• English
  • Business News
Wednesday, September 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2027: Kungiyoyi 110 Ne Ke Neman Rajistan Zama Jam’iyyun Siyasa A Yanzu Haka – INEC

by Yusuf Shuaibu
2 months ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Zaben Gwamnoni: Za Mu Ba Marada Kunya – INEC
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC), Farfesa Mahmood Yakubu, ya bayyana cewa hukumar ta karbi wasikun kungiyoyi 110 da ke neman rajista a matsayin jam’iyyu siyasa kafin zaben 2027.

Yakubu ya bayyana hakan a yayin taron INEC tare da manyan jami’an kafafen watsa labarai da aka gudanar a Abuja.

  • Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 1,191, Sun Ceto 543 Cikin Watanni Uku
  • Kamfanin Simintin Dangote Ya Tallafa Wa Manoma 50 A Benue

Shugaban INEC ya bayyana cewa tun ranar 23 ga Yuni, hukumar ta karbi wasikun kuma tana gudanar da aiki a kansu bisa doka da ka’idojin zabe.

“Tun a ranar Litinin, 23 ga Yuni 2025, hukumar ta karbi wasikun kungiyoyi 110 da suke son rajista a matsayin jam’iyyu na siyasa. Muna aiki tukuru wajen sarrafa bukatun tare da bin tsarin da aka gindaya a cikin doka da kuma ka’idojinmu na zabe.

“Mun amince da duk bukatun ban da guda shida da aka karba kwanan nan wadanda za a kammala aikinsu kafin karshen mako,” ya bayyana.

Labarai Masu Nasaba

Rudani Ya Kunno Kai Yayin Da INEC Ta Ki Amincewa Da Shugabancin ADC

‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido

Yakubu ya jaddada kokarin hukuma wajen yin adalci.

“Za mu duba dukkan bukatun cikin adalci ba tare da la’akari da matsayin wadanda suka kawo su ba, lallai hukumar zabe ba za ta taba karya ka’idojinta ba.”

Shugaban INEC ya musanta zarginsu cewa hukumar kokarin hada kai da wasu domin saba ka’ida wajen yin ragisara, ya tunawa da irin wannan zargin da ba tare da hujja ba da aka yi a shekarar 2013.

Ya bayyana cewa hukumar ta amince da dukkan wasikun da aka karba illa guda shida, wadanda za a yi aiki a kai kafin karshen mako. Haka nan ya lura cewa dokoki da ka’idojin zabe ta 2022 kan jam’iyyun siyasa yana nan a shafin intanet na hukumar.

Yakubu ya kara da cewa za a fitar da cikakken jerin kungiyoyi 110, ciki har da sunayensu da yadda ake takaitawa da adireshi, da sunayen shugabanninsu da sakatarensu, nan ba da jumawa ba za a wallafa su a shafin intanet na INEC da kafofin sada zumunta don tabbatar da gaskiyar lamari ga jama’a.

Daya daga cikin kungiyoyin masu neman zama jam’iyyun siyasa, ADA ana zargin cewa ta samu goyon bayan ne da hadakar wasu shahararrun mutane masu tasiri a siyasa, ciki har da tsohon mataimakin shugaban kasa Atiku Abubakar da tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, da kuma tsohon gwamnan Jihar Ribas, Rotimi Amaechi.

Wata kungiyar kuma wanda ake tsammanin tana samun goyon baya daga magoya bayan tsohon dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar LP, Peter Obi, ta gabatar da bukatar rajista karkashin suna mai kama da na LP, wanda ke nuna damuwa game da yiwuwar maimaitawar sunan LP.

INEC ta ce akwai kura-kurai mai yawan gaske a cikin wasu takardun da aka gabatar. Wasu daga cikin kungiyoyin sun yi amfani da suna iri daya, wanda hakan ya sab awa ka’idodin INEC.

Kazalika, INEC ta gano cewa akwai kungiyar da ta gabatar da bukatar yin rajistar guda biyu, kowanne tare da shugabanci da adireshi daban.

INEC ta bayyana cewa za ta tantance dukkan bukatun bisa ga tsarin doka da ka’idojin aikinta kafin ta yi rajista ko ta ki.

Bugu da kari, INEC ta ce akwai bukatar da aka shigar mata na neman yin rajista daban-daban har guda biyu a karkashin sunan ‘Obidient Peoples Party’.

