• English
  • Business News
Friday, July 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Haɗewar NILEST Da NARICT Barazana Ce Ga Walwala Da Ayyukan Cibiyoyin’

by Sadiq
1 year ago
in Labarai
0
‘Haɗewar NILEST Da NARICT Barazana Ce Ga Walwala Da Ayyukan Cibiyoyin’
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ƙungiyar masana fasahar fata da na kimiyyar sinadarai ta Nijeriya ta damu matuƙa da haɗewar Cibiyar Fasahar Fata da Kimiyya ta Nijeriya (NILEST) da kuma Cibiyar Bincike Kan kimiyyar Sinadarai (NARICT), inda ta bayyana cewa hakan babbar barazana ce ga jin daɗi da walwalar masu gudanarwa. 

Idan za a iya tunawa batun haɗewar ma’aikatu da hukumomin gwamnati ya zama ruwan dare tun bayan fitar da rahoton Oronsanye game da sauye-sauyen ayyukan gwamnati sama da shekaru goma sha biyu da suka gabata.

  • ‘Yan Bindiga Sun Tarwatsa Kauyuka 10 A Jihar Kaduna
  • Pogba Zai Ɗaukaka Ƙara A Kan Dakatar Da Shi Daga Buga Ƙwallo Na Tsawon Shekaru 4

Ana ɗaukar wannan matakin a matsayin wata dabara da gwamnati ta ɓullo da shi domin rage kuɗaɗen da ƙasa ke kashewa wajen gudanar da ayyukan gwamnati. Sauran dalilan haɗewar sun haɗa da; kawar da tsarin rashin gudanarwa, maimaita ayyuka, kwaikwayo, da sake fasalin ayyukan gwamnati wanda zai inganta yanayin gudanar da ayyuka.

A cikin wata sanarwa da ƙungiyar ta masana fasahar fata da kimiyyar sinadarai ta Nijeriya ta fitar ɗauke da sa hannun shugaban ƙungiyar na ƙasa, Dr. Julius Putshaka, ya ce ya zama wajibi a yi nazari sosai kan illolin da ke tattare da irin wannan haɗewar na wasu hukumomi.

Sanarwar ta ƙara da cewa: “rashin amincewar ƙungiyar masana fasahar fata da na kimiyyar sinadarai ta Nijeriya dangane da haɗewar waɗannan hukumomi ya samo asali ne daga damuwar da ke tattare da yiwuwar tafka asarar ƙwararrun masana saboda waɗannan cibiyoyi suna da hurumi daban-daban.

Labarai Masu Nasaba

A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya

Biyan ‘Yan Fansho Naira Biliyan 22: NUP Da NLC Sun Bukaci A Yi Koyi Da Gwamna Abba

“A yayin da NILEST ke da alhakin gudanar da bincike tare da horar da ma’aikata a fannin fasahar fata da ƙirgi tare da samar da ɗaliban da za su yi wa masana’antar fata hidima da kuma wasu sassa da dama a wasu hukumomin gwamnati, Cibiyar NARICT a ɗaya ɓangaren kuma tana da alhakin gudanar da bincike a cikin albarkatun ƙasa domin samar da sinadarai da za a yi amfani da su wajen aikace-aikacen masana’antu.

“Dole ne a nanata cewa NILEST ta taka muhimmiyar rawa wajen bunƙasa ɓangarori masu muhimmanci a ɓangaren samar da fata da ƙirgi. Tare da cibiyoyi masu gudanar da ayyuka da kuma wasu da aka faɗaɗa ayyukan, ofisoshin cibiyar sun bazu a duk yankuna shida na siyasa na faɗin ƙasar, kuma ta kasance a matsayin jagora ga ‘yan kasuwa masu sana’ar dogaro da kai a masana’antar.

“Cibiyar ta horar da dubban ‘yan kasuwa da masu sana’o’in hannu a faɗin ƙasar nan tare da haɗin gwiwar ƙungiyoyi daban-daban da gwamnatocin jihohi kuma har yanzu tana samar da ƙarin hanyoyin gudanar da irin waɗannan ayyuka.

“Yana da kyau a lura da irin tasirin da wannan cibiya za ta iya yi wajen samar da arziƙi da kuma musayar kuɗaɗen ƙasashen waje ga ƙasar nan ta hanyar samar da ingantattun fata da ƙirgi da za a iya fitar da su zuwa ƙasashen waje a manyan cibiyoyinta da ke Sakkwato, Kano, da Maiduguri.

