ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Adawa Sun Yi Gargadi Kan Barazanar Dakile Dimokuradiyya Mai Jam’iyyu Da Dama

by Yusuf Shuaibu
6 months ago
Gargadi

Hadakar shugabannin ‘yan adawa sun zargi gwamnatin tarayya da amfani da hukumomin yaki da cin hanci da rashawa wajen tsoratarwa da tsangwama ga ‘yan adawa, suna gargadin cewa wannan yanayi yana kawo barazana mai tsanani ga dimokuradiyya mai jam’iyyu da dama a Nijeriya.

A cikin wata sanarwa da suka fitar, shugabannin sun zargi gwamnatin Shugaba kasa Bola Tinubu da amfani da hukumomin gwamnati a matsayin makami, musamman hukumar yaki da cin hanci da rashawa da ‘yansanda da kuma hukumar yaki da safararar haramtattun kudade, don tursasa wa ‘yan adawan siyasa a karkashin jagorancin yaki da rashawa.

  • Wang Yi Ya Zanta Da Ministocin Wajen Cambodia Da Thailand 
  • Gwamnan Zamfara Ya Naɗa Farfesa Ibrahim Tsafe A Matsayin Sabon Shugaban Jami’ar ZAMSUT

Bayanin ya kasance na hadin gwiwa ne da ya hada da tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar da tsohon shugaban majalisar dattawa kuma shugaban jam’iyyar ADC, Sanata Dabid Mark da tsohon dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar LP, Mista Peter Obi da tsohon gwamnan Jihar Edo, Babban John Odigie-Oyegun da tsohon mataimakin shugaban jam’iyyar PDP na yankin kudu, Babban Olabode George da kuma tsohon karamin ministan harkokin tsaro, Lawal Batagarawa.

ADVERTISEMENT

“Yan Nijeriya sun shaida abin da yake faruwa yanzu a matsayin wata manufa ta boye, wadda ba ta bi tsarin dimokuradiyya ba, don tabbatar da cewa dukkan gwamnatocin jihohi suna karkashin ikon jam’iyyar shugaban kasa, ana hanyar tsoratar da gwamnonin adawa a boye ta hanyar yaki da cin hanci da rashawa har sai sun mika wuya kuma sun karkata daga ra’ayisu.

“Kwanan nan wasu gwamnonin adawa da suka koma jam’iyyar gwamnati sun karfafa zargin da jama’a suke yi na matsin lamba na siyasa ba tare da tunani ko neman shawarwarin mutum ba, wannan lamari ya saba wa tsarin dimokuradiyya.

LABARAI MASU NASABA

2027: Rashin Hadin Kan Atiku Da Obi Da Kwankwaso Na Iya Taimaka Wa Tazarcen Tinubu

Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya Sun Shiga Rudani A Yayin Da Wa’adin Mika Sunayen Mambobi Ya Shude

“Wannan tsarin ya kasace wani bangare ne na babban farmaki wanda ba wai kawai ga shugabannin da aka zaba ba har da manyan jiga-jigan ‘yan adawa da ake ganin sune masu tsara sabbin hadin kai kafin zaben shekarar 2027.

“Dole ne mu fadadar kan wannan mummunan aikin, idan aka bar shi ya ci gaba ba tare da kulawa ba, yana da hadari sosai ga makomar dimokuradiyyar Nijeriya,” in ji sanarwar.

Shugabannin sun kara zargin cewa hukumomi da ke yaki da cin hanci da rashawa sun aikinsu ne kadai a kan ‘yan adawa, suna yi ikirarin cewa ana yawan watsi da tuhumar da ake yi wa mambobin jam’iyyar gwamnati, yayin da ake matsa lamba sosai kan tuhumar da ake yi wa ‘yan adawa har ma a gabatar da su a kafafen watsa labarai.

Sun ce maganganun da aka yi a baya na cewa tsohon shugaban jam’iyya mai mulki, Adams Oshiomhole, ya ce “dazarar ka shiga APC, an gafarta maka dukkan zunubanka,” wanda suka ce ya zama alamar yadda jama’a ke kallon rashin daidaito wajen amfani da dokokin yaki da cin hanci da rashawa a Nijeriya.

Sun kara da cewa, “Wasu ‘yan misalai na baya-bayan nan sun kara tabbatar da wannan lamari. Watanni da suka gabata, an samu wata minista cikin wani al’amari na almundahanan kudade wanda har sai da ta kai fushin al’umma ya tilasta masa yin murabus.

