• English
  • Business News
Saturday, September 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2027: Idan Kana Son Tarwatsa PDP, To Ka Dawo Da Peter Obi – Wike

by Sulaiman and Yusuf Shuaibu
3 weeks ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Daraktoci Da Jami’an FCT 7 Na Fuskantar Tuhume-tuhume Kan Badakar Fili
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ministan Babban Birnin Tarayya Abuja, Nyesom Wike, ya gargadi cewa jam’iyyar PDP za ta fuskantanci hadarin tarwatsewa idan ta yi kokarin dawo da tsohon dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar LP, Peter Obi a cikin jikinta kafin zaben 2027.

 

A yayin wata tattaunawarsa tare da ‘yan jarida, Wike ya ce PDP ba ta dauki darasi ba game da kuskurenta na baya wadanda suka janyo mata rashin nasara a zaben 2023.

  • An Shiga Damuwa Yayin Da Gwamnatin Nijeriya Ke Jinkiri Wajen Biyan ‘Yan Kwangila
  • Gwamnatin Kaduna Ta Zargi El-Rufai Da Yunkurin Tayar Da Tarzoma A Jihar

Ya tunatar da cewa shi da sauran shugabannin jam’iyyar sun sake maimaita wanjen kuskuren na bari dan takarar shugaban kasa da shugaban jam’iyyar na kasa su fito daga yankin arewacin Nijeriya, wannan wani mataki ne na wanda ya saba da tsarin siyasar kasar nan.

 

Labarai Masu Nasaba

Lalacewar Tsarin Zabe Babbar Barazana Ce Ga Dorewar Dimokuradiyyar Afirka — Jonathan

Rudani Ya Kunno Kai Yayin Da INEC Ta Ki Amincewa Da Shugabancin ADC

“Tun daga ranar farko, na gaya wa abokan aikina da ke cikin jam’iyyar PDP cewa kuna daba wa cikinku wuka. Idan kuka bari abubuwan da ke faruwa su ci gaba a haka, za ji a jikinku. Kuma me na ce? Ba za ku iya fitar da dan takarar shugaban kasa da shugaban jam’iyya na kasa su fito a yankin guda ba,” in ji Wike.

 

Tsohon gwamnan Jihar Ribas ya zargi PDP da rashin yin adalci wajen rarraba mukamai da kuma watsi da kiraye-kirayen yin adalci da daidaito, a cewarsa, wannan mataki su ne makasudin rashin nasarar jam’iyyar a zaben bara.

 

“Yana da kyau tun yanzu a warwaren matsalar tikitin takarar shugaban kasa kuma na shugaban jam’iyyar na kasa n. A gani na hakan shi ya fi dacewa. Kuma shi ne adalci a siyasance. Ba na yin dana sani a kan haka,” ya bayyana.

 

Wike ya jaddada cewa dole ne shugabancin kasar nan ya sake komawa yankin kudu don tabbatar da adalci da daidaito a cikin harkokin siyasar Nijeriya.

 

A cewarsa, girman kai da kin sauraron gaskiya daga wasu shugabannin PDP sun sa jam’iyyar taraunata, sannan kuma ta samu rashin karfi tare rasa samun mulki.

 

Ya kuma musanta maganganun da suka shafi yiwuwar dawowar Obi cikin PDP, yana bayyana wannan mataki a matsayin mai tsananin hadari a cikin jam’iyyar.

 

“Ta wani dalili za ku dawo mana da Obi cikin wannan jam’iyyar? Kana son kashe jam’iyyar ne? Obi wanda yake zagin jam’iyyar, yana cewa ta lalace, yanzu kuma jam’iyyar ta zama mai kyau a gare shi ne? Burin mutum na iya sa mutane su kasance har zuwa gidan Shaidan,” in ji Wike.

Ministan ya kara jaddada cewa irin wannan hukunci zai kara lalata ingancin jam’iyyar kuma zai tarwatsa duk wata ginshikin da ya rage a cikin jam’iyyar a halin yanzu.

Ya ce, “Idan kana son tarwatsa jam’iyyar ne, to zai ka gaggauta shigo da Obi cikin jam’iyyar. Babu wata hanya da zai dawo saboda burinsa na kashin kai. Babu dabara da kuma ka’ida a wannan mataki,” ya kara bayyanawa.

