• English
  • Business News
Friday, June 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2027: Ganawar Manyan Jam’iyyun Adawa Ta Kara Wa Yunkurin Maja Kaimi

by Yusuf Shuaibu
1 year ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
2027: Ganawar Manyan Jam’iyyun Adawa Ta Kara Wa Yunkurin Maja Kaimi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ziyarar da dan takarar shugaban kasa a zaben 2023 karkashin jam’iyyar LP, Peter Obi ya kai wa manyan kusoshin ‘yan siyasa na kasa ciki har da dan takarar shugaban kasa na PDP a zaben 2023, Atiku Abubakar ta haifar da zazzafar muhawara tare da bude babin yunkurin da ‘yan adawa ke yi na kwace mulki a hannun APC a zaben 2027.

Atiku ya wallafa hotunan ganawar a shafinsa na Tuwita tare da bayyana cewa abun alfahari ne a gare shi a yau da ya karbi bakoncin Peter Obi.

  • Zanga-zangar Karin Kudin Wuta: Gwamnati Ta Shelanta Matakin Da Za Ta Dauka
  • Ziyarar Xi Jinping A Turai Ta Fitar Da Muryar Kiyaye Zaman Lafiya Da Yin Hadin Gwiwa

Daya daga cikin mataimakan Atiku wanda ya bukaci a sakaya sunansa ya bayyana cewa ganawar ta kasance ta sirri ce, amma har yau Atiku yana nan kan bakansa na ganin jam’iyyun adawa sun yi maja domin kwace mulki a hannun APC.

Haka shi ma mai magana da yawun dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar LP, Yunusa Tanko ya ce, tabbas wannan ganawa ce ta sirri kuma babu wani abu idan mutum ya ziyarci tsohon abokinsa.

 Ya kara da cewa a duk lokacin da irin wadannan mutane suka tattauna batutuwa daban-daban, to abin da ake fata a karshen tattaunawar ya zama ya amfani ‘yan Nijeriya baki daya.

Labarai Masu Nasaba

‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba

Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?

Kafin ya ziyarci Atiku, Obi ya yi ganawar sirri da tsohon gwamnan Jihar Jigawa, Sule Lamido a gidansa da ke Abuja. Mataimaki na musamman ga Lamido, Mansur Ahmed ya tabbatar da wannan ziyarar, inda ya ce shugabannin guda biyu sun gudanr da wata ganawa ta sirri.

Sannan kuma, a wata sanarwa da Tanko ya fitar ya ce Peter Obi ya kuma ziyarci tsohon shugaban majalisar dattawa, Bukola Saraki.

“A dukkanin wadannan ziyarce-ziyarce an tattauna batutuwan da suka shafi kasa ta yadda za a rage wa ‘yan Nijeriya wahalhalun da suke ciki ba tare da la’akari da matsayinsu ko kuma wurin da suke zaune ba. Musamman ma an yi tsokaci kan matsin rayuwa da al’ummar Nijeriya ke ciki.

“Wani abu mai muhimmanci da aka tattauna a wadannan ziyarce-ziyarce shi ne, halin da ake ciki a yankin arewacin Nijeriya,” in ji sanarwar.

Peter Obi ya kasance mataimakin dan takarar shugaban kasa na Atiku a zaben 2019, inda ya raba gari da tsohon mataimakin shugaban kasan daga bisani, wanda ya zama dan takarar shugaban kasa a zaben 2023, sakamakon kiraye-kirayen da ake yi masa ya bar PDP ya koma wata jam’iyya domin ya samu damar tsayawa takara.

Yayin da Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu ya zama wanda ya yi nasara a zaben 2023 da kuri’u 8,794,726, masana harkokin siyasa sun yi hasashen cewa Atiku da Obi za su sake neman tikitin takara da su bai wa jam’iyya mai mulki ciwon kai.

Atiku ya samu kuri’u 6,984,520, yayin da Obi ya samu kuri’a 6,101,533. Dukkaninsu biyun sun samu kuri’u 11,262,978 a zaben 2019, yayin da tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari ya samu kuri’u 15,191,847.

Ziyarar da Obi ya kai wa Atiku a ranar Litinin, ta zo ce kwana guda bayan da mai magana da yawun Atiku, Paul Ibe, a wata tattaunawa ya nanata cewa, Atiku bai tilasta wa Obi barin PDP ba, amma ya zargi ministan Abuja, Nyeson Wike da zama dalilin barin Obi jam’iyyar PDP.

