• English
  • Business News
Thursday, September 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ɗaukar Nauyin Ƴan Ta’addan Da Suka Farmake Mu A Kaduna Aka Yi – El-Rufai

by Abubakar Sulaiman
3 days ago
in Siyasa
0
Ɗaukar Nauyin Ƴan Ta’addan Da Suka Farmake Mu A Kaduna Aka Yi – El-Rufai
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Tsohon gwamnan jihar Kaduna kuma tsohon ministan babban birnin tarayya (FCT), Malam Nasir El-Rufai, ya zargi gwamnatin jihar Kaduna da ɗaukar nauyin ƴan daban da suka tarwatsa taron jam’iyyar adawa ta ADC a ranar Asabar.

A wata hira da aka yi da shi a shirin Sunday Politics na gidan talabijin ta Channels da wakilinmu ya kalla, El-Rufai ya yi watsi da iƙirarin rundunar ƴansandan Kaduna cewa jam’iyyarsu ce ta gayyato ƴan daba.

  • ADC Ta Bukaci Tinubu Ya Kafa Dokar Ta Baci A Katsina Da Zamfara Kan Rashin Tsaro
  • Hatsarin Jirgi: Babu Batun Zagon-ƙasa Ga Harkokin Sufurin Jiragen Ƙasan Abuja-Kaduna – Gwamnati

Ya bayyana wannan magana a matsayin “shashanci” tare da jaddada cewa ƴansandan da kansu sun bayar da kariya ga ƴan ta’addan da suka yi ɓarna a wajen. “Wauta ce a ce ni zan gayyato ƴan daba domin su farmaki taron jam’iyyata. Ƴansandan suna wurin, suna sane da abin da ya faru. Sun ba wa ƴan dabbar kariya. Waɗannan ƴan dabar gwamnati ce ta ɗauki nauyinsu,” in ji shi.

El-Rufai ya ƙara bayyana cewa tun a farkon shekarar nan ya rubuta ƙorafi ga Sufeton Ƴansandan Nijeriya kan wasu jami’an ƴansanda a Kaduna da ake amfani da su wajen tsoratar da ’yan adawa tare da yin garkuwa da su. Ya ce har yanzu yana jiran sakamakon binciken da aka fara a kan lamarin.

Tsohon gwamnan ya nuna takaici kan yadda tsarin aikin ƴansandan a Nijeriya ya taɓarɓare. A cewarsa, maimakon jami’an tsaro su kare al’umma, yanzu ana amfani da su wajen ba da kariya ga masu haddasa tashin hankali. “Wannan iƙirarin na ƴansandan cewa ADC za ta gayyato ’yan daba domin su tarwatsa taronta alama ce ta durƙushewar tsarin ƴansandan. Da muna da ƴansanda, yanzu kuwa inuwa ce kawai ta yi saura,” in ji shi.

Labarai Masu Nasaba

Ba Abin Da Zai Hana Tinubu Sake Lashe Zaɓe A 2027 – Jigon APC

Gwamnan Bauchi Ya Gargaɗi Magoya Bayan Wike A PDP

Ya kuma tuna da tsohon abokin ajinsu wanda ya kasance tsohon Sufeton ƴansanda, marigayi Solomon Arase, wanda ya rasu a ranar Lahadi a Abuja bayan gajeriyar rashin lafiya. El-Rufai ya bayyana shi a matsayin mutum nagari, yana mai cewa tsarin ƴansanda na yanzu ya sha bamban da lokacin da Arase ya jagoranta. Daga ƙarshe, ya ce zai sake rubuta ƙorafi ga IGP da kuma hukumar kula da ƴansanda (PSC), yana mai gargadi cewa idan jami’an tsaro suka zama kariya ga masu tada fitina, to hakan zai kai ƙasa ga rugujewa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: ADCAPCElrufaiUba Sani
ShareTweetSendShare
Previous Post

Xi Jinping Ya Gana Da Narendra Modi 

Next Post

Gwamnatin Tarayya Na Shiri Da Ƴan Bindiga, Tana Ba Su Biliyoyi — El-Rufai

Related

Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista
Siyasa

Ba Abin Da Zai Hana Tinubu Sake Lashe Zaɓe A 2027 – Jigon APC

16 hours ago
2027: Fastocin Takarar Shugaban Ƙasa Na Gwamnan Bauchi Sun Bayyana
Manyan Labarai