Wike ya ci gaba da cewa yana tsaye kan matsayinsa cewa a yi adalci da gaskiya da kuma bin tsarin karba-karba domin ta wannan hanya ce kadai jam’iyyar PDP za ta sau damar dawo da tasirinta a kasar nan.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnatin Kano Ta Ƙuduri Aniyar Daƙile Ambaliyar Ruwa A Birane

Next Post

‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido

Related

Yadda Na Kawo Karshen Yajin Aikin ASUU Cikin Kwana Daya – Jonathan
Tambarin Dimokuradiyya

Lalacewar Tsarin Zabe Babbar Barazana Ce Ga Dorewar Dimokuradiyyar Afirka — Jonathan

2 hours ago
Fursunoni Ba Za Su Samu Damar Kada Kuri’a Ba A Zaben 2023 – INEC
Tambarin Dimokuradiyya

Rudani Ya Kunno Kai Yayin Da INEC Ta Ki Amincewa Da Shugabancin ADC

3 weeks ago
‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido

3 weeks ago
ADC Ta Bukaci Tinubu Ya Kafa Dokar Ta Baci A Katsina Da Zamfara Kan Rashin Tsaro
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ta Bukaci Tinubu Ya Kafa Dokar Ta Baci A Katsina Da Zamfara Kan Rashin Tsaro

4 weeks ago
katin zabe
Tambarin Dimokuradiyya

INEC Ta Bayyana Damuwarta Kan Katunan Zabe 360,000 Da Ba A Karba Ba A Kano

4 weeks ago
Jam’iyyar PDP Ta Janye Daga Shiga Zaɓen Ƙananan Hukumomi A Kebbi
Tambarin Dimokuradiyya

Shugabannin PDP Sun Shiga Dimuwa Yayin Da APC Ke Zawarcin Wasu Gwamnoninsu

4 weeks ago
Next Post
‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido

‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido

LABARAI MASU NASABA

Sabon Farashin Jigilar Mahajjata A 2026, Ƴan Arewa N8.2m, Ƴan Kudu N8.5m

Sabon Farashin Jigilar Mahajjata A 2026, Ƴan Arewa N8.2m, Ƴan Kudu N8.5m

September 27, 2025
Dalilin Gwamnatin Tarayya Da Hukumar FAO Na Zuba Dala Biliyan 3.14 A Fannin Noma

Dalilin Gwamnatin Tarayya Da Hukumar FAO Na Zuba Dala Biliyan 3.14 A Fannin Noma

September 27, 2025
Yadda Na Kawo Karshen Yajin Aikin ASUU Cikin Kwana Daya – Jonathan

Lalacewar Tsarin Zabe Babbar Barazana Ce Ga Dorewar Dimokuradiyyar Afirka — Jonathan

September 27, 2025
Ana Fatan Majalisar Wakilan Amurka Za Ta Taka Muhimmiyar Rawa Wajen Raya Hadin Gwiwar Sin Da Amurka

Ana Fatan Majalisar Wakilan Amurka Za Ta Taka Muhimmiyar Rawa Wajen Raya Hadin Gwiwar Sin Da Amurka

September 26, 2025
2027: Abubuwan Da Jam’iyyun Siyasar Nijeriya Ke Tsammanin Samu Daga Sabon Shugaban INEC

2027: Abubuwan Da Jam’iyyun Siyasar Nijeriya Ke Tsammanin Samu Daga Sabon Shugaban INEC

September 26, 2025
Jerin Tattaunawa Ta Musamman Da CMG Ya Gudanar Sun Maida Hankali Kan GGI

Jerin Tattaunawa Ta Musamman Da CMG Ya Gudanar Sun Maida Hankali Kan GGI

September 26, 2025
’Yansanda Sun Kama ‘Yan Fashi A Kaduna, Sun Ƙwato Bindiga Da Wayoyi

’Yansanda Sun Kama ‘Yan Fashi A Kaduna, Sun Ƙwato Bindiga Da Wayoyi

September 26, 2025
Nazari Kan Littafin Baba Zube Na 5 (Gwamnati)

Nazari Kan Littafin Baba Zube Na 5 (Gwamnati)

September 26, 2025
A Karo Na Hudu ’Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Sun Yi Nasarar Kammala Ayyukansu A Wajen Kumbon

A Karo Na Hudu ’Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Sun Yi Nasarar Kammala Ayyukansu A Wajen Kumbon

September 26, 2025
Katsina Za Ta Ɗauki Nauyin Karatun Mahaddata Alƙur’ani – Gwamna Radda

Sulhu Da ‘Yan Bindiga A Katsina: Nasara Ko Matsala?

September 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.