“Duk da haka, bayan ta sauka daga mukaminta, ba a taba tuhuma ko gurfanar da ita a gaban EFCC ba, kuma yanzu tana shiga cikin yakin neman zaben shugaban kasa karo na biyu.

“Haka kuma, wani minista ya ci gaba da rike mukaminsa duk da cewa jami’ar da ya ce ya yi karatu sun musunta hakan, inda suka musanta takardar shaidar karatunsa a fili. Shi ma ya yi murabus ne kawai bayan matsin lamba daga jama’a. Watanni bayan haka, ba a shigar da kara a kansa ba.

“Wannan aikin na musguna wa ‘yan adawa yana rage ingancin yunkurin yaki da cin hanci da rashawa kuma yana keta amincin jama’a ga hukumomin kasa,” sanarwar ta kara da cewa.

A matsayin wani bangare na bukatunsu, shugabannin jam’iyyun adawa sun yi kira ga babban lauyan gwamatin tarayya, tare da tuntubar majalisar kasa da su kafa wata hukumar bincike mai zaman kanta don duba asusun gwamnatin tarayya da jihohi da kananan hukumomi daga shekarar 2015 zuwa 2025.

Sun ce akwai bukatar hukumar da aka ba da shawarar ta sami cikakken damar shiga bayanan kudi na jama’a, ta wallafa bincikenta, ta bayyana tsarin tuhuma da shawarwari na gyara don karfafa EFCC.

Shugaban ‘yan adawa sun kuma ba da shawarar saka jami’an yaki da cin hanci da rashawa kai tsaye cikin tsarin biyan kudi da kashe kudaden gwamnati a dukkan matakan gwamnati maimakon kawai hukunta ta tsaya kan kamawa masu laifuka.

Sun yi kira ga ‘yan Nijeriya su kare dimokiradiyya, masu sanya hannu sun ce a makwannin masu zuwa, za su tattauna da abokan hulda na kasashen waje, ofisoshin jakadanci da kungiyoyin duniya don bayyana damuwa kan abin da suka bayyana a matsayin karuwa cusa siyasa a hukumomin yaki da cin hanci na Nijeriya.

A ranar Asabar, ADC ta zargi hukumar yaki da cin hanci da rashawa kan saka siyasa da batun soke belin da aka bai wa tsohon ministan shari’a, Abubakar Malami.

Sai dai a ranar Asabar, hukumar ta ce an bai wa Malami belin tun a ranar 28 ga Nuwamba, 2025, amma ya kasa bin sharuddan belin duk da an ba shi karin lokaci bisa dalilan lafiya.

EFCC ta ce an sake gayyatar Malami a karshe a ranar 8 ga Disamba, 2025, kuma an tsare shi har sai ya cika dukkan sharuddan belin da aka gindaya masa.

Gargadi
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Masana Tattalin Arziki Sun Yi Watsi Da Rahoton NBS Kan Tattalin Arziki
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Alƙawarin Wa’adi Ɗaya Na Peter Obi Ya Raba Kawunan Ƴan Arewa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    ‘Yan Majalisar Wakilai 50 Da Suka Rasa Tikitin Takara A Zaɓen Fid Da Gwani Na APC
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Zaɓen Fitar Da Gwani: APC Na Fuskantar Barazanar Tawaye

MASU ALAKA

Gargadi
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Rashin Hadin Kan Atiku Da Obi Da Kwankwaso Na Iya Taimaka Wa Tazarcen Tinubu

May 16, 2026
Adawa
Tambarin Dimokuradiyya

Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya Sun Shiga Rudani A Yayin Da Wa’adin Mika Sunayen Mambobi Ya Shude

May 15, 2026
Abincin Da Ya Kamata Ku Ci Lokacin Al’ada
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Hadakar ‘Yan Adawa Ta Rushe Yayin Da Tikitin Takarar Shugaban Kasa Ya Raba Kan Shugabannin ADC

May 9, 2026
Next Post
Yawan Jarin Waje Da Kasar Sin Ta Yi Amfani Da Shi A Watan Nuwamban Bana Ya Karu Da Kaso 26.1%

Yawan Jarin Waje Da Kasar Sin Ta Yi Amfani Da Shi A Watan Nuwamban Bana Ya Karu Da Kaso 26.1%

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.