ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 6, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2027: Ganawar Manyan Jam’iyyun Adawa Ta Kara Wa Yunkurin Maja Kaimi

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
Adawa

Ziyarar da dan takarar shugaban kasa a zaben 2023 karkashin jam’iyyar LP, Peter Obi ya kai wa manyan kusoshin ‘yan siyasa na kasa ciki har da dan takarar shugaban kasa na PDP a zaben 2023, Atiku Abubakar ta haifar da zazzafar muhawara tare da bude babin yunkurin da ‘yan adawa ke yi na kwace mulki a hannun APC a zaben 2027.

Atiku ya wallafa hotunan ganawar a shafinsa na Tuwita tare da bayyana cewa abun alfahari ne a gare shi a yau da ya karbi bakoncin Peter Obi.

  • Zanga-zangar Karin Kudin Wuta: Gwamnati Ta Shelanta Matakin Da Za Ta Dauka
  • Ziyarar Xi Jinping A Turai Ta Fitar Da Muryar Kiyaye Zaman Lafiya Da Yin Hadin Gwiwa

Daya daga cikin mataimakan Atiku wanda ya bukaci a sakaya sunansa ya bayyana cewa ganawar ta kasance ta sirri ce, amma har yau Atiku yana nan kan bakansa na ganin jam’iyyun adawa sun yi maja domin kwace mulki a hannun APC.

ADVERTISEMENT

Haka shi ma mai magana da yawun dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar LP, Yunusa Tanko ya ce, tabbas wannan ganawa ce ta sirri kuma babu wani abu idan mutum ya ziyarci tsohon abokinsa.

 Ya kara da cewa a duk lokacin da irin wadannan mutane suka tattauna batutuwa daban-daban, to abin da ake fata a karshen tattaunawar ya zama ya amfani ‘yan Nijeriya baki daya.

LABARAI MASU NASABA

Zaben Fitar Da Gwani Na APC: Tinubu Zai Shiga Tsakani Wajen Warware Rikicin Jam’iyyar

2027:Gwamnoni Na Fuskantar Turjiya Wajen Gwagwarmayar Kare Kujerunsu Da Kuma Samar Da Magadansu

Kafin ya ziyarci Atiku, Obi ya yi ganawar sirri da tsohon gwamnan Jihar Jigawa, Sule Lamido a gidansa da ke Abuja. Mataimaki na musamman ga Lamido, Mansur Ahmed ya tabbatar da wannan ziyarar, inda ya ce shugabannin guda biyu sun gudanr da wata ganawa ta sirri.

Sannan kuma, a wata sanarwa da Tanko ya fitar ya ce Peter Obi ya kuma ziyarci tsohon shugaban majalisar dattawa, Bukola Saraki.

“A dukkanin wadannan ziyarce-ziyarce an tattauna batutuwan da suka shafi kasa ta yadda za a rage wa ‘yan Nijeriya wahalhalun da suke ciki ba tare da la’akari da matsayinsu ko kuma wurin da suke zaune ba. Musamman ma an yi tsokaci kan matsin rayuwa da al’ummar Nijeriya ke ciki.

“Wani abu mai muhimmanci da aka tattauna a wadannan ziyarce-ziyarce shi ne, halin da ake ciki a yankin arewacin Nijeriya,” in ji sanarwar.

Peter Obi ya kasance mataimakin dan takarar shugaban kasa na Atiku a zaben 2019, inda ya raba gari da tsohon mataimakin shugaban kasan daga bisani, wanda ya zama dan takarar shugaban kasa a zaben 2023, sakamakon kiraye-kirayen da ake yi masa ya bar PDP ya koma wata jam’iyya domin ya samu damar tsayawa takara.

Yayin da Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu ya zama wanda ya yi nasara a zaben 2023 da kuri’u 8,794,726, masana harkokin siyasa sun yi hasashen cewa Atiku da Obi za su sake neman tikitin takara da su bai wa jam’iyya mai mulki ciwon kai.

Atiku ya samu kuri’u 6,984,520, yayin da Obi ya samu kuri’a 6,101,533. Dukkaninsu biyun sun samu kuri’u 11,262,978 a zaben 2019, yayin da tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari ya samu kuri’u 15,191,847.

Ziyarar da Obi ya kai wa Atiku a ranar Litinin, ta zo ce kwana guda bayan da mai magana da yawun Atiku, Paul Ibe, a wata tattaunawa ya nanata cewa, Atiku bai tilasta wa Obi barin PDP ba, amma ya zargi ministan Abuja, Nyeson Wike da zama dalilin barin Obi jam’iyyar PDP.

