• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2027: Fafutukar Jan Akalar Jam’iyyar PDP Ta Koma Jihohi

by Yusuf Shuaibu
11 months ago
in Labarai
0
2027: Fafutukar Jan Akalar Jam’iyyar PDP Ta Koma Jihohi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Alamu dai na nuni da cewa fafutukar neman jan akalar jam’iyyar PDP gabanin zaben 2027, ya rikiɗe ya koma zuwa jihohi, a daidai lokacin da jam’iyyar ke shirin gudanar da zabukan shugabannin jam’iyyar a jihohi 20.

Rahotonni sun bayyana cewa za a gudanar da zaben shugabannin jam’iyyar ne a jihohi da suka hada da Akwa Ibom, Bayelsa, Kurus Ribas, Delta, Ribas, Kano, Katsina, Benuwai, Kaduna da Filato, a ranar 31 ga watan Agusta.

  • Ranar Dimokuraɗiyyar:  Ƴan Nijeriya Fushi Suke, PDP Ga Tinubu 
  • Rikicin PDP: Daraktan Yakin Neman Zaben Atiku Ya Caccaki Wike

Sauran jihohin da ake sa ran gudanar da zaben shugabannin sun hada da Taraba, Bauchi, Gombe, Inugu, Imo, Abiya, Ogun, Ondo, Ekiti, Edo, Anambra da Babban Birnin Tarayya Abuja.

Wata takarda da aka samu a sakatariyar jam’iyyar PDP ta kasa a karshen mako, ta nuna cewa za a yi taron gundumomi da na kananan hukumomi a jihohin da abin ya shafa a ranakun 27 ga watan Yuli da 10 ga watan Agusta. A ranar 26 ga watan Satumba ne ake sa ran kwamitin zartarwa na PDP zai yi taro domin amincewa da dukkan zababbun shugabannin zartaswa da kuma cimma matsaya kan batun babban taron jam’iyyar na kasa wanda zai bayar da damar a zabi shugaban jam’iyyar na kasa.

Majiyarmu ta bayyana cewa a daidai lokacin da za a gudanar da zabukan sabbin shugabannin jam’iyyar a matakin jiha, manyan ‘yan jam’iyyar adawa sun karkata akalarsu zuwa jihohin.

Labarai Masu Nasaba

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

Babbar jam’iyyar adawa ta PDP na fama da rikice-rikice a jihohi 12 da suka hada da Kano, Katsina, Ribas, Edo, Ebonyi, Ogun, Filato, Neja da Kuros Ribas, da kuma yankin kudu maso gabas. Shugabannin jam’iyyar PDP a jihohin da abin ya shafa sun shiga fafatawa don ganin sun mallaki akalar jam’iyyar gabanin zaben 2027.

Tun bayan zaben 2023, magoya bayan tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar da kuma ministan Babban Birnin Tarayya Abuja, Nyesom Wike, sun shiga takun saka a kan jan akalar jam’iyyar PDP gabanin zaben 2027.

Kafin taron karshe na kwamitin zartarwa na kasa da jam’iyyar ta gudanar a ranar 18 ga watan Afrilu, bangarorin biyu sun fafata kan ko wane ne daga cikinsu zai samar da sahihin shugaban jam’iyyar na kasa.  Sai dai kwamitin zartaswa na jam’iyyar ya dage zaben sabon shugaban jam’iyyar na kasa har zuwa taronta na gaba wanda aka shirya za a yi a ranar 26 ga Satumban 2024.

A kwanakin baya ne dai wasu daga cikin kwamitocin rikon kwarya sun umurci daukacin ‘ya’yan jam’iyyar a jihohinsu da su sake tantance mambobinsu a gaban taron, a matsayin wani bangare na kara karfi gabanin zaben jam’iyyar a matakin jiha. Sai dai a wata sanarwa da sakataren yada labarai na jam’iyyar na kasa, Debo Ologunagba ya fitar, ya ce kwamitin gudanarwa na jam’iiyar ya yi watsi da kwamitocin, inda ya ce babu wani tsohon mamba da ake sa ran za a sake tantance shi.

