• English
  • Business News
Thursday, August 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Kama Tsohon Firaministan Mali Bisa Zargin Karkatar Da Dukiyar Gwamnati

by Sadiq
6 hours ago
in Kasashen Ketare
0
An Kama Tsohon Firaministan Mali Bisa Zargin Karkatar Da Dukiyar Gwamnati
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

An kama tsohon Firaministan Mali, Choguel Kokalla Maïga, bisa tuhumar cin hanci, rashawa da ɓarnatar da kadarorin gwamnati. 

Wannan na zuwa ne bayan rahoton wani bincike da ya gano wasu kashe-kashe na kuɗin gwamnati ba bisa ƙa’ida ba a lokacin da Maïga yake riƙe da ofishin Firaminista da kuma jagorantar Universal Access Fund (AGEFAU).

  • Allah Zai Kunyata Masu ÆŠaukar Nauyin ’Yan Ta’adda – Gwamnan Zamfara
  • Rangwame: Tinubu Ya Bada Umarnin Sake Bitar Tsarin Yadda Ake KarÉ“ar Haraji 

Rahoton ya bayyana cewa an kashe kuÉ—aÉ—en ba tare da hujja ba, kamar kashe miliyan 15 na CFA a liyafar rana guda a garin Konobougou, alhali dokar kashe kuÉ—i ta iyakance irin wannan taro zuwa 75,000 CFA.

Haka kuma an gano wasu kuÉ—aÉ—e da aka fitar don balaguro da ayyuka ba tare da hujja mai karfi ba.

Bayan fitar rahoton, an gayyaci Maïga tare da wasu tsoffin mataimakansa da suka haɗa da Issiaka Ahmadou Singaré, tsohon shugaban ma’aikata, daraktan kuɗi da gudanarwa na ofishin Firaminista, da wasu manyan jami’an AGEFAU domin yin bayani.

Labarai Masu Nasaba

Afrika Ba Ta Cikin Jerin Fannonin Da Muke Ba Fifiko – Amurka

Waɗanne Ƙasashe Ne Suka Amince Da Kafa Ƙasar Falasɗinu?

Lauyan Maïga, Cheick Oumar Konaré, ya bayyana cewa kamun bai dace ba saboda Maïga ba shi da niyyar guduwa ko lalata shaidu, yana kuma zargin cewa wannan wani mataki ne na siyasa saboda tsohon Firaministan ya daɗe yana sukar gwamnatin soja tun bayan tsawaita mulkinsu ba tare da gudanar da zaɓe ba.

Maïga, ya hau kujerar Firaminista a watan Yulin 2021 bayan gwamnatin sojoji ta yi juyin mulki, inda ya goyi bayan dakatar da shirye-shiryen zaɓe don bai wa gwamnatin soja ƙarin lokaci.

Sai dai daga baya ya fara sukar wasu matakan gwamnati, musamman bayan an dakatar da shi daga kujerarsa a watan Nuwamban 2024.

Tun bayan juyin mulkin 2020 da na 2021, Mali ta kasance ƙarƙashin mulkin soja, kuma ana zargin gwamnati da take haƙƙin ɗan adam da murƙushe ‘yan adawa.

A kwanakin baya ma an kama wasu sojoji bisa zargin kitsa juyin mulki.

Kamun Maïga ya janyo ce-ce-ku-ce a ƙasar, inda wasu ke ganin matakin a matsayin wani yunƙuri na yaƙi da cin hanci, yayin da wasu kuma ke kallonsa a matsayin dabarar murjushe ‘yan adawa, musamman a wannan lokaci da ake buƙatar haɗin kai don dawo da tsarin dimokuraɗiyya a Mali.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: KamuMaliTsohon FiraministaZargi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamna Sule Ya Ziyarci Gidan Yarin Keffi Bayan Tserewar Fursunoni 16

Next Post

NAF Ta Kashe ‘Yan Ta’adda 600 Cikin Wata 8 A Nijeriya

Related

Afrika Ba Ta Cikin Jerin Fannonin Da Muke Ba Fifiko – Amurka
Kasashen Ketare

Afrika Ba Ta Cikin Jerin Fannonin Da Muke Ba Fifiko – Amurka

5 days ago
Waɗanne Ƙasashe Ne Suka Amince Da Kafa Ƙasar Falasɗinu?
Kasashen Ketare

Waɗanne Ƙasashe Ne Suka Amince Da Kafa Ƙasar Falasɗinu?