A cewarta, wasu ana takaita sunayenu sun yi kama da na jam’iyyun da aka soke rajistarsu a baya, kuma an shigar da wasu takardu ba tare da sa sunayen shugabannin jam’iyyar ba, wanda haka ya saba wa ka’idojin INEC.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: INEC
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin: Tsawaitar Rikicin Ukraine Ba Zai Amfani Kowa Ba

Next Post

Sin Da Ghana Za Su Karfafa Hadin Gwiwarsu

Related

Fursunoni Ba Za Su Samu Damar Kada Kuri’a Ba A Zaben 2023 – INEC
Tambarin Dimokuradiyya

Rudani Ya Kunno Kai Yayin Da INEC Ta Ki Amincewa Da Shugabancin ADC

4 days ago
‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido

5 days ago
Daraktoci Da Jami’an FCT 7 Na Fuskantar Tuhume-tuhume Kan Badakar Fili
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Idan Kana Son Tarwatsa PDP, To Ka Dawo Da Peter Obi – Wike

5 days ago
ADC Ta Bukaci Tinubu Ya Kafa Dokar Ta Baci A Katsina Da Zamfara Kan Rashin Tsaro
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ta Bukaci Tinubu Ya Kafa Dokar Ta Baci A Katsina Da Zamfara Kan Rashin Tsaro

2 weeks ago
katin zabe
Tambarin Dimokuradiyya

INEC Ta Bayyana Damuwarta Kan Katunan Zabe 360,000 Da Ba A Karba Ba A Kano

2 weeks ago
Jam’iyyar PDP Ta Janye Daga Shiga Zaɓen Ƙananan Hukumomi A Kebbi
Tambarin Dimokuradiyya

Shugabannin PDP Sun Shiga Dimuwa Yayin Da APC Ke Zawarcin Wasu Gwamnoninsu

2 weeks ago
Next Post
Sin Da Ghana Za Su Karfafa Hadin Gwiwarsu

Sin Da Ghana Za Su Karfafa Hadin Gwiwarsu

LABARAI MASU NASABA

Tayar Da Yaki A Zamanin Nan Kauyanci Ne

Tayar Da Yaki A Zamanin Nan Kauyanci Ne

September 10, 2025
INEC Ta Amince Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

INEC Ta Amince Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

September 10, 2025
Sin Za Ta Kafa Yankin Kare Muhallin Halittu Na Huangyan Dao

Sin Za Ta Kafa Yankin Kare Muhallin Halittu Na Huangyan Dao

September 10, 2025
An Ɗauke Wuta Sakamakon Lalacewar Babbar Tashar Lantarkin Nijeriya

An Ɗauke Wuta Sakamakon Lalacewar Babbar Tashar Lantarkin Nijeriya

September 10, 2025
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamnatin Kaduna Ta Umarci Makarantu Masu Zaman Kansu Da Su Nemi Amincewarta Kafin Ƙara Kuɗi

September 10, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Hasashen Ambaliyar Ruwa A Jihohin Arewa 15

Yadda Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Yaya Da Ƙannuwa Da Wasu A Zaria

September 10, 2025
Kwankwaso Ya Gana Da Shugabannin NNPP A Kuros Ribas Don Tunkarar Zaɓen 2027

Kwankwaso Ya Gana Da Shugabannin NNPP A Kuros Ribas Don Tunkarar Zaɓen 2027

September 10, 2025
Akwai Tara Mai Tsauri Ga Duk Wanda Ya Sare Bishiya Ba Bisa Ƙa’ida Ba – Gwamnatin Kano

Akwai Tara Mai Tsauri Ga Duk Wanda Ya Sare Bishiya Ba Bisa Ƙa’ida Ba – Gwamnatin Kano

September 10, 2025
majalisar kasa

Majalisa Ta Bai Wa Minista Sa’o’i 48 Ya Bayyana A Gabanta Kan Hatsarin Jirgin Abuja Zuwa Kaduna

September 10, 2025
Kasar Sin Ta Zama Dandalin Karfafa Cudanya Da Cinikayya Tsakanin Kasa Da Kasa

Kasar Sin Ta Zama Dandalin Karfafa Cudanya Da Cinikayya Tsakanin Kasa Da Kasa

September 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.