Wata majiya mai karfi a sakatariyar PDP ta shaida cewa, sake tabbatar da mambobin jam’iyyar wata dabara ce da wasu daga cikin ‘yan jam’iyyar suka yi don ganin sun fatattaki abokan hamayyarsu a fafatawar da suke yi na jan akalar jam’iyyar. “Kuna sane cewa kwanan nan kwamitin gudanarwa na kasa ya ce tsofaffin membobin ba dole ba ne a sake tantancesu. Wadanda za su kada kuri’a ‘yan jam’iyya ne masu rajista. Abin da wadancan mutanen suke yi, suna cewa kowa ya je ya gyara. Don haka, za su dauki katunan da fom, ba za su ba wa wasu mutane ba. Yana daga cikin fafutuka na kula da tsarin jam’iyya.

“Jam’iyyar ta fitar da sanarwar cewa sabunta rajista ba na tsofaffin mambobin ba ne. Yanzu duk ‘yan jam’iyyar ne za su kada kuri’a. Abin da suke so su yi shi ne a hana wasu mutane rike katunan jam’iyyar. A cikin wadancan jihohin da ake fama da rikici, wasu bangarori sun yi kokarin kawar da abokan hamayyarsu. Amma nan da nan aka fitar da wannan sanarwa, an shawo kan lamarin baki daya.”

Wani shugaban jam’iyyar daga kudu maso gabas shi ma ya shaida cewa, “Ka san muna da bangarori da suka hada da na Atiku da na Wike. Har yanzu akwai wani bangare na uku wanda ya kunshi mutanen da ba su yarda da Wike da Atiku ba.  Wasu ‘ya’yan jam’iyyar PDP na yin gangami ne domin mayar da jam’iyyar kan hayyacinta. Kamar yadda kuka sani, wadanda aka zaba ne za su yanke shawarar yadda jam’iyyar za ta kasance a gaba.  Wadada aka zabe ne za su nuna wadanda ke rike da mukamai.”

A daidai lokacin da ake tunkarar zaben shugabannin jam’iyyar a matakin jiha, tashin hankali na ci gaba da faruwa a jihohi 12, yayin da jiga-jigan jam’iyyar ke fafutukar ganin sun mallaki akalar jam’iyyar.

Alal misali, shugabannin jam’iyyar adawa a Ebonyi sun ja kunnen ‘ya’yan jam’iyyar PDP wajen kokarin neman shugabanci.

“Ana wannan fafutuka ne domin tsayawa takara a zaben 2027 a jihar. Wasu jiga-jigan da ba su da nasaba da jama’a suna dagewa ne domin su mallaki jam’iyyar gabanin zaben gwamna mai zuwa,” wani dan jam’iyyar a jihar ya shaida haka.

Har ila yau, a Jihar Edo, mambobin kungiyar ‘Legacy Group’ karkashin jagorancin Cif Dan Orbih sun yi artabu da Gwamna Godwin Obaseki kan yadda ake jan akalar jam’iyyar. Wani jigo a jam’iyyar ya shaida cewa ‘ya’yan kungiyar ba su taka kara sun karya ba sakamakon dakatar da Orbih a matsayin mataimakin shugaban jam’iyyar na kasa da kwamitin gudanarwa ya yi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kasar Sin Za Ta Kaddamar Da Biranen Gwajin Amfani Da Tsarin Taswira Na Tauraron Dan Adam Na BeiDou

Next Post

Kwamitin Kolin JKS Ya Gudanar Da Taron Manema Labarai Dangane Da Taronsa Na Uku

Related

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya
Manyan Labarai

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

55 seconds ago
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC
Labarai

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

3 hours ago
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi
Labarai

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

4 hours ago
Daurarru
Labarai

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

13 hours ago
Wutar lantarki
Labarai

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

15 hours ago
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka
Labarai

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

16 hours ago
Next Post
Kwamitin Kolin JKS Ya Gudanar Da Taron Manema Labarai Dangane Da Taronsa Na Uku

Kwamitin Kolin JKS Ya Gudanar Da Taron Manema Labarai Dangane Da Taronsa Na Uku

LABARAI MASU NASABA

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

June 7, 2025
Neja

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

June 7, 2025
Adawa

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

June 7, 2025
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

June 7, 2025
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

June 7, 2025
Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

June 6, 2025
Wutar lantarki

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.