Kamar dai yadda Cibiyar Fata da ta shahara a duniya ta Indiya take, NILEST ita ma tana ba da tallafin fasaha ta hanyar horar da darussan kan haɓaka ƙirƙira, yin samfuri tare da samarwa, bayar da shawarwari da tuntuɓa, shirya rahotannin yadda za a gudanar da ayyuka, da kula da inganci, tare da sauran ɗimbin ayyuka daban-daban.”

Hakazalika sun yi nuni da cewa, da irin nasarorin da aka samu da kuma tasirin da aka samu a ɓangarori da dama, haɗakar ka iya isar da saƙon koma baya a tsakanin masu ruwa da tsaki a masana’antar fata, musamman a wannan lokaci da NILEST ke aiwatar da manufofi da shirin gwamnatin tarayya kan harkokin fata da ƙirgi.

“Muna da ja kan cewa haɗewar na iya haifar da ruɗani wajen yanke hukunci, tare da kuma rage karsashi kan wasu batutuwa ko rashin samun daidaito wajen aiwatar da manufofin gwamnati, kawo cikas ga ayyukan da ake da su ko shirye-shirye a cikin masana’antar fata da NILEST ke aiwatarwa”, in ji sanarwar.

Kazalika sanarwar ta ce za a iya kuma samun karkatar ra’ayoyin masu ruwa da tsaki da kuma gurgunta ƙwazo da dabarun ƙwararru. A matsayin su na masu ruwa da tsaki a kan lamuran fata, kungiyar ta ce ta lura da cewa haɗewar waɗannan cibiyoyi, zai iya zama barazana ga masu ruwa da tsaki wanda zai haifar da gazawar cika alƙawuran alfanun da za a samu na irin wannan haɗakar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Talauci Da Rashin Aikin Yi Ne Silar Matsalar Tsaro A Arewa – Dan Masani

Next Post

Gwamnatin Kano Ta Kafa Kwamitin Kar-ta-kwana Kan Haramtattun Gine-gine

Related

A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya
Labarai

A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya

4 hours ago
Biyan Tukuici: Gwamna Yusuf Ya Ƙaddamar Da Tallafin Naira 50,000 Ga Mata 5,200 Duk Wata A Kano
Labarai

Biyan ‘Yan Fansho Naira Biliyan 22: NUP Da NLC Sun Bukaci A Yi Koyi Da Gwamna Abba

5 hours ago
Kasar Sin Ta Nuna Alhinin Rasuwar Tsohon Shugaban Nijeriya Buhari
Labarai

Za A Dinga Tunawa Da Buhari A Matsayin Waliyyi A Siyasar Nijeriya —Dakta Zangina

6 hours ago
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista
Manyan Labarai

Tinubu Ya Nada Ɗan Babangida A Matsayin Shugaban Bankin Manoma

7 hours ago
‘Yan Kasuwa Na Shirin Yi Wa Dangote Zanga-zanga Kan Rage Farashin Gas
Labarai

‘Yan Kasuwa Na Shirin Yi Wa Dangote Zanga-zanga Kan Rage Farashin Gas

7 hours ago
Lai Ching-Te Bai Cancanci Zama Jagoran Yankin Taiwan Ba
Ra'ayi Riga

Lai Ching-Te Bai Cancanci Zama Jagoran Yankin Taiwan Ba

7 hours ago
Next Post
Kano

Gwamnatin Kano Ta Kafa Kwamitin Kar-ta-kwana Kan Haramtattun Gine-gine

LABARAI MASU NASABA

Dangote

Dalilin Da Ya Sa Dangote Ya Jinjina Wa Hukumar NPA

July 18, 2025
Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin

Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin

July 18, 2025
2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

July 18, 2025
Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi

Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi

July 18, 2025
majalisar kasa

Kirkirar Sabbin Jihohi Da Kananan Hukumomi Sun Dabaibaye Sauraron Jin Ra’ayoyin Gyaran Tsarin Mulki

July 18, 2025
Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Zambia Da Ci 5-0

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Zambia Da Ci 5-0

July 18, 2025
Yawan Jarin Waje Da Sin Ta Samu Ya Haura Dalar Amurka Biliyan 700

Yawan Jarin Waje Da Sin Ta Samu Ya Haura Dalar Amurka Biliyan 700

July 18, 2025
A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya

A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya

July 18, 2025
Biyan Tukuici: Gwamna Yusuf Ya Ƙaddamar Da Tallafin Naira 50,000 Ga Mata 5,200 Duk Wata A Kano

Biyan ‘Yan Fansho Naira Biliyan 22: NUP Da NLC Sun Bukaci A Yi Koyi Da Gwamna Abba

July 18, 2025
Sin Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ta Kai Syria

Sin Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ta Kai Syria

July 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.