ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 17, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2027: Matsaloli Na Barazana Ga Kawancen Jam’iyyun Adawa 

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
Adawa

Bayan da kotun koli ta zartar da hukunci na tabbatar da nasarar Shugaban kasa, Bola Tinubu a zaben 2023, jam’iyyun adawa sun yi kunkurin shirya kawance domin tunkarar APC a 2027, sai dai kuma matsaloli sun turnuke wannan yukurin na jam’iyyun adawa. 

Amma tambayoyin mai muhimmanci da mutane ke ci gaba da yi ita ce, yadda jam’iyyun adawan za su samu nasarar yin wannan kwance bayan da sun gaza magance matsaloli da yawa kan lamarin.

  • Kungiyar Lauyoyi Ta Tabbatar Da Fara Gurfanar Da Masu Laifukan Zaben 2023
  • Gwamnan Zamfara Ya Kai Ziyarar Ta’aziyya Garin Mada

Jiga-jigan ‘yan siyasa a tsakanin jam’iyyun adawa sun ci gaba da tattaunawa tare da shawartar juna kan kafa kwancen siyasa ta yadda za su sami karfin tunkarar Shugaba Tinubu wanda zai nemi wa’adin mulki na biyu bayan shudewar mulkinsa na farko a 2027.

ADVERTISEMENT

Idan za a iya tunawa dai, an samu irin wannan kwancen siyasa a 2013 lokacin da jam’iyyun CPC, ACN, ANPP, APGA da kuma wani bangare na jam’iyyar PDP suka dunkule wuri daya tare da samar da jam’iyya daya mai suna APC.

Tun a ranar 15 ga Oktoban 2023, dan takarar shugaban kasa karkashin jam’iyyar PDP a 2023, Atiku Abubakar ya yi kira ga daukacin jam’iyyun adawa da ke kasar nan wajen samar da kwancen siyasa domin takatar da APC na yunkurin mayar da Nijeriya karkashin jam’iyya daya. Ya dai bayyana hakan ne lokacin da yake amsar bakwancin mambobin kwamitin zartarwa na cibiyar hadakar jam’iyyu.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027

Ya ce, “Muna ganin yadda jam’iyyar APC tane kara kaimi wajen mayar da Nijeriya tsarin jam’iyya daya. Idan har muka kasa hada kai wajen kalubantar jam’iyya mai mulki, za ta lalata mana dimokuradiyya kuma hakan zai shafi goben yaran da za a haifa nan gaba.”

Bayan haka, jam’iyyun PDP, NNPP, ADC, APM, SDP, YPP, da ZLP sun kafa wata kungiya da suka kira da CCPP bayan ganawa da shugabannin jam’iyyun guda 7 da ya gudana a shalkwatan jam’iyyar SDP da ke Abuja a ranar 6 ga Disambar 2023.

Shugabannin jam’iyyun adawa na ci gaba da sokar gwamnatin Tinubu na cewa ya kawo wasu tsare-tsaren tattalin arziki da suka janyo tsadar rayuwa da fatara da kuma radadin kuncin rayuwa ga ‘yan Nijeriya. Haka kuma sun bayyana damuwarsu kan karuwar rashin tsaro a kasar nan.

Sai dai kuma sakataren jam’iyyar APC na kasa, Felid Morka, ya bukaci ‘yan Nijeriya kar su dauki kawacen jam’iyyun adawa da muhimmanci, su kaance da jam’iyyar APC.

Bincike ya tabbatar da cewa har yanzu ‘yan takarar shugaban kasa na jam’iyya daban-daban da masu ruwa da tsaki na jam’iyyun adawa ba su kammala amincewa da wannan kawancin ba tare da kin yin watsi da akidar jam’iyyunsu. Haka kuma ba su yarda da yi wa wata sabuwar jam’iyya rajista ba.

An bayyana cewa kafin kawancen jam’iyyun adawan ya yuwu, sai dukkan jam’iyyun sun bayar da takardunsu ga hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) kafin su samu damar yi wa sabon jam’iyya rajista.

Ana ganin cewa wannan kawancen na jam’iyyun adawa zai yi wuya saboda akwai bambance-bambancin ra’ayoyi a tsakanin mambobin jam’iyyun.

Masu bincike sun bayana cewa matsalolin da ke barazana ga dorewar kawancen dai sun hada da rikicin cikin gina da rabuwar kai a tsakanin manyan jam’iyyun adawa. Sun kuma bayyana cewa za a samu matsala wajen fitar da dan takara idan har aka samu nasarar yin wannan kawance.

Haka kuma suna ganin cewa wasu manyan ‘yan siyasa masu matukar karfi da ke cikin gwamnatin Tinubu ba za su taba bari wannan kawanci ya samu nasara ba, domin kalubalantarsa a 2027.

2027
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    An Samu Ruɗani Kan Rashin Bayyana Jerin Ƴan Takarar Jam’iyyun Siyasa Na Zaɓen 2027

MASU ALAKA

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan
Manyan Labarai

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

July 15, 2026
Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027
Tambarin Dimokuradiyya

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027

July 11, 2026
Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara
Tambarin Dimokuradiyya

Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

July 11, 2026
Next Post
Damben Boxing: Anthony Joshua Ya Doke Francis Ngannou A Saudi Arabia

Damben Boxing: Anthony Joshua Ya Doke Francis Ngannou A Saudi Arabia

LABARAI MASU NASABA

Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

July 17, 2026
Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

July 17, 2026
Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

July 16, 2026
Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 16, 2026
Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara

Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara

July 16, 2026
Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL

Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL

July 16, 2026
Tasirin Da Sabbin Hare-haren Amurka Da Iran Za Su Iya Haifarwa Duniya

Tasirin Da Sabbin Hare-haren Amurka Da Iran Za Su Iya Haifarwa Duniya

July 16, 2026
Sin Na Kokarin Sanya Ci Gaban Fasaha Ya Inganta Bunkasa Da Wadatar Dan Adam

Sin Na Kokarin Sanya Ci Gaban Fasaha Ya Inganta Bunkasa Da Wadatar Dan Adam

July 16, 2026
Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027

Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027

July 16, 2026
Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Kazakhstan

Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Kazakhstan

July 16, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.