• English
  • Business News
Friday, September 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sin: Bin Tafarki Na Gaskiya

by CGTN Hausa and Sulaiman
2 days ago
in Ra'ayi Riga
0
Sin: Bin Tafarki Na Gaskiya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A yau, al’ummar kasar Sin sun gudanar da wani gagarumin gangami da faretin soji a birnin Beijing na kasar, domin tunawa da cikar shekaru 80 da samun nasarar yakin da al’ummar Sin suka yi da mamayar dakarun kasar Japan, da yakin duniya na kin tafarkin murdiya. Shugabanin wasu kasashe 26 ne suka halarci bikin tunawa da ya gudana, inda shugaban kasar Sin Xi Jinping ya yi alkawarin cewa, jama’ar kasar Sin za su tsaya tsayin daka wajen bin tafarki na gaskiya, wanda zai haifar da ci gaban daukacin dan Adam, da bin hanyar raya kasa cikin lumana, da yin aiki kafada da kafada da al’ummun kasashe daban daban, wajen gina al’umma mai kyakkyawar makomar bai daya ga bil’adama.

 

Me ya sa Sinawa za su iya bin tafarki na gaskiya? Domin sun dade suna jin radadin yake-yake.

  • Ya Kamata El-Rufai Ya Yi Bayani Kan Zargin Gwamnati Na Biyan ‘Yan Bindiga Kuɗaɗe – Datti
  • Xi Jinping Ya Duba Faretin Rundunonin Sojoji Da Kayayyakin Soja, Shugabannin Kasashe 26 Su Ma Sun Halarci Bikin

Kasar Sin babban fagen daga ne a yakin duniya na kin tafarkin murdiya. Lokacin da sojojin Japan suka fara mamaye kasar Sin a shekara ta 1931, Sinawa sun kasance na farko a duniya wajen daga tutar yaki da tafarkin murdiya. Yayin da wasu kasashen yammacin duniya ke tunanin magance yaki da ‘yan Nazi, sojoji da fararen hula na kasar Sin sun riga sun tashi haikan don yaki da maharan kasar Japan, ko da yake ba su da makamai masu inganci a lokacin.

Sama da shekaru 80 da suka gabata, kasar Sin ta kasance cikin talauci da rauni, kuma sadaukarwar da Sinawa suka yi wajen kare kasarsu tana da yawa. Bisa kididdigar da aka yi, yawan sojojin kasar Sin da fararen hula na kasar da suka rasa rayuka, ko kuma suka ji rauni a yakin da suka yi da sojojin Japan ya zarce miliyan 35, inda yawan hasarar da aka samu ya haura dala biliyan 600. Al’ummar kasar Sin, bisa babbar sadaukarwar da suka yi, sun samar da damar cin nasara a yakin da jama’ar kasashe daban daban suka yi na kin tafarkin murdiya. Saboda a yayin yakin na tsawon shekaru 14 da Sinawa suka yi da maharan kasar Japan, fagen daga dake kasar Sin ya janyo hankalin kaso 60% zuwa 94% na sojojin kasa na kasar Japan. Wannan yanayi ya wargaza muradin sojojin Japan da masu bin tafarkin murdiya na kasar Jamus, na hadin gwiwa a kokarin mamaye duniya daga dukkan bangarorin gabas da yamma.

Labarai Masu Nasaba

Kasar Sin Za Ta Ci Gaba Da Ba Da Gudummawarta Wajen Kiyaye Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya 

Kyakkyawan Fata Kan Nasarar Yaki Da Akidar Mulkin Danniya A Duniya

Yakin da Sinawa suka yi cikin adalci ya sa su samun karramawa, da goyon baya daga gamayyar kasa da kasa. Kana yadda al’ummun kasashe daban daban a wancan lokaci suka hada kai da juna a karkashin tutar yaki da tafarkin murdiya, ko da yake akwai bambanci a tsakaninsu ta fuskokin kasa, da kabila, da kuma akida, ya kai ga cimma nasara a yakin kin tafarkin murdiya, da tabbatar da sabon tsarin kasa da kasa bayan yakin a karshe.

Tarihin yakin da al’ummar Sin suka yi da mamayar dakarun kasar Japan, da yakin duniya na kin tafarkin murdiya ya nuna mana wasu tunani masu zurfi, wadanda jama’ar kasar Sin suka san su sosai:

Da farko dai, komai wahalhalun da aka sha, adalci zai yi galaba a kan muguntawa, haske kuma zai kori duhu. Wannan tamkar doka ce ta tarihi.

Na biyu, ‘yan Adam na da makomar bai daya. Ya kamata a samu daidaituwa, da jituwa, da cude-ni-in-cude-ka, tsakanin kasashe da kabilu daban daban, ta yadda za a samu damar tabbatar da tsaron bai daya, da kawar da yaki daga karshensa.

A zamanin da muke ciki, ana ta samun abkuwar rikice-rikice a duniya, inda dan Adam suka sake fuskantar bukatar yin zabi tsakanin cudanya da juna ko yin gaba da juna, zaman lafiya ko yaki. Sai dai kasar Sin ta riga ta samu babban ci gaba: Yanzu kasar na bikin tunawa da nasarar da ta samu ta gagarumin faretin soji. Kana a karkashin jagorancin jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin, jama’ar kasar na ta kokarin zamanantar da kasarsu bisa hadin kansu.