“Atiku Abubakar bai tilasta wa Obi ficewa daga PDP ba. Atiku yana matukar kulawa da dangantakar da ke tsakaninsa da Obi,” in ji Ibe.

Idan za a iya tunawa dai, tun bayan kamala zaben 2023, Atiku yana kan gaba wajen bukatar jam’iyyun adawa su kafa kawancen kwace mulki a hannun jam’iyyar APC a zaben 2027.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AdawaJam'iyyaPDP
ShareTweetSendShare
Previous Post

Yadda Ƙungiyar Matasan Arewa Kan Harkokin Tsaro Ta Shirya Tattaunawa Kan Batun ‘Yansandan Jihohi

Next Post

Wutar Lantarki Ta Yi Ajalin Wani Mutum A Bayelsa

Related

‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba

6 days ago
Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?
Tambarin Dimokuradiyya

Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?

2 weeks ago
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Adawa Na Cacakar APC A Yankin Arewa Maso Yamma Bisa Goyon Bayan Tazarcen Tinubu

2 weeks ago
Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027
Tambarin Dimokuradiyya

Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027

1 month ago
Adawa
Tambarin Dimokuradiyya

Amfani Da Karfin Gwamnati Kan ‘Yan Adawa Zai Jawo Wa Tinubu Illa A 2027 – Sule Lamido

1 month ago
‘Yan Siyasa Na Gwagwarmaya Ne Kadai Wajen Neman Mukami Ba Wai Don Talakawa Ba — Bafarawa
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Siyasa Na Gwagwarmaya Ne Kadai Wajen Neman Mukami Ba Wai Don Talakawa Ba — Bafarawa

1 month ago
Next Post
Wutar Lantarki Ta Yi Ajalin Wani Mutum A Bayelsa

Wutar Lantarki Ta Yi Ajalin Wani Mutum A Bayelsa

LABARAI MASU NASABA

Xi Da Trump Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

Xi Da Trump Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

June 5, 2025
Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Yi Watsi Da Amfani Da Batun Tsaron Kasa Barkatai

Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Yi Watsi Da Amfani Da Batun Tsaron Kasa Barkatai

June 5, 2025
Wani Matashi Dan Shekara 33 Ya Rasu Bayan Ya Fada Wata Tsohuwar Rijiya A Kano

Wani Matashi Dan Shekara 33 Ya Rasu Bayan Ya Fada Wata Tsohuwar Rijiya A Kano

June 5, 2025
Ma’aikatar Harkokin Waje: Kasar Sin Ta Kasance Gwarzuwa Wajen Samar Da Ci Gaba Ba Tare Da Gurbata Muhalli Ba

Ma’aikatar Harkokin Waje: Kasar Sin Ta Kasance Gwarzuwa Wajen Samar Da Ci Gaba Ba Tare Da Gurbata Muhalli Ba

June 5, 2025
‘Yansanda Sun Hallaka Ɗan Fashi Da Makami Tare Da Jikkata Wasu Da Dama A Bauchi 

‘Yansanda Sun Hallaka Ɗan Fashi Da Makami Tare Da Jikkata Wasu Da Dama A Bauchi 

June 5, 2025
Lambar “-1.5” Gargadi Ce Da Al’ummar Duniya Ke Yi Ga Azzaluma 

Lambar “-1.5” Gargadi Ce Da Al’ummar Duniya Ke Yi Ga Azzaluma 

June 5, 2025
Sabbin Matakan Amurka Game Da Masu Shiga Kasar Sun Ci Karo Da Ikirarinta Na Mutunta Hakkokin Bil Adama

Sabbin Matakan Amurka Game Da Masu Shiga Kasar Sun Ci Karo Da Ikirarinta Na Mutunta Hakkokin Bil Adama

June 5, 2025
Bukola Saraki Ya Tallafawa Al’ummar Mokwa Da Gudunmawar Kuɗi

Bukola Saraki Ya Tallafawa Al’ummar Mokwa Da Gudunmawar Kuɗi

June 5, 2025
Diaz Ba Na Sayarwa Bane – Liverpool Ta Fadawa Barcelona

Diaz Ba Na Sayarwa Bane – Liverpool Ta Fadawa Barcelona

June 5, 2025
Wani Injin Jirgi Mai Saukar Ungulu Kirar Kasar Sin Ya Samu Shaidar Amincewa 

Wani Injin Jirgi Mai Saukar Ungulu Kirar Kasar Sin Ya Samu Shaidar Amincewa 

June 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.