2 weeks ago
Amurka Ta Gargaɗi Ƴan Nijeriya Kan Zuwa Ƙasarta Domin Haihuwa
Kasashen Ketare

Amurka Ta Gargaɗi Ƴan Nijeriya Kan Zuwa Ƙasarta Domin Haihuwa

2 weeks ago
Faransa Za Ta Fara Jefa Kayan Agaji Ta Sama A Gaza
Kasashen Ketare

Faransa Za Ta Fara Jefa Kayan Agaji Ta Sama A Gaza

2 weeks ago
Iran Ta Zargi Birtaniya, Faransa, Da Jamus Da Gazawa Kan Yarjejeniyar Nukiliyar 2015
Kasashen Ketare

Iran Ta Zargi Birtaniya, Faransa, Da Jamus Da Gazawa Kan Yarjejeniyar Nukiliyar 2015

3 weeks ago
Bayan Shekaru 20 Yana Bacci, Yariman Saudiyya Ya Rasu
Kasashen Ketare

Bayan Shekaru 20 Yana Bacci, Yariman Saudiyya Ya Rasu

4 weeks ago
Next Post
NAF Ta Kashe ‘Yan Ta’adda 600 Cikin Wata 8 A Nijeriya

NAF Ta Kashe 'Yan Ta’adda 600 Cikin Wata 8 A Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

An Cafke Motocin Dako 50 Makare Da Abinci Za Su Shiga Nijar A Zamfara

Gwamna Lawal Ya Ziyarci Yankunan Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Wa Hari A Zamfara

August 14, 2025
’Yansanda Sun Kama Mutum 2 Da Bindigogi Da Alburusai A Filato

’Yansanda Sun Kama Mutum 2 Da Bindigogi Da Alburusai A Filato

August 14, 2025
NAF Ta Kashe ‘Yan Ta’adda 600 Cikin Wata 8 A Nijeriya

NAF Ta Kashe ‘Yan Ta’adda 600 Cikin Wata 8 A Nijeriya

August 14, 2025
An Kama Tsohon Firaministan Mali Bisa Zargin Karkatar Da Dukiyar Gwamnati

An Kama Tsohon Firaministan Mali Bisa Zargin Karkatar Da Dukiyar Gwamnati

August 14, 2025
Gwamna Sule Ya Ziyarci Gidan Yarin Keffi Bayan Tserewar Fursunoni 16

Gwamna Sule Ya Ziyarci Gidan Yarin Keffi Bayan Tserewar Fursunoni 16

August 14, 2025
Yadda Ƙananan Hukumomi Ke Yin Sulhu Da ‘Yan Bindiga A Katsina

Yadda Ƙananan Hukumomi Ke Yin Sulhu Da ‘Yan Bindiga A Katsina

August 14, 2025
Allah Zai Kunyata Masu ÆŠaukar Nauyin ’Yan Ta’adda – Gwamnan Zamfara

Allah Zai Kunyata Masu ÆŠaukar Nauyin ’Yan Ta’adda – Gwamnan Zamfara

August 13, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Ta Bayyana Rashin Gamsuwa Da Manufar Shugaba Trump Ta Korar Marasa Galihu

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Ta Bayyana Rashin Gamsuwa Da Manufar Shugaba Trump Ta Korar Marasa Galihu

August 14, 2025
Gyaruwar Alakar Kasuwancin Sin Da Amurka Ta Zarce Bukatun Kasashen Biyu

Gyaruwar Alakar Kasuwancin Sin Da Amurka Ta Zarce Bukatun Kasashen Biyu

August 13, 2025
APC

2027: Jagororin APC Na Kudu-maso-Yamma Sun Amince Da Tinubu Ya Sake Tsayawa Takara

August 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.