ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, June 22, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Kaduna Ta Zargi El-Rufai Da Yunkurin Tayar Da Tarzoma A Jihar

by Sulaiman
10 months ago
uba sani

Gwamnatin Jihar Kaduna ta zargi tsohon gwamnan jihar, Malam Nasir El-Rufai, da kokarin jefa jihar cikin rashin kwanciyar hankali ta hanyar abin da ta bayyana a matsayin ayyuka masu tayar da hankali da ikirarin karya.

 

A cikin wata sanarwa da aka fitar a Kaduna, kwamishinan Tsaro da Harkokin Cikin Gida, Dr. Suleiman Shuaibu, ya zargi El-Rufai da shirin dawo da jihar cikin rarrabuwar kawuna ta tashin hankali, inda ya ce gwamnati ba za ta lamunci kowanne yunkurin barazana ga zaman lafiya ba.

ADVERTISEMENT
  • Spence Na Dab Da Kafa Tarihin Zama Musulmi Na Farko Da Zai Buga Wa Ingila Ƙwallo
  • An Kaddamar Da Cibiyar Raya Ilimin Dijital Ta Sin Da Afirka A Tanzania

“Gwamnatin ba za ta zauna ta yi shiru ta bar tsohon shugaba da ya bar jihar cikin halin tabarbarewa, ya tayar da rikici ya jefa Kaduna cikin wani sabon yanayi na tashin hankali na kabilanci da addini, rashin tsaro da koma bayan tattalin arziki ba,” in ji wani bangare na sanarwar.

 

LABARAI MASU NASABA

Yanzu-Yanzu: An Kashe Manoma 18 Da Raunata Wasu A Wani Sabon Hari A Filato

Yanzu-Yanzu: Firaiministan Birtaniya Keir Starmer Ya Yi Murabus

Dr. Shuaibu ya ce maganganun El-Rufai na baya-bayan nan, ciki har da zargin da ya yi a talabijin na kasa cewa gwamnati ta tarayya da ta jihar na “ba wa ‘yan ta’adda cin hanci,” karya ne, mai hadari, kuma an yi su ne don raunana kokarin tsaro. Ya kara da cewa Ofishin Mai Ba Shugaban Kasa Shawara kan Harkokin Tsaron (ONSA) ya riga ya musanta wannan zargi a matsayin mara tushe.

 

Ya ce hukumomin tsaro da shirye-shiryen cikin gida sun samu nasarori masu yawa a karkashin gwamna Uba Sani, inda ya bayar da misalin cafke manyan shugabannin ‘yan ta’adda da kuma dawo da kwanciyar hankali a yankunan da ke cikin tashin hankali kamar Birnin Gwari, Giwa, Kajuru da Kachia.

 

Kwamishinan ya kara da zargin cewa El-Rufai ya kara kokarin yin tasiri bayan kalubalen siyasa da abokan siyasa na suka fuskanta a yayin zaben cike gurbi na 16 ga Agusta. Ya kuma bayyana cewa gwamnatin Gwamna Sani ta mai da hankali kan gina zaman lafiya, hadin kai da ci gaba, kuma ba za ta bar kowanne mutum ya “kawo koma-baya ga ci gaban da aka samu” ba. A daya bangaren kuma Kungiyar Kwararrun ‘Yan APC (ALP) ta nuna rashin jin dadi kan maganganun da ake danganta wa tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Mallam Nasir El-Rufai, inda ya yi zargin cewa gwamnatin tarayya karkashin Shugaba Bola Ahmed Tinubu na kara wa ‘yan ta’adda karfi.

