ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 6, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wutar Lantarki Ta Yi Ajalin Wani Mutum A Bayelsa

by Sadiq
2 years ago
Wutar Lantarki

Wani mutum mai suna Amas ya rasa ransa sakamakon makalewa da ya yi a jikin wayar wutar lantarki a unguwar Ekeki, kusa da hedikwatar ‘yansanda da ke kan titin Azikoro a Yenagoa, babban birnin Jihar Bayelsa.

Marigayin dai ba ma’aikacin Kamfanin Power Holding Company of Nigeria (PHCN) ba ne, amma yana zaune ne a unguwar kuma yana hada wa mutane wuta.

  • 2027: Ganawar Manyan Jam’iyyun Adawa Ta Kara Wa Yunkurin Maja Kaimi
  • CAC Da Masu POS Sun Amince Da Wa’adin Mako Biyu Don Rijista

Mazauna yankin sun shaida wa manema labarai cewa, sakamakon rashin wutar lantarki da ake fama da shi a jihar, akasarin mutane sun gwammace hada wutar lantarki a kan layin gwamnatin tarayya wanda ake samun wutar lantarkin akalla sa’o’i 12 zuwa 13 a kullum.

ADVERTISEMENT

Marigayin dan asalin karamar hukumar Nembe a jihar ya rasu ya bar ‘ya’ya biyu, ya makale ne a kan wayar wutar lantarkin kafin jami’an kamfanin PHCN su sauko da shi.

Wani mazaunin Azikoro mai suna Micheal Orubo wanda lamarin ya faru a kan idonsa, ya bayyana marigayin a matsayin mutum mai saukin kai wanda yake aikin hada wutar lantarki domin kula da iyalinsa.

LABARAI MASU NASABA

Matsalar Tsaro Da Tsadar Kayan Noma Na Barazana Ga Samar Da Abinci A Daminar Bana

Ban Sha Wata Wahala Ba A Gwagwarmayar Shiga Harkar Fim —Hadiza

Ya ce, “Amas yana zaune a unguwarmu, kuma yana aikin hada wuta ne a yanki. Me ya sa mutuwa za ta zo masa a haka? Ya tafi ya bar mu ba zai sake dawowa ba.

“Yana da saukin kai, wa zai kula da yaran da ya bari. Kudin da yake samu a aikin hada wutar lantarki da shi yake amfani wajen ciyar da iyalinsa. Wace irin mutuwa ce wannan? Mutumin da muke tare tsawon lokacin da ake ruwan sama yanzu, ya tafi ne da nufin idan ruwa ya dauke ya gyara musu wuta.”

Wani mazaunin yankin ya ce, “Ya wuce ni bai wuce minti biyar ba. Ruwan sama yana tsayawa, sai ihun mutane muka jiyo, nan take muka garzaya wajen da lamarin ya faru amma ba za mu iya taimakonsa ba, saboda ya daure jikinsa da bel, don haka ya makale sosai a jikin falwaya, saboda duk mun tsorata kuma har yanzu ana ruwan sama.”

Ma’aikatan kamfanin wuta na PHCN, daga baya sun zo sauke gawar daga jikin falwayar da ya makale.

Kakakin rundunar ‘yansandan jihar, ASP Musa Muhammed bai ce komai kan faruwar lamarin ba zuwa lokacin hada wannan rahoton.

MASU ALAKA

Matsalar Tsaro Da Tsadar Kayan Noma Na Barazana Ga Samar Da Abinci A Daminar Bana
Rahotonni

Matsalar Tsaro Da Tsadar Kayan Noma Na Barazana Ga Samar Da Abinci A Daminar Bana

June 6, 2026
Ban Sha Wata Wahala Ba A Gwagwarmayar Shiga Harkar Fim —Hadiza
Labarai

Ban Sha Wata Wahala Ba A Gwagwarmayar Shiga Harkar Fim —Hadiza

June 6, 2026
Sanata Wamakko Ya Koka Kan Taɓarɓarewar Sha’anin Tsaro
Manyan Labarai

Sanata Wamakko Ya Koka Kan Taɓarɓarewar Sha’anin Tsaro

June 6, 2026
Next Post
RA’AYI: Sauye-sauyen Sheka Ba Zai Sa Ka Ci Zabe Ba A Nijeriya

RA’AYI: Sauye-sauyen Sheka Ba Zai Sa Ka Ci Zabe Ba A Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Rundunar Sojan Kasar Sin Ta Sa Ido Kan Jirgin Ruwan Yakin Kasar Holland Da Ya Tsallake Mashigin Tekun Taiwan

Rundunar Sojan Kasar Sin Ta Sa Ido Kan Jirgin Ruwan Yakin Kasar Holland Da Ya Tsallake Mashigin Tekun Taiwan

June 6, 2026
Sin Tana Adawa Da Karin Takunkumin Da Amurka Ta Sanya Wa Cuba

Sin Tana Adawa Da Karin Takunkumin Da Amurka Ta Sanya Wa Cuba

June 6, 2026
Matsalar Tsaro Da Tsadar Kayan Noma Na Barazana Ga Samar Da Abinci A Daminar Bana

Matsalar Tsaro Da Tsadar Kayan Noma Na Barazana Ga Samar Da Abinci A Daminar Bana

June 6, 2026
Ban Sha Wata Wahala Ba A Gwagwarmayar Shiga Harkar Fim —Hadiza

Ban Sha Wata Wahala Ba A Gwagwarmayar Shiga Harkar Fim —Hadiza

June 6, 2026
Alfanu Da Rashin Alfanun Tallata Hotunan Ango Da Amarya Kafin Daura Aure

Alfanu Da Rashin Alfanun Tallata Hotunan Ango Da Amarya Kafin Daura Aure

June 6, 2026
Darajar Naira Ta Sauka A Kasuwar Musayar Kuɗaɗe

Darajar Naira Ta Sauka A Kasuwar Musayar Kuɗaɗe

June 6, 2026
Yadda Ake Miyar Margi Da Kifin Tarwad

Yadda Ake Miyar Margi Da Kifin Tarwad

June 6, 2026
Sanata Wamakko Ya Koka Kan Taɓarɓarewar Sha’anin Tsaro

Sanata Wamakko Ya Koka Kan Taɓarɓarewar Sha’anin Tsaro

June 6, 2026
A Matsayinki Na Mace, Kada Ki Yi Wasa Da Wadannan Abubuwa

A Matsayinki Na Mace, Kada Ki Yi Wasa Da Wadannan Abubuwa

June 6, 2026
Hadimin El-Rufai Ya Zargi ICPC Da Hana Shi Samun Kulawar Likita

Hadimin El-Rufai Ya Zargi ICPC Da Hana Shi Samun Kulawar Likita

June 6, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.