ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, July 27, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Adawa Sun Yi Gargadi Kan Barazanar Dakile Dimokuradiyya Mai Jam’iyyu Da Dama

by Yusuf Shuaibu
7 months ago
Gargadi

Hadakar shugabannin ‘yan adawa sun zargi gwamnatin tarayya da amfani da hukumomin yaki da cin hanci da rashawa wajen tsoratarwa da tsangwama ga ‘yan adawa, suna gargadin cewa wannan yanayi yana kawo barazana mai tsanani ga dimokuradiyya mai jam’iyyu da dama a Nijeriya.

A cikin wata sanarwa da suka fitar, shugabannin sun zargi gwamnatin Shugaba kasa Bola Tinubu da amfani da hukumomin gwamnati a matsayin makami, musamman hukumar yaki da cin hanci da rashawa da ‘yansanda da kuma hukumar yaki da safararar haramtattun kudade, don tursasa wa ‘yan adawan siyasa a karkashin jagorancin yaki da rashawa.

  • Wang Yi Ya Zanta Da Ministocin Wajen Cambodia Da Thailand 
  • Gwamnan Zamfara Ya Naɗa Farfesa Ibrahim Tsafe A Matsayin Sabon Shugaban Jami’ar ZAMSUT

Bayanin ya kasance na hadin gwiwa ne da ya hada da tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar da tsohon shugaban majalisar dattawa kuma shugaban jam’iyyar ADC, Sanata Dabid Mark da tsohon dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar LP, Mista Peter Obi da tsohon gwamnan Jihar Edo, Babban John Odigie-Oyegun da tsohon mataimakin shugaban jam’iyyar PDP na yankin kudu, Babban Olabode George da kuma tsohon karamin ministan harkokin tsaro, Lawal Batagarawa.

ADVERTISEMENT

“Yan Nijeriya sun shaida abin da yake faruwa yanzu a matsayin wata manufa ta boye, wadda ba ta bi tsarin dimokuradiyya ba, don tabbatar da cewa dukkan gwamnatocin jihohi suna karkashin ikon jam’iyyar shugaban kasa, ana hanyar tsoratar da gwamnonin adawa a boye ta hanyar yaki da cin hanci da rashawa har sai sun mika wuya kuma sun karkata daga ra’ayisu.

“Kwanan nan wasu gwamnonin adawa da suka koma jam’iyyar gwamnati sun karfafa zargin da jama’a suke yi na matsin lamba na siyasa ba tare da tunani ko neman shawarwarin mutum ba, wannan lamari ya saba wa tsarin dimokuradiyya.

LABARAI MASU NASABA

Manufofin Tattalin Arzikin Gwamnatin Tinubu Sun Lalata Rayukan Al’ummar Nijeriya —ADC

Jadawalin INEC:Kotun Daukaka Kara Ta Kassara Fatan Jam’iyyu Da ‘Yan Siyasa

“Wannan tsarin ya kasace wani bangare ne na babban farmaki wanda ba wai kawai ga shugabannin da aka zaba ba har da manyan jiga-jigan ‘yan adawa da ake ganin sune masu tsara sabbin hadin kai kafin zaben shekarar 2027.

“Dole ne mu fadadar kan wannan mummunan aikin, idan aka bar shi ya ci gaba ba tare da kulawa ba, yana da hadari sosai ga makomar dimokuradiyyar Nijeriya,” in ji sanarwar.

Shugabannin sun kara zargin cewa hukumomi da ke yaki da cin hanci da rashawa sun aikinsu ne kadai a kan ‘yan adawa, suna yi ikirarin cewa ana yawan watsi da tuhumar da ake yi wa mambobin jam’iyyar gwamnati, yayin da ake matsa lamba sosai kan tuhumar da ake yi wa ‘yan adawa har ma a gabatar da su a kafafen watsa labarai.

