• English
  • Business News
Saturday, September 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2027: Masu Neman Takarar Shugaban Kasa A PDP Sun Kara Matsa Kaimi Bayan Ficewar Atiku

by Yusuf Shuaibu and Sulaiman
2 months ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Jam’iyyar PDP Ta Janye Daga Shiga Zaɓen Ƙananan Hukumomi A Kebbi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwagwarmayar neman takarar shugaban kasa a jam’yyar PDP a 2027 ta kara kaimi tun bayan da tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya fice daga jam’iyyar, wanda ta bude hanya ga gwamnan Jihar Oyo, Seyi Makinde, gwamnan Jihar Bauchi, Bala Mohammed, da sauran masu sha’awar neman takarar shugaban kasa da ke neman kalubalantar tazarcen Shugaban kasa Bola Tinubu.

Masu ruwa da tsaki na PDP, wadanda suka yi jawabi kan lamarin cikin sirri, sun tabbatar da cewa burin tsayawa takarar shugabancin kasar na Makinde da Bala ya kasance sanannen abu a tsakanin muhimman masu ruwa da tsaki na jam’iyyar.

  • Gwamnan Jigawa Ya Rattaba Hannu Kan Kudirin Dokar Tabbatar Da Hisbah
  • Matsalar Tsaro: Sarakuna Sun Bukaci Gwamnati Ta Canza Salo

Wata majiya mai tushe daga jam’iyyar ta bayyana cewa PDP ta bude kofa ga duk masu neman takarar shugaban kasa bisa bin dokokin jam’iyyar.

Yayin da babban jigon jam’iyyar PDP, Cif Bode George, ya tabbatar a cikin wani tattaunawa ta musamman cewa, ana ci gaba da kokarin samun dan takarar shugaban kasa daga kudu, sauran mambobin kwamitin zartarwa na kasa sun bayyana ra’ayi daban-daban kan batun tsarin karba-karba na yankuna.

A daidai lokacin da PDP ke fama da rikicin cikin gida da suka hada da na shugabanci da batun tsarin karba-karba a tsakanin yankuna wanda jam’iyyar ke kokarin warwarewa kafin zaben 2027.

Labarai Masu Nasaba

Rudani Ya Kunno Kai Yayin Da INEC Ta Ki Amincewa Da Shugabancin ADC

‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido

Kwanan nan jam’iyyar PDP ta gudanar da taron kwamitin zartarwa karo na 100 da aka gudanar ranar 30 ga Yuni, PDP ta warware rikicin da ya dade yana ci mata tuwo a kwarya na batun mukamin sakataren jam’iyyar na kasa wanda ta tabbatar da Sanata Samuel Anyanwu a matsayin sakataren jam’iyyar.

Duk da wannan warware batun, Atiku da wasu magoya bayansa sun fice daga jam’iyyar sakamakon rashin warware rikicin gida na jam’iyyar.

A ranar 1 ga Yuli, Atiku da Peter Obi da Rotimi Amaechi da Nasir El-Rufai, da wasu sun kulla hadaka a karkashin jam’iyyar ADC, sun ce sun yi wannan hadakar ne domin kalubalantar APC a zaben 2027.

A matsayin wani bangare na wannan yunkurin hadin gwiwa, sun nada tsohon shugaban majalisar dattawa, Dabid Mark a matsayin shugaban jam’iyyar na kasa na wucin gadi da tsohon gwamnan Jihar Osun, Rauf Aregbesola a matsayin sakataren jam’iyyar na kasa na wucin gadi.

Majiya mai tushe ta tabbatar da cewa Makinde da Bala Mohammed su ne manyan ‘yan takarar shugaban kasa a jam’iyyar a yanzu haka, yayin da ake sa ran wasu jiga-jigan jam’iyyar za su biyo baya kafin zaben 2027.

Majiyar ta ce, “Ana tambayar game da wadanda suka nuna sha’awarsu na neman tikitin takarar shugaban kasa a jam’iyya a halin yanzu. Duk da dai ba su fito fili sun bayyana ba, mun ji daga wurin shugabannin jam’iyyar, cewa Makinde da Bala Mohammed har ma da wasu tsoffin gwamnonin daga Kudu suna da sha’awar neman tikitin shugaban kasa jam’iyyar PDP a 2027.

“Amma a hakikanin gaskiya, a yanzu haka ba za mu iya sanin adadin wadanda suke sha’awar tsayawa takarar shugaban kasa a PDP, sai idan lokaci ya yi duk za a san su. Don haka, jam’iyyar PDP ta bude kofarta ga kowa, kuma ta kasance jam’iyyar da ke da karbuwa sosai a tsakanin ‘yan Nijeriya.”

