labarai sun bada rahoton cewa akwai ‘yan adawa fiye da 300 suka bar jam’iyyar PDP da sauran wasu jam’iyyun adawa zuwa APC tun dga shekarar 2023.

Yayin da dukkan sauya shekar siyasa abin ya faru ne a majalisun gwamnatin tarayya dana Jihohi, rushewar jam’yyar PDP da dukkannin abubuwanta zuwa APC a Jihar Delta,karkashin jagorancin gwamna Sheriff Oborebwori,wannan shi ne babban barin wata jam’iyyar siyasa zuwa wata wanda ana iya cewar ita ce ficewa daga jam’iyya da ta fi tayar da hankali.

Gwamann Jihar Akwa Ibom Umo Eno shi ma ana ta rade- raden cewar nan bada jimawa ba zai koma APC ,yayin dai lamarin ya kara kamari domin da akwai wsu manyan jiga- jigan da ake sa ran za su koma jam’iyya mai mulki.

Sai dai kuma maganganun da Shugaban jam’iyyar APC, Dakta Abdullahi Ganduje’ sun jawo ma shi caccaka dangane da hakan.

Shi ma Shugaban kasa Bola Tinubu bada dadewa ba a wani taron jam’iyyar,yace tsarin jam’iyya daya bai da kyau ga mulkin farar hula;amma kuma ba hawan ba saukar a wani babin na shi yace ana maraba da dk wanda yake son dawowa jam’iyyar, saboda ai tsarin mulki ne ya bada damar ‘yancin yin hakan.

Halin da ake ciki yanzu Nijeriya tafiyar da mulkin farar hula mai jam’iyyun siyasa da aka yi wa rajista 18.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Rundunar Sojin Nijeriya Ta Bayyana Dalilan Hana Jami’anta Auren ‘Yan Kasashen Waje
Rahotonni

Rundunar Sojin Nijeriya Ta Bayyana Dalilan Hana Jami’anta Auren ‘Yan Kasashen Waje

November 15, 2025
Zargin Kisan Kiristoci: Dalilan Da Ya Sa Trump Ba Zai Iya Kai Wa Nijeriya Hari Ba
Manyan Labarai

Zargin Kisan Kiristoci: Dalilan Da Ya Sa Trump Ba Zai Iya Kai Wa Nijeriya Hari Ba

November 12, 2025
Majalisa Na Binciken Kwangilar Titin Naira Biliyan 1.46 Da Aka Yi Watsi Da Shi A Kaduna
Rahotonni

Matsalar Tsaro: Yadda Dabarun Uba Sani Suka Mayar Da Tsoro Zuwa Kyakkyawar Fata A Jihar Kaduna

November 8, 2025
Next Post
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

LABARAI MASU NASABA

Kakakin Majalisar Taraba Da Ƴan Majalisa 15 Sun Fice Daga PDP Zuwa APC

Kakakin Majalisar Taraba Da Ƴan Majalisa 15 Sun Fice Daga PDP Zuwa APC

November 17, 2025
Hakimi, Osimhen Da Salah Ƴan Wasan Da Ke Takara A Ƙyautar Gwarzon Afrika

Hakimi, Osimhen Da Salah Ƴan Wasan Da Ke Takara A Ƙyautar Gwarzon Afrika

November 17, 2025
Tsohuwar Firaministan Bangaladesh Sheikha Hasina,

An Yanke Wa Tsohuwar Shugabar Bangladesh Hukuncin Kisa

November 17, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Ɗalibai Ƴan Mata, Sun Kashe Mataimakin Shugaban Makaranta A Kebbi

Ƴan Bindiga Sun Sace Ɗalibai Ƴan Mata, Sun Kashe Mataimakin Shugaban Makaranta A Kebbi

November 17, 2025
Mutane 42 Sun Mutu A Wani Hatsarin Tankar Dizal Da Motar Masu Umrah A Hanyar Makka

Mutane 42 Sun Mutu A Wani Hatsarin Tankar Dizal Da Motar Masu Umrah A Hanyar Makka

November 17, 2025
Ba Mu Samu Labarin Kai Wa Laftanar Yerima Hari Ba – Ƴansanda

Ba Mu Samu Labarin Kai Wa Laftanar Yerima Hari Ba – Ƴansanda

November 17, 2025
Sarki Sanusi Ya Shawarci Unguwannin Da Suka Fuskanci Matsalar Tsaro Su Sa Idon

Sarki Sanusi Ya Shawarci Unguwannin Da Suka Fuskanci Matsalar Tsaro Su Sa Idon

November 17, 2025
Laftanal Yarima Ya Tsallake Rijiya Da Baya A Abuja

Laftanal Yarima Ya Tsallake Rijiya Da Baya A Abuja

November 16, 2025
Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su

Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su

November 16, 2025
Fasinjojin Da Kasar Sin Ta Yi Jigilarsu Ta Jirgin Kasa Daga Janairu Zuwa Oktoba Sun Kai Biliyan 3.95

Fasinjojin Da Kasar Sin Ta Yi Jigilarsu Ta Jirgin Kasa Daga Janairu Zuwa Oktoba Sun Kai Biliyan 3.95

November 16, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.