• English
  • Business News
Saturday, September 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

PDP Ta Dage Kan Gudanar Da Taronta Duk Da Sabbin Sharuɗɗan Da Ɓangaren Wike Ya Gindaya

by Idris Aliyu Daudawa
5 hours ago
in Siyasa
0
PDP Ta Dage Kan Gudanar Da Taronta Duk Da Sabbin Sharuɗɗan Da Ɓangaren Wike Ya Gindaya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Babbar jam’iyar adawa ta PDP ta ƙaddamar da kwamitin gudanar da taronta na ƙasa mai mambobi 119, insa shugabannin jam’iyyar suka yi gargaɗin cewa ba za su sake lamintar wani yunƙuri ya ruguza taron ba.

Shugaban jam’iyyar PDP na ƙasa, Umar Damagum da shugaban ƙungiyar gwamnonin PDP, Bala Mohammed da shugaban kwamitin amintattu da tsohon shugaban majalisar dattawa, Adolphus Wabara, sun tabbatar da cewa jam’iyyar ta shirya tunkarar gudanar da taronta na ƙasa ba gudu ba ja dawa.

  • PDP Ta Zama Fanko, Ta Rasa Komai– Dele Momodu
  • 2027: Idan Kana Son Tarwatsa PDP, To Ka Dawo Da Peter Obi – Wike

Sai dai kuma ɓangaren ministan Babban Birnin Tarayya Abuja, Nyesom Wike, ya fitar da sabbin sharuɗɗa kafin gudanar da babban taron jam’iyyar da zai gudana a ranar 15 da 16 ga Nuwamba, 2025, wanda aka tsara za a yi a garin Ibadan, Babban Birnin Jihar Oyo.

PDP ta tsinci kanta cikin rikici tun bayan gudanar da zaɓen fid da gwani na shugaban ƙasa a 2023, wanda ya fitar da tsohon mataimakin shugaba ƙasa, Atiku Abubakar a matsayin ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar.

Bayan fitowar Atiku, wanda ya zo na biyu ya kasance gwamnan Jihar Ribas a lokacin, Nyesom Wike, ya samu goyon bayan wasu daga cikin gwamnonin abokansa, ciki har da Samuel Ortom (Benuwai), Seyi Makinde (Oyo), Ifeanyi Ugwuanyi (Inugu), da Okezie Ikpeazu (Abiya). Wanda suka kafa ƙungiyar G-5 don yin aiki tare wajen yaƙar Atiku.

Labarai Masu Nasaba

INEC Ta Amince Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

APC Ce Ke Kai Mana Hari Saboda Siyasa – Malami

Wike ya goyi bayan Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu, a wani mataki da ya samu matsayin ministan Babban Birnin Tarayya Abuja.

Duk da yake har yanzu shi mamba ne na PDP, Wike ya kasance yana bayyana cewa zai ci gaba da kasancewa cikin jam’iyyar yayin da yake kuma yin aiki don sake zaɓen Tinubu, wani matsayin da yawancin mambobin PDP ba sa jin daɗinsa.

Kafin yanzu, jam’iyyar ta shiga cikin wata babbar matsala kan matsayin sakatare jam’iyyar na ƙasa, tsakanin Samuel Anyanwu, wanda Wike yake goyo baya, da Sunday Ude-Okoye, wanda yake samun goyon bayan Gwamnan Jihar Inugu, Peter Mbah.

Mafi yawancin shugabannin jam’iyyar sun yi tunanin cewa idan har Anyanwu ya dawo a matsayin sakataren jam’iyyar na ƙasa zai kwantar da hankalin Wike. Amma kafin babban taron na Ibadan, ministan Abuja ya fito da sabbin sharuɗɗa.

Vangaren magoya bayan Wike sun gudanar da taro tare da shimfiɗa sabbin sharuɗɗa ta yadda za a iya gudanar da taron cikin zaman lafiya da kwanciyar hankali.

Cikin waɗanda suka halarci taron sun haɗa da tsofaffin gwamnonin, Samuel Ortom (Benuwai), Ifeanyi Ugwuanyi (Inugu), Ayo Fayose (Ekiti) da Okezie Ikpeazu (Abiya), da sakataren jam’iyyar na ƙasa, Anyanwu.

