ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, July 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Kaduna Ta Zargi El-Rufai Da Yunkurin Tayar Da Tarzoma A Jihar

by Sulaiman
10 months ago
uba sani

Gwamnatin Jihar Kaduna ta zargi tsohon gwamnan jihar, Malam Nasir El-Rufai, da kokarin jefa jihar cikin rashin kwanciyar hankali ta hanyar abin da ta bayyana a matsayin ayyuka masu tayar da hankali da ikirarin karya.

 

A cikin wata sanarwa da aka fitar a Kaduna, kwamishinan Tsaro da Harkokin Cikin Gida, Dr. Suleiman Shuaibu, ya zargi El-Rufai da shirin dawo da jihar cikin rarrabuwar kawuna ta tashin hankali, inda ya ce gwamnati ba za ta lamunci kowanne yunkurin barazana ga zaman lafiya ba.

ADVERTISEMENT
  • Spence Na Dab Da Kafa Tarihin Zama Musulmi Na Farko Da Zai Buga Wa Ingila Ƙwallo
  • An Kaddamar Da Cibiyar Raya Ilimin Dijital Ta Sin Da Afirka A Tanzania

“Gwamnatin ba za ta zauna ta yi shiru ta bar tsohon shugaba da ya bar jihar cikin halin tabarbarewa, ya tayar da rikici ya jefa Kaduna cikin wani sabon yanayi na tashin hankali na kabilanci da addini, rashin tsaro da koma bayan tattalin arziki ba,” in ji wani bangare na sanarwar.

 

LABARAI MASU NASABA

Sana’ar Ƙosai: Remi Tinubu Ta Yi Kira ga Burna Boy da Davido Su Taimaka wa Talakawa

Mahara Sun Kashe Mutane 9 Ƴan Gida Ɗaya, Har Da Jariri Ɗan Wata 2 A Filato

Dr. Shuaibu ya ce maganganun El-Rufai na baya-bayan nan, ciki har da zargin da ya yi a talabijin na kasa cewa gwamnati ta tarayya da ta jihar na “ba wa ‘yan ta’adda cin hanci,” karya ne, mai hadari, kuma an yi su ne don raunana kokarin tsaro. Ya kara da cewa Ofishin Mai Ba Shugaban Kasa Shawara kan Harkokin Tsaron (ONSA) ya riga ya musanta wannan zargi a matsayin mara tushe.

 

Ya ce hukumomin tsaro da shirye-shiryen cikin gida sun samu nasarori masu yawa a karkashin gwamna Uba Sani, inda ya bayar da misalin cafke manyan shugabannin ‘yan ta’adda da kuma dawo da kwanciyar hankali a yankunan da ke cikin tashin hankali kamar Birnin Gwari, Giwa, Kajuru da Kachia.

 

Kwamishinan ya kara da zargin cewa El-Rufai ya kara kokarin yin tasiri bayan kalubalen siyasa da abokan siyasa na suka fuskanta a yayin zaben cike gurbi na 16 ga Agusta. Ya kuma bayyana cewa gwamnatin Gwamna Sani ta mai da hankali kan gina zaman lafiya, hadin kai da ci gaba, kuma ba za ta bar kowanne mutum ya “kawo koma-baya ga ci gaban da aka samu” ba. A daya bangaren kuma Kungiyar Kwararrun ‘Yan APC (ALP) ta nuna rashin jin dadi kan maganganun da ake danganta wa tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Mallam Nasir El-Rufai, inda ya yi zargin cewa gwamnatin tarayya karkashin Shugaba Bola Ahmed Tinubu na kara wa ‘yan ta’adda karfi.