“Atiku Abubakar bai tilasta wa Obi ficewa daga PDP ba. Atiku yana matukar kulawa da dangantakar da ke tsakaninsa da Obi,” in ji Ibe.

Idan za a iya tunawa dai, tun bayan kamala zaben 2023, Atiku yana kan gaba wajen bukatar jam’iyyun adawa su kafa kawancen kwace mulki a hannun jam’iyyar APC a zaben 2027.

Adawa
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Matsalar Tsaro Da Tsadar Kayan Noma Na Barazana Ga Samar Da Abinci A Daminar Bana
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Zaben Fitar Da Gwani Na APC: Tinubu Zai Shiga Tsakani Wajen Warware Rikicin Jam’iyyar
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027:Gwamnoni Na Fuskantar Turjiya Wajen Gwagwarmayar Kare Kujerunsu Da Kuma Samar Da Magadansu
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Masana Tattalin Arziki Sun Yi Watsi Da Rahoton NBS Kan Tattalin Arziki

MASU ALAKA

Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP
Tambarin Dimokuradiyya

Zaben Fitar Da Gwani Na APC: Tinubu Zai Shiga Tsakani Wajen Warware Rikicin Jam’iyyar

June 5, 2026
2027:Gwamnoni Na Fuskantar Turjiya Wajen Gwagwarmayar Kare Kujerunsu Da Kuma Samar Da Magadansu
Tambarin Dimokuradiyya

2027:Gwamnoni Na Fuskantar Turjiya Wajen Gwagwarmayar Kare Kujerunsu Da Kuma Samar Da Magadansu

June 5, 2026
Adawa
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Rashin Hadin Kan Atiku Da Obi Da Kwankwaso Na Iya Taimaka Wa Tazarcen Tinubu

May 16, 2026
Next Post
Wutar Lantarki Ta Yi Ajalin Wani Mutum A Bayelsa

Wutar Lantarki Ta Yi Ajalin Wani Mutum A Bayelsa

LABARAI MASU NASABA

Kofin Duniya: Sababbin Dokokin Da FIFA Ta Kawo

Kofin Duniya: Sababbin Dokokin Da FIFA Ta Kawo

June 6, 2026
Kafar CMG Ta Kulla Yerjeniyoyin Hadin Gwiwa Da Hukumomin Kasar Laos

Kafar CMG Ta Kulla Yerjeniyoyin Hadin Gwiwa Da Hukumomin Kasar Laos

June 6, 2026
Rundunar Sojan Kasar Sin Ta Sa Ido Kan Jirgin Ruwan Yakin Kasar Holland Da Ya Tsallake Mashigin Tekun Taiwan

Rundunar Sojan Kasar Sin Ta Sa Ido Kan Jirgin Ruwan Yakin Kasar Holland Da Ya Tsallake Mashigin Tekun Taiwan

June 6, 2026
Sin Tana Adawa Da Karin Takunkumin Da Amurka Ta Sanya Wa Cuba

Sin Tana Adawa Da Karin Takunkumin Da Amurka Ta Sanya Wa Cuba

June 6, 2026
Matsalar Tsaro Da Tsadar Kayan Noma Na Barazana Ga Samar Da Abinci A Daminar Bana

Matsalar Tsaro Da Tsadar Kayan Noma Na Barazana Ga Samar Da Abinci A Daminar Bana

June 6, 2026
Ban Sha Wata Wahala Ba A Gwagwarmayar Shiga Harkar Fim —Hadiza

Ban Sha Wata Wahala Ba A Gwagwarmayar Shiga Harkar Fim —Hadiza

June 6, 2026
Alfanu Da Rashin Alfanun Tallata Hotunan Ango Da Amarya Kafin Daura Aure

Alfanu Da Rashin Alfanun Tallata Hotunan Ango Da Amarya Kafin Daura Aure

June 6, 2026
Darajar Naira Ta Sauka A Kasuwar Musayar Kuɗaɗe

Darajar Naira Ta Sauka A Kasuwar Musayar Kuɗaɗe

June 6, 2026
Yadda Ake Miyar Margi Da Kifin Tarwad

Yadda Ake Miyar Margi Da Kifin Tarwad

June 6, 2026
Sanata Wamakko Ya Koka Kan Taɓarɓarewar Sha’anin Tsaro

Sanata Wamakko Ya Koka Kan Taɓarɓarewar Sha’anin Tsaro

June 6, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.