Wani jigo a jam’iyyar wanda ya nemi a Sakaye sunansa don ba a shi izinin yin magana a hukumance ba, ya goyi bayan bude tikitin takarar shugaban kasa a PDP a 2027 ga dukkan ‘yan Nijeriya.

Shi kuwa, tsohon mataimakin shugaban PDP na yankin kudu maso yammaci, Eddy Olafeso, ya bayyana cewa shugabannin jam’iyyar sun dauki darashi ga abubuwan da suka faru a baya.

Yayin da tsohon sakataren jam’iyyar na kasa, Ibrahim Tsauri, ya shawarci mambobin jam’iyyar cewa su bar uwar jam’iyyar ta yanke hukunci, sannan kuma ya yi gargadi kan kauce wa bin tsarin karba-karba.

A nasa martanin, daraktan yada labarai na jam’iyyar APC, Bala Ibrahim ya ce Shugaban Tinubu zai kayar da Makinde, Bala Mohammed, ko wani dan takarar da PDP ta tsaida a 2027.

Ibrahim ya bayyana cewa, “Makinde da Bala Mohammed ba su da wata gogewa a matakin kasa na siyasar Nijeriya. Wadannan gwamnonin biyu ba za su iya jure fafatawar siyasar kasa nan ba. Ba su da gogewar da dan takararmu yake da shi.

“Mutane da ka ambata ba su da ikon doke shugaban kasa a kowanne fanni na siyasa. Wannan ba matsala ce da za ta ba mu ciwon kai ba. Koma dai wane yanki PDP zai fitar da dan takarar shugaban kasa ba zai yi nasara ba a 2027.”

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Xi Jinping Ya Karbi Takardun Nadi Daga Sabbin Jakadun Kasashen Waje

Next Post

Binciken Jin Raayoyi Na CGTN: Duniya Ta Saba Da “Kauracewar” Amurka

Related

Fursunoni Ba Za Su Samu Damar Kada Kuri’a Ba A Zaben 2023 – INEC
Tambarin Dimokuradiyya

Rudani Ya Kunno Kai Yayin Da INEC Ta Ki Amincewa Da Shugabancin ADC

7 days ago
‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido

1 week ago
Daraktoci Da Jami’an FCT 7 Na Fuskantar Tuhume-tuhume Kan Badakar Fili
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Idan Kana Son Tarwatsa PDP, To Ka Dawo Da Peter Obi – Wike

1 week ago
ADC Ta Bukaci Tinubu Ya Kafa Dokar Ta Baci A Katsina Da Zamfara Kan Rashin Tsaro
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ta Bukaci Tinubu Ya Kafa Dokar Ta Baci A Katsina Da Zamfara Kan Rashin Tsaro

2 weeks ago
katin zabe
Tambarin Dimokuradiyya

INEC Ta Bayyana Damuwarta Kan Katunan Zabe 360,000 Da Ba A Karba Ba A Kano

2 weeks ago
Jam’iyyar PDP Ta Janye Daga Shiga Zaɓen Ƙananan Hukumomi A Kebbi
Tambarin Dimokuradiyya

Shugabannin PDP Sun Shiga Dimuwa Yayin Da APC Ke Zawarcin Wasu Gwamnoninsu

2 weeks ago
Next Post
Binciken Jin Raayoyi Na CGTN: Duniya Ta Saba Da “Kauracewar” Amurka

Binciken Jin Raayoyi Na CGTN: Duniya Ta Saba Da "Kauracewar" Amurka

LABARAI MASU NASABA

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido Ba

September 13, 2025
Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

September 12, 2025
Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

September 12, 2025
Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

September 12, 2025
Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

September 12, 2025
Shugaban Ghana: Manufar Soke Biyan Harajin Kwastam Ta Kasar Sin Ta Ba Da Damammaki Ga Afirka

Shugaban Ghana: Manufar Soke Biyan Harajin Kwastam Ta Kasar Sin Ta Ba Da Damammaki Ga Afirka

September 12, 2025
Gwamna Lawal Ya Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa Da Sama Da Naira Biliyan Ɗaya

Gwamna Lawal Ya Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa Da Sama Da Naira Biliyan Ɗaya

September 12, 2025
Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

September 12, 2025
Yawan Yarjejeniyar Zuba Jari Da Aka Kulla a CIFIT Ya Kai 1154

Yawan Yarjejeniyar Zuba Jari Da Aka Kulla a CIFIT Ya Kai 1154

September 12, 2025
Korafin Philippines Ya Tabbatar Da Halascin Matakan Da Sin Ke Dauka Na Kare Muhalli a Tsibirin Huangyan

Korafin Philippines Ya Tabbatar Da Halascin Matakan Da Sin Ke Dauka Na Kare Muhalli a Tsibirin Huangyan

September 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.