El-Rufai
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Sana’ar Ƙosai: Remi Tinubu Ta Yi Kira ga Burna Boy da Davido Su Taimaka wa Talakawa
  • Sulaiman
    Sin Tana Matsayi Na Farko A Duniya A Fannin Kirkire-kirkiren Wutar Lantarki
  • Sulaiman
    Sin Ta Yi Kunnen Doki Da Nijeriya A Gasar Kwallon Kafa Tsakanin Kasashe 4 Ta ‘Yan Kasa Da 17
  • Sulaiman
    Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Fitar Da Sanarwa Game Da Cika Shekaru 10 Da Fitar Da Hukuncin Takkadamar “Philippines Da China”

MASU ALAKA

Sana’ar Ƙosai: Remi Tinubu Ta Yi Kira ga Burna Boy da Davido Su Taimaka wa Talakawa
Manyan Labarai

Sana’ar Ƙosai: Remi Tinubu Ta Yi Kira ga Burna Boy da Davido Su Taimaka wa Talakawa

July 13, 2026
Mahara Sun Kashe Mutane 9 Ƴan Gida Ɗaya, Har Da Jariri Ɗan Wata 2 A Filato
Manyan Labarai

Mahara Sun Kashe Mutane 9 Ƴan Gida Ɗaya, Har Da Jariri Ɗan Wata 2 A Filato

July 12, 2026
Hukumar Alhazai Ta Kano Ta Sa Miliyan 8.5 A Matsayin Kuɗin Hajjin 2027
Manyan Labarai

Hukumar Alhazai Ta Kano Ta Sa Miliyan 8.5 A Matsayin Kuɗin Hajjin 2027

July 12, 2026
Next Post
Ministan Wajen Najeriya: Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Ya Samarwa Afirka Damammakin Ci Gaba

Ma’aikatan Ofishin Jakadancin Nijeriya Sun Koka Kan Rashin Biyan Basussukan Albashi

LABARAI MASU NASABA

Sana’ar Ƙosai: Remi Tinubu Ta Yi Kira ga Burna Boy da Davido Su Taimaka wa Talakawa

Sana’ar Ƙosai: Remi Tinubu Ta Yi Kira ga Burna Boy da Davido Su Taimaka wa Talakawa

July 13, 2026
Sin Tana Matsayi Na Farko A Duniya A Fannin Kirkire-kirkiren Wutar Lantarki

Sin Tana Matsayi Na Farko A Duniya A Fannin Kirkire-kirkiren Wutar Lantarki

July 12, 2026
Mahara Sun Kashe Mutane 9 Ƴan Gida Ɗaya, Har Da Jariri Ɗan Wata 2 A Filato

Mahara Sun Kashe Mutane 9 Ƴan Gida Ɗaya, Har Da Jariri Ɗan Wata 2 A Filato

July 12, 2026
Sin Ta Yi Kunnen Doki Da Nijeriya A Gasar Kwallon Kafa Tsakanin Kasashe 4 Ta ‘Yan Kasa Da 17

Sin Ta Yi Kunnen Doki Da Nijeriya A Gasar Kwallon Kafa Tsakanin Kasashe 4 Ta ‘Yan Kasa Da 17

July 12, 2026
FIFA Na Nazarin Faɗaɗa Gasar Kofin Duniya Zuwa Ƙasashe 64

FIFA Na Nazarin Faɗaɗa Gasar Kofin Duniya Zuwa Ƙasashe 64

July 12, 2026
Hukumar Alhazai Ta Kano Ta Sa Miliyan 8.5 A Matsayin Kuɗin Hajjin 2027

Hukumar Alhazai Ta Kano Ta Sa Miliyan 8.5 A Matsayin Kuɗin Hajjin 2027

July 12, 2026
Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Fitar Da Sanarwa Game Da Cika Shekaru 10 Da Fitar Da Hukuncin Takkadamar “Philippines Da China”

Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Fitar Da Sanarwa Game Da Cika Shekaru 10 Da Fitar Da Hukuncin Takkadamar “Philippines Da China”

July 12, 2026
Atiku Ya Soki Shirin Ƙara Kuɗin Jarabawar WAEC Da NECO Zuwa N50,000

Atiku Ya Soki Shirin Ƙara Kuɗin Jarabawar WAEC Da NECO Zuwa N50,000

July 12, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Daraktan Hollywood Carl Rinsch Zai Shafe Watanni 30 A Gidan Gyaran Hali

July 12, 2026
Mataimakin Firaministan Sin Ya Jadadda Bukatar Kare Rayuka Da Dukiyoyin Jama’a Yayin Rangadi A Beijing

Mataimakin Firaministan Sin Ya Jadadda Bukatar Kare Rayuka Da Dukiyoyin Jama’a Yayin Rangadi A Beijing

July 12, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.