• English
  • Business News
Sunday, October 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2027: Kungiyoyi 110 Ne Ke Neman Rajistan Zama Jam’iyyun Siyasa A Yanzu Haka – INEC

by Yusuf Shuaibu
3 months ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Zaben Gwamnoni: Za Mu Ba Marada Kunya – INEC
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC), Farfesa Mahmood Yakubu, ya bayyana cewa hukumar ta karbi wasikun kungiyoyi 110 da ke neman rajista a matsayin jam’iyyu siyasa kafin zaben 2027.

Yakubu ya bayyana hakan a yayin taron INEC tare da manyan jami’an kafafen watsa labarai da aka gudanar a Abuja.

  • Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 1,191, Sun Ceto 543 Cikin Watanni Uku
  • Kamfanin Simintin Dangote Ya Tallafa Wa Manoma 50 A Benue

Shugaban INEC ya bayyana cewa tun ranar 23 ga Yuni, hukumar ta karbi wasikun kuma tana gudanar da aiki a kansu bisa doka da ka’idojin zabe.

“Tun a ranar Litinin, 23 ga Yuni 2025, hukumar ta karbi wasikun kungiyoyi 110 da suke son rajista a matsayin jam’iyyu na siyasa. Muna aiki tukuru wajen sarrafa bukatun tare da bin tsarin da aka gindaya a cikin doka da kuma ka’idojinmu na zabe.

“Mun amince da duk bukatun ban da guda shida da aka karba kwanan nan wadanda za a kammala aikinsu kafin karshen mako,” ya bayyana.

Labarai Masu Nasaba

ADC Ta Umarci Dukkan Mambobinta Su Yi Murabus Daga Tsoffin Jam’iyyunsu

Dage Zaben Shugabannin PDP Na Jihohi Ya Kara Ruruta Wutar Rikici A Jam’iyyar

Yakubu ya jaddada kokarin hukuma wajen yin adalci.

“Za mu duba dukkan bukatun cikin adalci ba tare da la’akari da matsayin wadanda suka kawo su ba, lallai hukumar zabe ba za ta taba karya ka’idojinta ba.”

Shugaban INEC ya musanta zarginsu cewa hukumar kokarin hada kai da wasu domin saba ka’ida wajen yin ragisara, ya tunawa da irin wannan zargin da ba tare da hujja ba da aka yi a shekarar 2013.

Ya bayyana cewa hukumar ta amince da dukkan wasikun da aka karba illa guda shida, wadanda za a yi aiki a kai kafin karshen mako. Haka nan ya lura cewa dokoki da ka’idojin zabe ta 2022 kan jam’iyyun siyasa yana nan a shafin intanet na hukumar.

Yakubu ya kara da cewa za a fitar da cikakken jerin kungiyoyi 110, ciki har da sunayensu da yadda ake takaitawa da adireshi, da sunayen shugabanninsu da sakatarensu, nan ba da jumawa ba za a wallafa su a shafin intanet na INEC da kafofin sada zumunta don tabbatar da gaskiyar lamari ga jama’a.

Daya daga cikin kungiyoyin masu neman zama jam’iyyun siyasa, ADA ana zargin cewa ta samu goyon bayan ne da hadakar wasu shahararrun mutane masu tasiri a siyasa, ciki har da tsohon mataimakin shugaban kasa Atiku Abubakar da tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, da kuma tsohon gwamnan Jihar Ribas, Rotimi Amaechi.

Wata kungiyar kuma wanda ake tsammanin tana samun goyon baya daga magoya bayan tsohon dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar LP, Peter Obi, ta gabatar da bukatar rajista karkashin suna mai kama da na LP, wanda ke nuna damuwa game da yiwuwar maimaitawar sunan LP.

INEC ta ce akwai kura-kurai mai yawan gaske a cikin wasu takardun da aka gabatar. Wasu daga cikin kungiyoyin sun yi amfani da suna iri daya, wanda hakan ya sab awa ka’idodin INEC.

Kazalika, INEC ta gano cewa akwai kungiyar da ta gabatar da bukatar yin rajistar guda biyu, kowanne tare da shugabanci da adireshi daban.

INEC ta bayyana cewa za ta tantance dukkan bukatun bisa ga tsarin doka da ka’idojin aikinta kafin ta yi rajista ko ta ki.

Bugu da kari, INEC ta ce akwai bukatar da aka shigar mata na neman yin rajista daban-daban har guda biyu a karkashin sunan ‘Obidient Peoples Party’.

A cewarta, wasu ana takaita sunayenu sun yi kama da na jam’iyyun da aka soke rajistarsu a baya, kuma an shigar da wasu takardu ba tare da sa sunayen shugabannin jam’iyyar ba, wanda haka ya saba wa ka’idojin INEC.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: INEC
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin: Tsawaitar Rikicin Ukraine Ba Zai Amfani Kowa Ba

Next Post

Sin Da Ghana Za Su Karfafa Hadin Gwiwarsu

Related

ADC Ta Dakatar Da Shugabanta Da Wasu Jiga-jigai 3 A Kebbi
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ta Umarci Dukkan Mambobinta Su Yi Murabus Daga Tsoffin Jam’iyyunsu

1 day ago
Dage Zaben Shugabannin PDP Na Jihohi Ya Kara Ruruta Wutar Rikici A Jam’iyyar
Tambarin Dimokuradiyya

Dage Zaben Shugabannin PDP Na Jihohi Ya Kara Ruruta Wutar Rikici A Jam’iyyar

1 day ago
Yadda Na Kawo Karshen Yajin Aikin ASUU Cikin Kwana Daya – Jonathan
Tambarin Dimokuradiyya

Lalacewar Tsarin Zabe Babbar Barazana Ce Ga Dorewar Dimokuradiyyar Afirka — Jonathan

1 week ago
Fursunoni Ba Za Su Samu Damar Kada Kuri’a Ba A Zaben 2023 – INEC
Tambarin Dimokuradiyya

Rudani Ya Kunno Kai Yayin Da INEC Ta Ki Amincewa Da Shugabancin ADC

4 weeks ago
‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido

4 weeks ago
Daraktoci Da Jami’an FCT 7 Na Fuskantar Tuhume-tuhume Kan Badakar Fili
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Idan Kana Son Tarwatsa PDP, To Ka Dawo Da Peter Obi – Wike

4 weeks ago
Next Post
Sin Da Ghana Za Su Karfafa Hadin Gwiwarsu

Sin Da Ghana Za Su Karfafa Hadin Gwiwarsu

LABARAI MASU NASABA

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

October 4, 2025
Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

October 4, 2025
Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

October 4, 2025
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

October 4, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

October 4, 2025
Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

October 4, 2025
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

October 4, 2025
Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

October 4, 2025
Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

October 4, 2025
Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

October 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.