ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, November 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2027: Idan Kana Son Tarwatsa PDP, To Ka Dawo Da Peter Obi – Wike

by Sulaiman and Yusuf Shuaibu
2 months ago
PDP

Ministan Babban Birnin Tarayya Abuja, Nyesom Wike, ya gargadi cewa jam’iyyar PDP za ta fuskantanci hadarin tarwatsewa idan ta yi kokarin dawo da tsohon dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar LP, Peter Obi a cikin jikinta kafin zaben 2027.

 

A yayin wata tattaunawarsa tare da ‘yan jarida, Wike ya ce PDP ba ta dauki darasi ba game da kuskurenta na baya wadanda suka janyo mata rashin nasara a zaben 2023.

ADVERTISEMENT
  • An Shiga Damuwa Yayin Da Gwamnatin Nijeriya Ke Jinkiri Wajen Biyan ‘Yan Kwangila
  • Gwamnatin Kaduna Ta Zargi El-Rufai Da Yunkurin Tayar Da Tarzoma A Jihar

Ya tunatar da cewa shi da sauran shugabannin jam’iyyar sun sake maimaita wanjen kuskuren na bari dan takarar shugaban kasa da shugaban jam’iyyar na kasa su fito daga yankin arewacin Nijeriya, wannan wani mataki ne na wanda ya saba da tsarin siyasar kasar nan.

 

LABARAI MASU NASABA

Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta

“Tun daga ranar farko, na gaya wa abokan aikina da ke cikin jam’iyyar PDP cewa kuna daba wa cikinku wuka. Idan kuka bari abubuwan da ke faruwa su ci gaba a haka, za ji a jikinku. Kuma me na ce? Ba za ku iya fitar da dan takarar shugaban kasa da shugaban jam’iyya na kasa su fito a yankin guda ba,” in ji Wike.

 

Tsohon gwamnan Jihar Ribas ya zargi PDP da rashin yin adalci wajen rarraba mukamai da kuma watsi da kiraye-kirayen yin adalci da daidaito, a cewarsa, wannan mataki su ne makasudin rashin nasarar jam’iyyar a zaben bara.

 

“Yana da kyau tun yanzu a warwaren matsalar tikitin takarar shugaban kasa kuma na shugaban jam’iyyar na kasa n. A gani na hakan shi ya fi dacewa. Kuma shi ne adalci a siyasance. Ba na yin dana sani a kan haka,” ya bayyana.

 

Wike ya jaddada cewa dole ne shugabancin kasar nan ya sake komawa yankin kudu don tabbatar da adalci da daidaito a cikin harkokin siyasar Nijeriya.

 

A cewarsa, girman kai da kin sauraron gaskiya daga wasu shugabannin PDP sun sa jam’iyyar taraunata, sannan kuma ta samu rashin karfi tare rasa samun mulki.

 

Ya kuma musanta maganganun da suka shafi yiwuwar dawowar Obi cikin PDP, yana bayyana wannan mataki a matsayin mai tsananin hadari a cikin jam’iyyar.

 

“Ta wani dalili za ku dawo mana da Obi cikin wannan jam’iyyar? Kana son kashe jam’iyyar ne? Obi wanda yake zagin jam’iyyar, yana cewa ta lalace, yanzu kuma jam’iyyar ta zama mai kyau a gare shi ne? Burin mutum na iya sa mutane su kasance har zuwa gidan Shaidan,” in ji Wike.

Ministan ya kara jaddada cewa irin wannan hukunci zai kara lalata ingancin jam’iyyar kuma zai tarwatsa duk wata ginshikin da ya rage a cikin jam’iyyar a halin yanzu.

Ya ce, “Idan kana son tarwatsa jam’iyyar ne, to zai ka gaggauta shigo da Obi cikin jam’iyyar. Babu wata hanya da zai dawo saboda burinsa na kashin kai. Babu dabara da kuma ka’ida a wannan mataki,” ya kara bayyanawa.

Wike ya ci gaba da cewa yana tsaye kan matsayinsa cewa a yi adalci da gaskiya da kuma bin tsarin karba-karba domin ta wannan hanya ce kadai jam’iyyar PDP za ta sau damar dawo da tasirinta a kasar nan.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya
Tambarin Dimokuradiyya

Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya

November 7, 2025
Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta
Tambarin Dimokuradiyya

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta

October 17, 2025
peter
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Peter Obi Ya Shiga Rudani Kan Jam’iyyar Da Zai Tsaya Takara

October 17, 2025
Next Post
‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido

‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido

LABARAI MASU NASABA

Coas

Bayan Ganawa Da Tinubu, COAS Ya Tabbatar Wa ‘Yan Nijeriya Samun Ingantaccen Tsaro

November 11, 2025
Sin: Amurka Ba Ta Sa Lura Ga Kare Hakkin Dan Adam

Sin: Amurka Ba Ta Sa Lura Ga Kare Hakkin Dan Adam

November 11, 2025
Bikin CIIE Ya Nuna Yadda Sin Ke Ba Da Jagora Kan Harkokin Bude Kofa

Bikin CIIE Ya Nuna Yadda Sin Ke Ba Da Jagora Kan Harkokin Bude Kofa

November 11, 2025
Za Mu Ci Gaba Da Tallafa Wa ’Yansanda Domin Inganta Ayyukan Su A Zamfara – Gwamna Lawal

Za Mu Ci Gaba Da Tallafa Wa ’Yansanda Domin Inganta Ayyukan Su A Zamfara – Gwamna Lawal

November 11, 2025
CIIE Ya Kasance Gadar Sada Tattalin Arzikin Kasar Sin Da Na Duniya

CIIE Ya Kasance Gadar Sada Tattalin Arzikin Kasar Sin Da Na Duniya

November 11, 2025
CMG Ya Gabatar Da Sabbin Manhajoji 10 Da Ya Kirkiro Don Watsa Gasar Wasannin Motsa Jiki Ta Kasar Sin Karo Na 15

CMG Ya Gabatar Da Sabbin Manhajoji 10 Da Ya Kirkiro Don Watsa Gasar Wasannin Motsa Jiki Ta Kasar Sin Karo Na 15

November 11, 2025
‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutum 3 A Nasarawa

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutum 3 A Nasarawa

November 11, 2025
Cikin Wata Ɗaya, ‘Yansanda Sun Kama Mutane 200 Da Ake Zargi Da Laifuka A Katsina

Cikin Wata Ɗaya, ‘Yansanda Sun Kama Mutane 200 Da Ake Zargi Da Laifuka A Katsina

November 11, 2025
CIIE Ya Ba ‘Yan Kasuwar Afirka Damar Habaka Cinikinsu Da Sin 

CIIE Ya Ba ‘Yan Kasuwar Afirka Damar Habaka Cinikinsu Da Sin 

November 11, 2025
Me Sabon Tarihin Da Aka Kafa A Baje Kolin CIIE Ke Nunawa?

Me Sabon Tarihin Da Aka Kafa A Baje Kolin CIIE Ke Nunawa?

November 11, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.