Jawabin shugaba Xi Jinping ya bayyanawa duniya cewa: Kasar Sin mai karfi za ta ci gaba da samar da gudummawa ga ci gaban al’ummar dan Adam da na tattalin arzikin duniya cikin lumana.

Bari mu yi kokarin neman samun ci gaba tare, bisa wani tafarki na gaskiya. (Bello Wang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ba Abin Da Zai Hana Tinubu Sake Lashe Zaɓe A 2027 – Jigon APC

Next Post

Kungiyar Kare Shirye-shiryen Tinubu Ta Nemi A Dakatar Da Shugaban Kamfanin NNPCL 

Related

Kasar Sin Za Ta Ci Gaba Da Ba Da Gudummawarta Wajen Kiyaye Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya 
Ra'ayi Riga

Kasar Sin Za Ta Ci Gaba Da Ba Da Gudummawarta Wajen Kiyaye Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya 

15 hours ago
Kyakkyawan Fata Kan Nasarar Yaki Da Akidar Mulkin Danniya A Duniya
Ra'ayi Riga

Kyakkyawan Fata Kan Nasarar Yaki Da Akidar Mulkin Danniya A Duniya

2 days ago
Shawarar GGI: Faduwa Ta Zo Daidai Da Zama
Ra'ayi Riga

Shawarar GGI: Faduwa Ta Zo Daidai Da Zama

3 days ago
Yadda Kasar Sin Ta Nuna Wa Afirka Asalin Ma’Anar Hakkin Dan Adam Sabanin Irin Na Kasashen Yamma
Ra'ayi Riga

Yadda Kasar Sin Ta Nuna Wa Afirka Asalin Ma’Anar Hakkin Dan Adam Sabanin Irin Na Kasashen Yamma

7 days ago
Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Ya Kawo Wa Afirka Fatan Warware Matsalar Karancin Wutar Lantarki
Ra'ayi Riga

Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Ya Kawo Wa Afirka Fatan Warware Matsalar Karancin Wutar Lantarki

1 week ago
Ranar Hausa Ta Duniya: Ba Ka Iyawa Duk Dagewarka Kuma Ba A Yaba Maka
Ra'ayi Riga

Ranar Hausa Ta Duniya: Ba Ka Iyawa Duk Dagewarka Kuma Ba A Yaba Maka

1 week ago
Next Post
Kungiyar Kare Shirye-shiryen Tinubu Ta Nemi A Dakatar Da Shugaban Kamfanin NNPCL 

Kungiyar Kare Shirye-shiryen Tinubu Ta Nemi A Dakatar Da Shugaban Kamfanin NNPCL 

LABARAI MASU NASABA

Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai

Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai

September 5, 2025
Ministan Tsaro

Dawowar Matsalar Tsaro: Ta Haifar Da Cece-kuce Kan Daukar Matakin Kare Kai

September 5, 2025
Sin Ta Wanzar Da Ruhin Juriya Ta Hanyar Yakar Tafarkin Murdiya

Sin Ta Wanzar Da Ruhin Juriya Ta Hanyar Yakar Tafarkin Murdiya

September 4, 2025
An Kaddamar Da Cibiyar Raya Ilimin Dijital Ta Sin Da Afirka A Tanzania

An Kaddamar Da Cibiyar Raya Ilimin Dijital Ta Sin Da Afirka A Tanzania

September 4, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 13 A Wani Harin Kwanton-ɓauna A Borno

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 13 A Wani Harin Kwanton-ɓauna A Borno

September 4, 2025
Babban Sha’anin Dan Adam Na Wanzar Da Zaman Lafiya Da Ci Gaba Zai Samu Nasara

Babban Sha’anin Dan Adam Na Wanzar Da Zaman Lafiya Da Ci Gaba Zai Samu Nasara

September 4, 2025
Dakarun PLA Sun Gudanar Da Sintiri A Yankin Tekun Kudancin Sin

Dakarun PLA Sun Gudanar Da Sintiri A Yankin Tekun Kudancin Sin

September 4, 2025
Spence Na Dab Da Kafa Tarihin Zama Musulmi Na Farko Da Zai Buga Wa Ingila Ƙwallo

Spence Na Dab Da Kafa Tarihin Zama Musulmi Na Farko Da Zai Buga Wa Ingila Ƙwallo

September 4, 2025
Gwamna Sule Ya Gargaɗi ‘Yan Siyasa Kan Fara Yaƙin Neman Zaɓe A Nasarawa

Gwamna Sule Ya Gargaɗi ‘Yan Siyasa Kan Fara Yaƙin Neman Zaɓe A Nasarawa

September 4, 2025
Xi Ya Gana Da Shugaban Zimbabwe Da Na Jamhuriyar Kongo

Xi Ya Gana Da Shugaban Zimbabwe Da Na Jamhuriyar Kongo

September 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.