Gwamnan Bauchi Ya Gargaɗi Magoya Bayan Wike A PDP

23 hours ago
Ina Da Yaƙinin Tinubu Ne Zai Lashe Zaɓen 2027 — Wike
Siyasa

Ina Da Yaƙinin Tinubu Ne Zai Lashe Zaɓen 2027 — Wike

3 days ago
Ɗan Majalisa Zai Saya Wa Makinde Fam Ɗin Takarar Shugaban Ƙasa A 2027
Siyasa

Ɗan Majalisa Zai Saya Wa Makinde Fam Ɗin Takarar Shugaban Ƙasa A 2027

4 days ago
Peter Obi Ya Caccaki Gwamnati Kan Ƙarin Kuɗin Fasfo
Siyasa

Peter Obi Ya Caccaki Gwamnati Kan Ƙarin Kuɗin Fasfo

6 days ago
Ba Zan Nemi Kujerar Siyasa A 2027 Ba — El-Rufai
Siyasa

Ba Zan Nemi Kujerar Siyasa A 2027 Ba — El-Rufai

7 days ago
Next Post
Gwamnatin Tarayya Na Shiri Da Ƴan Bindiga, Tana Ba Su Biliyoyi — El-Rufai

Gwamnatin Tarayya Na Shiri Da Ƴan Bindiga, Tana Ba Su Biliyoyi — El-Rufai

LABARAI MASU NASABA

Ra’ayin Samar Da Ci Gaba Cikin Lumana: Daga Ra’ayin Sin Zuwa Matsayin Da Kasa Da Kasa Suka Cimma

Ra’ayin Samar Da Ci Gaba Cikin Lumana: Daga Ra’ayin Sin Zuwa Matsayin Da Kasa Da Kasa Suka Cimma

September 3, 2025
Gwamna Dauda Lawal Zai Yi Jawabi A Taron Kasuwanci Na AFSNET Karo Na Biyar A Ƙasar Algeria

Gwamna Dauda Lawal Zai Yi Jawabi A Taron Kasuwanci Na AFSNET Karo Na Biyar A Ƙasar Algeria

September 3, 2025
Tinubu Ya Naɗa Shugabannin Jami’o’in Ilimi Na Tarayya Da Ke Zariya Da Kano

Tinubu Ya Naɗa Shugabannin Jami’o’in Ilimi Na Tarayya Da Ke Zariya Da Kano

September 3, 2025
Gwamnoni Sun Yi Kira Ga Tinubu Kan Ci Gaba Da Hako Mai A Kolmani Da Tafkin Chadi 

Gwamnoni Sun Yi Kira Ga Tinubu Kan Ci Gaba Da Hako Mai A Kolmani Da Tafkin Chadi 

September 3, 2025
Kasar Sin Ta Shirya Bikin Gala Na Cika Shekaru 80 Da Samun Nasarar Yakin Turjiyar Jama’ar Kasar Da Yaki Da Mulkin Danniya A Duniya

Kasar Sin Ta Shirya Bikin Gala Na Cika Shekaru 80 Da Samun Nasarar Yakin Turjiyar Jama’ar Kasar Da Yaki Da Mulkin Danniya A Duniya

September 3, 2025
Lookman

Kofin Duniya: Lookman Da Dessers Sun Isa Sansanin Super Eagles A Uyo

September 3, 2025
Firaministan Senegal: Yadda Sinawa Ke Girmama Tarihi Da Kiyaye Labarun Abubuwan Da Suka Faru Da Su Na Da Matukar Burgewa 

Firaministan Senegal: Yadda Sinawa Ke Girmama Tarihi Da Kiyaye Labarun Abubuwan Da Suka Faru Da Su Na Da Matukar Burgewa 

September 3, 2025
Hatsarin Jiragen Ruwa

Mutane 29 Sun Rasa Rayukansu A Wani Hatsarin Jirgin Ruwa A Jihar Neja

September 3, 2025
Shettima

Za Mu Kare Bukatun Nijeriya A Mashigin Tekun Guinea – Shettima

September 3, 2025
Shekaru 80 Na Nasara: Kasar Sin Ta Nuna Gado Mai Kyau Na Yaki Da Zalunci

Shekaru 80 Na Nasara: Kasar Sin Ta Nuna Gado Mai Kyau Na Yaki Da Zalunci

September 3, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.