El-Rufai
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Cibiyar CBA Ta Kenya Za Ta Yi Hadin Gwiwa Da Wata Cibiyar Sin Wajen Bunkasa Noma Da Cinikayyar Lemar Kwadi
  • Sulaiman
    An Sanar Da Wadanda Suka Lashe Golden Goblet Na Bikin Fina-Finen Kasa Da Kasa Na Shanghai Karo Na 28
  • Sulaiman
    Nasiha Ga Uwargida Kan Zafin Kishi (1)
  • Sulaiman
    Kasar Sin Ta Karbi Bakuncin Taron Daidaita Batun Kare Hakkin Dan Adam

MASU ALAKA

Yanzu-Yanzu: An Kashe Manoma 18 Da Raunata Wasu A Wani Sabon Hari A Filato
Manyan Labarai

Yanzu-Yanzu: An Kashe Manoma 18 Da Raunata Wasu A Wani Sabon Hari A Filato

June 22, 2026
Yanzu-Yanzu: Firaiministan Birtaniya Keir Starmer Ya Yi Murabus
Labarai

Yanzu-Yanzu: Firaiministan Birtaniya Keir Starmer Ya Yi Murabus

June 22, 2026
Sojoji Sun Ceto Mutanen Da Aka Sace, Sun Daƙile Hari A Kaduna Da Zamfara
Manyan Labarai

Sojoji Sun Ceto Mutanen Da Aka Sace, Sun Daƙile Hari A Kaduna Da Zamfara

June 22, 2026
Next Post
Ministan Wajen Najeriya: Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Ya Samarwa Afirka Damammakin Ci Gaba

Ma’aikatan Ofishin Jakadancin Nijeriya Sun Koka Kan Rashin Biyan Basussukan Albashi

LABARAI MASU NASABA

Yanzu-Yanzu: An Kashe Manoma 18 Da Raunata Wasu A Wani Sabon Hari A Filato

Yanzu-Yanzu: An Kashe Manoma 18 Da Raunata Wasu A Wani Sabon Hari A Filato

June 22, 2026
Yanzu-Yanzu: Firaiministan Birtaniya Keir Starmer Ya Yi Murabus

Yanzu-Yanzu: Firaiministan Birtaniya Keir Starmer Ya Yi Murabus

June 22, 2026
Sojoji Sun Ceto Mutanen Da Aka Sace, Sun Daƙile Hari A Kaduna Da Zamfara

Sojoji Sun Ceto Mutanen Da Aka Sace, Sun Daƙile Hari A Kaduna Da Zamfara

June 22, 2026
Fisatattun Matasa Sun Ƙone Wata Mata Ƙurmus Kan Jita-Jitar Satar Yara A Kaduna

Fisatattun Matasa Sun Ƙone Wata Mata Ƙurmus Kan Jita-Jitar Satar Yara A Kaduna

June 22, 2026

Mutane 842 Ne Suka Rasa Ransu, Aka Yi Garkuwa Da Sama Da 270 A Watan Mayu – Rahoto

June 21, 2026
PRP Ta Zargi Kwankwaso Da Saye Fom Ɗin Takarar  Jamiyyar

PRP Ta Zargi Kwankwaso Da Saye Fom Ɗin Takarar Jamiyyar

June 21, 2026
An Ƙaddamar Da Dakarun Tsaron Daji 2,187 A Bauchi

An Ƙaddamar Da Dakarun Tsaron Daji 2,187 A Bauchi

June 21, 2026
An Sanar Da Wadanda Suka Lashe Golden Goblet Na Bikin Fina-Finen Kasa Da Kasa Na Shanghai Karo Na 28

An Sanar Da Wadanda Suka Lashe Golden Goblet Na Bikin Fina-Finen Kasa Da Kasa Na Shanghai Karo Na 28

June 21, 2026
Cibiyar CBA Ta Kenya Za Ta Yi Hadin Gwiwa Da Wata Cibiyar Sin Wajen Bunkasa Noma Da Cinikayyar Lemar Kwadi

Cibiyar CBA Ta Kenya Za Ta Yi Hadin Gwiwa Da Wata Cibiyar Sin Wajen Bunkasa Noma Da Cinikayyar Lemar Kwadi

June 21, 2026
Wasu Abubuwa Da Ke Sa Maza Hana Mata Fita Unguwa (Uwargida)

Nasiha Ga Uwargida Kan Zafin Kishi (1)

June 21, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.