ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NNPP Ta Buƙaci INEC Ta Yi Watsi Da Tarukan Jam’iyyar Da Kwankwaso Zai Jagoranta

by Sulaiman
7 months ago
Kwankwaso

Jam’iyyar NNPP ta bukaci hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) da ‘yan Nijeriya da su yi watsi da tarukan jam’iyya da ake ikirarin jagoran Kwankwasiyya, Sanata Rabiu Kwankwaso zai jagoranta, inda ta bayyana cewa tarukan sun sab awa doka.

A cikin wata sanarwa da sakataren jam’iyyar na kasa, Mista Ogini Olaposi, ya fitar, jam’iyyar ta bayyana cewa kotu ta umurci NNPP ta gudanar da tarukanta na kasa kuma an kammala su.

  • Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina
  • Shekara 25 Da Kafa ACF: Nasarori, Matsaloli Da Ƙalubale

Kamfanin dillancin labarai na Nijeriya ya ruwaito cewa Kwankwaso ya aika da wasika ga INEC, yana sanar da hukumar game da shirin gudanar da sabbin tarukan jam’iyya NNPP, daga 25 ga Nuwamba, zuwa Janairu 2026.

ADVERTISEMENT

Jam’iyyar ta bayyana cewa kungiyar Kwankwasiyya ba za ta iya gudanar da babban taron jam’iyya a madadinta ba, saboda yarjejeniyar da aka kulla zaben shugaban kasa na 2023 ya shude.

Jam’iyyar ta lura cewa Kwankwaso, dan takarar shugaban kasa na NNPP na 2023, da wasu ‘yan kungiyar Kwankwasiya sun ci gaba da ficewa daga cikin jam’iyyar saboda cin amanan jam’iyyar.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

“Har yanzu muna mamakin cewa wani mutum mai matsayi kamar na Kwankwaso zai nace wajen sace jam’iyyar da ta ba shi takara a zaben shugaban kasa na 2023 kyauta.”

NNPP ta bayyana cewa INEC dole ne ta cika nauyin da ke kansa ta hanyar bin dokokin kotu da kuma saka sahihan shugabannin jam’iyyar a adireshinta na intanet.

“Babbar kotun ta Jihar Abiya da babbar kotu a Abuja sun tabbatar da hana Kwankwaso da kungiyarsa daga shiga tsarin dimokuradiyya na cikin gida na NNPP kuma idan ya saba za a ladabtar da shi.

Abun bakin ciki ne cewa ana iya ganin Kwankwaso yana gudanar da kansa cikin rashin girmamawa ta hanyar kin bin hukuncin kotu da kuma karya doka.

“Shugabancin INEC na baya ya gaza mana, kuma muna fatan cewa shugabanci na yanzu zai nisanci rashin biyayya ga bin doka da oda na al’umma.

“Har yanzu muna mamakin dalilin da ya sa INEC ba ta mayar da martani ga wasikunmu da ke bukatar a mutunta bin hukuncin kotuna ba.

“A matsayinta na mai yanke hukunci, bai kata INEC ta ci gaba da zura ido kan al’amurar da ke bukatar hukunci cikin gaggawa ba da suka shafi zaman lafiyar al’umma.”

A cewar jam’iyyar, INEC tana da masaniya game da hukuncin kotu, duk da haka, tana mai da hankali ga kungiyoyin da ke son haddasa rikici a cikin dimokuracdiyyar Nijeriya.

“Mun rubuta wasiku da dama zuwa INEC kan wadannan lamarin, duk da haka, hukumar ta yi burus wanda hakn yana karfafa rashin biyayya ga dokokin Nijeriya.

“A karkashin irin wannan yanayi, za mu ci gaba da kiyaye zaman lafiya ga al’umma kuma mun umurci ‘yan jam’iyyarmu su yi watsi da taruka da zaben shugabannin jam’iyyar na bogi.

“Muna kara kira ga INEC ta taimaka wa dimokiradiyya tare da ceto Nijeriya. Ajandar sabon fata ta gwamnatin tarayya a yanzu za ta iya samun nasara ne kawai idan ana bin dokoki kuma ana girmama su”.

Kwankwaso
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • Sulaiman
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • Sulaiman
    Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
  • Sulaiman
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

MASU ALAKA

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
Tambarin Dimokuradiyya

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

June 19, 2026
2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

June 12, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
Tambarin Dimokuradiyya

Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

June 12, 2026
Next Post
Furucin Takaichi Game Da Taiwan Ya Aike Da Mummunan Sako Ga ’Yan Awaren Yankin

Furucin Takaichi Game Da Taiwan Ya Aike Da Mummunan Sako Ga ’Yan Awaren Yankin

LABARAI MASU NASABA

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.