ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NNPP Ta Buƙaci INEC Ta Yi Watsi Da Tarukan Jam’iyyar Da Kwankwaso Zai Jagoranta

by Sulaiman
6 months ago
Kwankwaso

Jam’iyyar NNPP ta bukaci hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) da ‘yan Nijeriya da su yi watsi da tarukan jam’iyya da ake ikirarin jagoran Kwankwasiyya, Sanata Rabiu Kwankwaso zai jagoranta, inda ta bayyana cewa tarukan sun sab awa doka.

A cikin wata sanarwa da sakataren jam’iyyar na kasa, Mista Ogini Olaposi, ya fitar, jam’iyyar ta bayyana cewa kotu ta umurci NNPP ta gudanar da tarukanta na kasa kuma an kammala su.

  • Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina
  • Shekara 25 Da Kafa ACF: Nasarori, Matsaloli Da Ƙalubale

Kamfanin dillancin labarai na Nijeriya ya ruwaito cewa Kwankwaso ya aika da wasika ga INEC, yana sanar da hukumar game da shirin gudanar da sabbin tarukan jam’iyya NNPP, daga 25 ga Nuwamba, zuwa Janairu 2026.

ADVERTISEMENT

Jam’iyyar ta bayyana cewa kungiyar Kwankwasiyya ba za ta iya gudanar da babban taron jam’iyya a madadinta ba, saboda yarjejeniyar da aka kulla zaben shugaban kasa na 2023 ya shude.

Jam’iyyar ta lura cewa Kwankwaso, dan takarar shugaban kasa na NNPP na 2023, da wasu ‘yan kungiyar Kwankwasiya sun ci gaba da ficewa daga cikin jam’iyyar saboda cin amanan jam’iyyar.

LABARAI MASU NASABA

2027: Rashin Hadin Kan Atiku Da Obi Da Kwankwaso Na Iya Taimaka Wa Tazarcen Tinubu

Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya Sun Shiga Rudani A Yayin Da Wa’adin Mika Sunayen Mambobi Ya Shude

“Har yanzu muna mamakin cewa wani mutum mai matsayi kamar na Kwankwaso zai nace wajen sace jam’iyyar da ta ba shi takara a zaben shugaban kasa na 2023 kyauta.”

NNPP ta bayyana cewa INEC dole ne ta cika nauyin da ke kansa ta hanyar bin dokokin kotu da kuma saka sahihan shugabannin jam’iyyar a adireshinta na intanet.

“Babbar kotun ta Jihar Abiya da babbar kotu a Abuja sun tabbatar da hana Kwankwaso da kungiyarsa daga shiga tsarin dimokuradiyya na cikin gida na NNPP kuma idan ya saba za a ladabtar da shi.

Abun bakin ciki ne cewa ana iya ganin Kwankwaso yana gudanar da kansa cikin rashin girmamawa ta hanyar kin bin hukuncin kotu da kuma karya doka.

“Shugabancin INEC na baya ya gaza mana, kuma muna fatan cewa shugabanci na yanzu zai nisanci rashin biyayya ga bin doka da oda na al’umma.

“Har yanzu muna mamakin dalilin da ya sa INEC ba ta mayar da martani ga wasikunmu da ke bukatar a mutunta bin hukuncin kotuna ba.

“A matsayinta na mai yanke hukunci, bai kata INEC ta ci gaba da zura ido kan al’amurar da ke bukatar hukunci cikin gaggawa ba da suka shafi zaman lafiyar al’umma.”

A cewar jam’iyyar, INEC tana da masaniya game da hukuncin kotu, duk da haka, tana mai da hankali ga kungiyoyin da ke son haddasa rikici a cikin dimokuracdiyyar Nijeriya.

“Mun rubuta wasiku da dama zuwa INEC kan wadannan lamarin, duk da haka, hukumar ta yi burus wanda hakn yana karfafa rashin biyayya ga dokokin Nijeriya.

“A karkashin irin wannan yanayi, za mu ci gaba da kiyaye zaman lafiya ga al’umma kuma mun umurci ‘yan jam’iyyarmu su yi watsi da taruka da zaben shugabannin jam’iyyar na bogi.

“Muna kara kira ga INEC ta taimaka wa dimokiradiyya tare da ceto Nijeriya. Ajandar sabon fata ta gwamnatin tarayya a yanzu za ta iya samun nasara ne kawai idan ana bin dokoki kuma ana girmama su”.

Kwankwaso
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya
  • Sulaiman
    Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina
  • Sulaiman
    Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
  • Sulaiman
    Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

MASU ALAKA

Kwankwaso
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Rashin Hadin Kan Atiku Da Obi Da Kwankwaso Na Iya Taimaka Wa Tazarcen Tinubu

May 16, 2026
Adawa
Tambarin Dimokuradiyya

Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya Sun Shiga Rudani A Yayin Da Wa’adin Mika Sunayen Mambobi Ya Shude

May 15, 2026
Abincin Da Ya Kamata Ku Ci Lokacin Al’ada
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Hadakar ‘Yan Adawa Ta Rushe Yayin Da Tikitin Takarar Shugaban Kasa Ya Raba Kan Shugabannin ADC

May 9, 2026
Next Post
Furucin Takaichi Game Da Taiwan Ya Aike Da Mummunan Sako Ga ’Yan Awaren Yankin

Furucin Takaichi Game Da Taiwan Ya Aike Da Mummunan Sako Ga ’Yan Awaren Yankin

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.