ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NNPP Ta Buƙaci INEC Ta Yi Watsi Da Tarukan Jam’iyyar Da Kwankwaso Zai Jagoranta

by Sulaiman
9 months ago
Kwankwaso

Jam’iyyar NNPP ta bukaci hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) da ‘yan Nijeriya da su yi watsi da tarukan jam’iyya da ake ikirarin jagoran Kwankwasiyya, Sanata Rabiu Kwankwaso zai jagoranta, inda ta bayyana cewa tarukan sun sab awa doka.

A cikin wata sanarwa da sakataren jam’iyyar na kasa, Mista Ogini Olaposi, ya fitar, jam’iyyar ta bayyana cewa kotu ta umurci NNPP ta gudanar da tarukanta na kasa kuma an kammala su.

  • Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina
  • Shekara 25 Da Kafa ACF: Nasarori, Matsaloli Da Ƙalubale

Kamfanin dillancin labarai na Nijeriya ya ruwaito cewa Kwankwaso ya aika da wasika ga INEC, yana sanar da hukumar game da shirin gudanar da sabbin tarukan jam’iyya NNPP, daga 25 ga Nuwamba, zuwa Janairu 2026.

ADVERTISEMENT

Jam’iyyar ta bayyana cewa kungiyar Kwankwasiyya ba za ta iya gudanar da babban taron jam’iyya a madadinta ba, saboda yarjejeniyar da aka kulla zaben shugaban kasa na 2023 ya shude.

Jam’iyyar ta lura cewa Kwankwaso, dan takarar shugaban kasa na NNPP na 2023, da wasu ‘yan kungiyar Kwankwasiya sun ci gaba da ficewa daga cikin jam’iyyar saboda cin amanan jam’iyyar.

LABARAI MASU NASABA

2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta

“Har yanzu muna mamakin cewa wani mutum mai matsayi kamar na Kwankwaso zai nace wajen sace jam’iyyar da ta ba shi takara a zaben shugaban kasa na 2023 kyauta.”

NNPP ta bayyana cewa INEC dole ne ta cika nauyin da ke kansa ta hanyar bin dokokin kotu da kuma saka sahihan shugabannin jam’iyyar a adireshinta na intanet.

“Babbar kotun ta Jihar Abiya da babbar kotu a Abuja sun tabbatar da hana Kwankwaso da kungiyarsa daga shiga tsarin dimokuradiyya na cikin gida na NNPP kuma idan ya saba za a ladabtar da shi.

Abun bakin ciki ne cewa ana iya ganin Kwankwaso yana gudanar da kansa cikin rashin girmamawa ta hanyar kin bin hukuncin kotu da kuma karya doka.

“Shugabancin INEC na baya ya gaza mana, kuma muna fatan cewa shugabanci na yanzu zai nisanci rashin biyayya ga bin doka da oda na al’umma.

“Har yanzu muna mamakin dalilin da ya sa INEC ba ta mayar da martani ga wasikunmu da ke bukatar a mutunta bin hukuncin kotuna ba.

“A matsayinta na mai yanke hukunci, bai kata INEC ta ci gaba da zura ido kan al’amurar da ke bukatar hukunci cikin gaggawa ba da suka shafi zaman lafiyar al’umma.”

A cewar jam’iyyar, INEC tana da masaniya game da hukuncin kotu, duk da haka, tana mai da hankali ga kungiyoyin da ke son haddasa rikici a cikin dimokuracdiyyar Nijeriya.

“Mun rubuta wasiku da dama zuwa INEC kan wadannan lamarin, duk da haka, hukumar ta yi burus wanda hakn yana karfafa rashin biyayya ga dokokin Nijeriya.

“A karkashin irin wannan yanayi, za mu ci gaba da kiyaye zaman lafiya ga al’umma kuma mun umurci ‘yan jam’iyyarmu su yi watsi da taruka da zaben shugabannin jam’iyyar na bogi.

“Muna kara kira ga INEC ta taimaka wa dimokiradiyya tare da ceto Nijeriya. Ajandar sabon fata ta gwamnatin tarayya a yanzu za ta iya samun nasara ne kawai idan ana bin dokoki kuma ana girmama su”.

Kwankwaso
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan
  • Sulaiman
    ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto
  • Sulaiman
    PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi
  • Sulaiman
    Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

MASU ALAKA

2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe
Tambarin Dimokuradiyya

2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe

September 5, 2026
Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta
Tambarin Dimokuradiyya

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta

September 4, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
Tambarin Dimokuradiyya

INEC Ta Zayyano Kalubalen Da Ke Iya Shafar Sahihancin Zaben 2027

August 28, 2026
Next Post
Furucin Takaichi Game Da Taiwan Ya Aike Da Mummunan Sako Ga ’Yan Awaren Yankin

Furucin Takaichi Game Da Taiwan Ya Aike Da Mummunan Sako Ga ’Yan Awaren Yankin

LABARAI MASU NASABA

Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.