Sun ce maganganun da aka yi a baya na cewa tsohon shugaban jam’iyya mai mulki, Adams Oshiomhole, ya ce “dazarar ka shiga APC, an gafarta maka dukkan zunubanka,” wanda suka ce ya zama alamar yadda jama’a ke kallon rashin daidaito wajen amfani da dokokin yaki da cin hanci da rashawa a Nijeriya.

Sun kara da cewa, “Wasu ‘yan misalai na baya-bayan nan sun kara tabbatar da wannan lamari. Watanni da suka gabata, an samu wata minista cikin wani al’amari na almundahanan kudade wanda har sai da ta kai fushin al’umma ya tilasta masa yin murabus.

“Duk da haka, bayan ta sauka daga mukaminta, ba a taba tuhuma ko gurfanar da ita a gaban EFCC ba, kuma yanzu tana shiga cikin yakin neman zaben shugaban kasa karo na biyu.

“Haka kuma, wani minista ya ci gaba da rike mukaminsa duk da cewa jami’ar da ya ce ya yi karatu sun musunta hakan, inda suka musanta takardar shaidar karatunsa a fili. Shi ma ya yi murabus ne kawai bayan matsin lamba daga jama’a. Watanni bayan haka, ba a shigar da kara a kansa ba.

“Wannan aikin na musguna wa ‘yan adawa yana rage ingancin yunkurin yaki da cin hanci da rashawa kuma yana keta amincin jama’a ga hukumomin kasa,” sanarwar ta kara da cewa.

A matsayin wani bangare na bukatunsu, shugabannin jam’iyyun adawa sun yi kira ga babban lauyan gwamatin tarayya, tare da tuntubar majalisar kasa da su kafa wata hukumar bincike mai zaman kanta don duba asusun gwamnatin tarayya da jihohi da kananan hukumomi daga shekarar 2015 zuwa 2025.

Sun ce akwai bukatar hukumar da aka ba da shawarar ta sami cikakken damar shiga bayanan kudi na jama’a, ta wallafa bincikenta, ta bayyana tsarin tuhuma da shawarwari na gyara don karfafa EFCC.

Shugaban ‘yan adawa sun kuma ba da shawarar saka jami’an yaki da cin hanci da rashawa kai tsaye cikin tsarin biyan kudi da kashe kudaden gwamnati a dukkan matakan gwamnati maimakon kawai hukunta ta tsaya kan kamawa masu laifuka.

Sun yi kira ga ‘yan Nijeriya su kare dimokiradiyya, masu sanya hannu sun ce a makwannin masu zuwa, za su tattauna da abokan hulda na kasashen waje, ofisoshin jakadanci da kungiyoyin duniya don bayyana damuwa kan abin da suka bayyana a matsayin karuwa cusa siyasa a hukumomin yaki da cin hanci na Nijeriya.

A ranar Asabar, ADC ta zargi hukumar yaki da cin hanci da rashawa kan saka siyasa da batun soke belin da aka bai wa tsohon ministan shari’a, Abubakar Malami.

Sai dai a ranar Asabar, hukumar ta ce an bai wa Malami belin tun a ranar 28 ga Nuwamba, 2025, amma ya kasa bin sharuddan belin duk da an ba shi karin lokaci bisa dalilan lafiya.

EFCC ta ce an sake gayyatar Malami a karshe a ranar 8 ga Disamba, 2025, kuma an tsare shi har sai ya cika dukkan sharuddan belin da aka gindaya masa.

