ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2027: Matsaloli Na Barazana Ga Kawancen Jam’iyyun Adawa 

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
Adawa

Bayan da kotun koli ta zartar da hukunci na tabbatar da nasarar Shugaban kasa, Bola Tinubu a zaben 2023, jam’iyyun adawa sun yi kunkurin shirya kawance domin tunkarar APC a 2027, sai dai kuma matsaloli sun turnuke wannan yukurin na jam’iyyun adawa. 

Amma tambayoyin mai muhimmanci da mutane ke ci gaba da yi ita ce, yadda jam’iyyun adawan za su samu nasarar yin wannan kwance bayan da sun gaza magance matsaloli da yawa kan lamarin.

  • Kungiyar Lauyoyi Ta Tabbatar Da Fara Gurfanar Da Masu Laifukan Zaben 2023
  • Gwamnan Zamfara Ya Kai Ziyarar Ta’aziyya Garin Mada

Jiga-jigan ‘yan siyasa a tsakanin jam’iyyun adawa sun ci gaba da tattaunawa tare da shawartar juna kan kafa kwancen siyasa ta yadda za su sami karfin tunkarar Shugaba Tinubu wanda zai nemi wa’adin mulki na biyu bayan shudewar mulkinsa na farko a 2027.

ADVERTISEMENT

Idan za a iya tunawa dai, an samu irin wannan kwancen siyasa a 2013 lokacin da jam’iyyun CPC, ACN, ANPP, APGA da kuma wani bangare na jam’iyyar PDP suka dunkule wuri daya tare da samar da jam’iyya daya mai suna APC.

Tun a ranar 15 ga Oktoban 2023, dan takarar shugaban kasa karkashin jam’iyyar PDP a 2023, Atiku Abubakar ya yi kira ga daukacin jam’iyyun adawa da ke kasar nan wajen samar da kwancen siyasa domin takatar da APC na yunkurin mayar da Nijeriya karkashin jam’iyya daya. Ya dai bayyana hakan ne lokacin da yake amsar bakwancin mambobin kwamitin zartarwa na cibiyar hadakar jam’iyyu.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

Ya ce, “Muna ganin yadda jam’iyyar APC tane kara kaimi wajen mayar da Nijeriya tsarin jam’iyya daya. Idan har muka kasa hada kai wajen kalubantar jam’iyya mai mulki, za ta lalata mana dimokuradiyya kuma hakan zai shafi goben yaran da za a haifa nan gaba.”

Bayan haka, jam’iyyun PDP, NNPP, ADC, APM, SDP, YPP, da ZLP sun kafa wata kungiya da suka kira da CCPP bayan ganawa da shugabannin jam’iyyun guda 7 da ya gudana a shalkwatan jam’iyyar SDP da ke Abuja a ranar 6 ga Disambar 2023.

Shugabannin jam’iyyun adawa na ci gaba da sokar gwamnatin Tinubu na cewa ya kawo wasu tsare-tsaren tattalin arziki da suka janyo tsadar rayuwa da fatara da kuma radadin kuncin rayuwa ga ‘yan Nijeriya. Haka kuma sun bayyana damuwarsu kan karuwar rashin tsaro a kasar nan.

Sai dai kuma sakataren jam’iyyar APC na kasa, Felid Morka, ya bukaci ‘yan Nijeriya kar su dauki kawacen jam’iyyun adawa da muhimmanci, su kaance da jam’iyyar APC.

Bincike ya tabbatar da cewa har yanzu ‘yan takarar shugaban kasa na jam’iyya daban-daban da masu ruwa da tsaki na jam’iyyun adawa ba su kammala amincewa da wannan kawancin ba tare da kin yin watsi da akidar jam’iyyunsu. Haka kuma ba su yarda da yi wa wata sabuwar jam’iyya rajista ba.

An bayyana cewa kafin kawancen jam’iyyun adawan ya yuwu, sai dukkan jam’iyyun sun bayar da takardunsu ga hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) kafin su samu damar yi wa sabon jam’iyya rajista.

Ana ganin cewa wannan kawancen na jam’iyyun adawa zai yi wuya saboda akwai bambance-bambancin ra’ayoyi a tsakanin mambobin jam’iyyun.

Masu bincike sun bayana cewa matsalolin da ke barazana ga dorewar kawancen dai sun hada da rikicin cikin gina da rabuwar kai a tsakanin manyan jam’iyyun adawa. Sun kuma bayyana cewa za a samu matsala wajen fitar da dan takara idan har aka samu nasarar yin wannan kawance.

Haka kuma suna ganin cewa wasu manyan ‘yan siyasa masu matukar karfi da ke cikin gwamnatin Tinubu ba za su taba bari wannan kawanci ya samu nasara ba, domin kalubalantarsa a 2027.

2027
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

MASU ALAKA

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
Tambarin Dimokuradiyya

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

June 19, 2026
2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

June 12, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
Tambarin Dimokuradiyya

Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

June 12, 2026
Next Post
Damben Boxing: Anthony Joshua Ya Doke Francis Ngannou A Saudi Arabia

Damben Boxing: Anthony Joshua Ya Doke Francis Ngannou A Saudi Arabia

LABARAI MASU NASABA

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.