Gargadi
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Manufofin Tattalin Arzikin Gwamnatin Tinubu Sun Lalata Rayukan Al’ummar Nijeriya —ADC
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Jadawalin INEC:Kotun Daukaka Kara Ta Kassara Fatan Jam’iyyu Da ‘Yan Siyasa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Tinubu Da Atiku Da Obi Na Ci Gaba Da Zafafa Neman Kuri’un Arewacin Nijeriya
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Zaben 2027:Tikitin Muslim-muslim Na Jam’iyyar APC Ya Sake Tayar Da Kura

MASU ALAKA

Manufofin Tattalin Arzikin Gwamnatin Tinubu Sun Lalata Rayukan Al’ummar Nijeriya —ADC
Tambarin Dimokuradiyya

Manufofin Tattalin Arzikin Gwamnatin Tinubu Sun Lalata Rayukan Al’ummar Nijeriya —ADC

July 25, 2026
Jadawalin INEC:Kotun Daukaka Kara Ta Kassara Fatan Jam’iyyu Da ‘Yan Siyasa
Tambarin Dimokuradiyya

Jadawalin INEC:Kotun Daukaka Kara Ta Kassara Fatan Jam’iyyu Da ‘Yan Siyasa

July 24, 2026
Tinubu Da Atiku Da Obi Na Ci Gaba Da Zafafa Neman Kuri’un Arewacin Nijeriya
Tambarin Dimokuradiyya

Tinubu Da Atiku Da Obi Na Ci Gaba Da Zafafa Neman Kuri’un Arewacin Nijeriya

July 17, 2026
Next Post
Yawan Jarin Waje Da Kasar Sin Ta Yi Amfani Da Shi A Watan Nuwamban Bana Ya Karu Da Kaso 26.1%

Yawan Jarin Waje Da Kasar Sin Ta Yi Amfani Da Shi A Watan Nuwamban Bana Ya Karu Da Kaso 26.1%

LABARAI MASU NASABA

Auto Draft

ADC Ta Buƙaci Tinubu Ya Bai Wa Waɗanda Aka Sace A Kaiama Da Borno Kulawa

July 27, 2026
Gargadi

Sojojin Ruwa Sun Cafke Jirgin Ruwa Maƙare Da Ɗanyen Mai Na Sata

July 26, 2026
Sin Za Ta Ci Gaba Da Kare Ikon Mulkin Yankuna Da Hakkoki Da Moriyarta Ta Teku

Sin Za Ta Ci Gaba Da Kare Ikon Mulkin Yankuna Da Hakkoki Da Moriyarta Ta Teku

July 26, 2026
Xi Jinping Ya Mika Sakon Murnar Cika Shekaru 61 Da Samun ‘Yancin Kai Ga Shugaban Maldives

Xi Jinping Ya Mika Sakon Murnar Cika Shekaru 61 Da Samun ‘Yancin Kai Ga Shugaban Maldives

July 26, 2026
Gargadi

Shugaban Ƙasa Tinubu Ya Naɗa Sabon Mai Ba Shi Shawara

July 26, 2026
Sin Ta Ayyana Shirin Ko-ta-kwana Na Samar Da Tallafin Gaggawa Ga Lardin Guangdong

Sin Ta Ayyana Shirin Ko-ta-kwana Na Samar Da Tallafin Gaggawa Ga Lardin Guangdong

July 26, 2026
Fina-finan Kasar Sin Suna Haskakawa Tare Da Samar Da Dimbin Kudaden Shiga A Zangon Nuna Fina-finai Na Lokacin Zafi Na Bana

Fina-finan Kasar Sin Suna Haskakawa Tare Da Samar Da Dimbin Kudaden Shiga A Zangon Nuna Fina-finai Na Lokacin Zafi Na Bana

July 26, 2026
Shugaban Senegal Ya Jinjinawa Kasar Sin Bisa Taimakon Gina Zaurukan Gudanar Da Wasannin Gasar Olympics Ta Matasa

Shugaban Senegal Ya Jinjinawa Kasar Sin Bisa Taimakon Gina Zaurukan Gudanar Da Wasannin Gasar Olympics Ta Matasa

July 26, 2026
Gargadi

Ƴan Bindiga Sun Yi Garkuwa Da Alƙalin Babbar Kotu A Kebbi

July 26, 2026
Bala Mohammed

Sadakin Budurwa ₦3,000 Na Bazawara ₦1,500: Gwamnatin Bauchi Ta Ƙaryata Batun

July 26, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.