Vangaren ya kafa sharaɗin cewa dole ne shugaban jam’iyyar na ƙasa ya fito daga yankin arewa na tsakiya bisa ga tsarin rabon muƙamai na yankuna na taron 2021.

A cewar ɓangaren, rashin bin ƙa’idojin da aka ambata zai sa tsarin babban taron ya ruguze ya zama mara inganci, saboda za a samu rarrabuwan kawuna a tsakanin ‘ya’yan jam’iyyar.

Sauran sharuɗɗan sun haɗa da yin kiran gaggawa ga kwamitin gudanarwa na ƙasa don gudanar da sabbin zaɓen shugabanni a jihohin Ebonyi da Anambra bisa ga hukuncin kotu da gudanar da sabon taron jam’iyyar na yankin kudu maso gabas da tabbatar da sakamakon taron kudu maso kudu da aka gudanar a Kalabar na Jihar Kuros Ribas, wanda kotu ta riga ta tabbatar da shi da kuma gudanar da zaɓen shugabannin ƙananan hukumomi na Jihar Ekiti cikin gaggawa bisa ga hukuncin kotu.

Amma yayin da yake magana a wajen ƙaddamar da kwamitin shirya taron mai mambobi 119 a hedkwatar PDP a Abuja, shugaban ƙungiyar gwamnonin PDP, Bala Mohammed ya bayyana cewa ba za su ci gaba da yin shiru ba suna barin wasu mutane suna lalata musu jam’iyyar.

Ya yaba da jagorancin Damagum da ingancin kwamitin taron, yana cewa, “Babu shakku kan ƙarfin wannan shugabancin. Sun yi hakan a baya, kuma muna ganin za su yi iya bakin ƙoƙarinsu. Gwamnonin PDP suna tare da sauran ‘ya’yan jam’iyyar nan wajen jagoran wannan kwamitin.

Da yake jawabi kan wannan dambarwar, masanin harkokin siyasa, Farfesa Kamilu Sani Fage ya gargaɗi cewa PDP na fuskantar wata matsala idan ba ta ɗauki matakan gaggawa wajen magance buƙatun Wike ba.

Ya ce Wike ya zama ƙarfan ƙafa a cikin jam’iyyar, domin yana iya bayar da umurni bisa irin gina mabiyansa, inda ya ce waɗannan sabbin sharuɗɗan da ya gindaya sun saɓa da tsarin dimokuraɗiyya.

Fage ya ƙara da cewa Wike yana ta yaƙar PDP tun daga 2023 ta hanyar tallata Tinubu, karɓar muƙamin minista a gwamnatin APC, da kuma raunana PDP a ƙasa da kuma a Jihar Ribas.

Ya gargaɗi cewa “Jam’iyyar tana buƙatar tabbatar da ladaftarwa. Babu wanda ya mallaki PDP. Idan suka bar Wike ya ci gaba, zai haifar da babbar matsala.”

A cewarsa, PDP na fuskantar haɗarin maimaita taron 2015, idan ba ta ɗauki mataki ba. “Idan tana son ta tsaya da ƙafarta, dole ne ta ɗauki matsaya mai ƙarfi. In ba haka ba, abin da ya faru a 2015 na iya maimaituwa a 2027.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Nyesom WikePDP
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango

Next Post

Gwamnatin Tarayya Ta Sanar Da Sabon Sharaɗi Na Buɗe Asusun Banki

Related

INEC Ta Amince Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC
Manyan Labarai

INEC Ta Amince Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

3 days ago
APC Ce Ke Kai Mana Hari Saboda Siyasa – Malami
Manyan Labarai

APC Ce Ke Kai Mana Hari Saboda Siyasa – Malami

4 days ago
Rikicin NNPP A Kano: Wani Tsagi Ya Soki Korar Abdulmumini Jibrin Kofa
Siyasa

Rikicin NNPP A Kano: Wani Tsagi Ya Soki Korar Abdulmumini Jibrin Kofa

7 days ago
Tsohon Mataimakin Gwamnan Gombe Da Wasu jigogin PDP Sun Koma APC
Siyasa

Tsohon Mataimakin Gwamnan Gombe Da Wasu jigogin PDP Sun Koma APC

1 week ago
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista
Siyasa

Ba Abin Da Zai Hana Tinubu Sake Lashe Zaɓe A 2027 – Jigon APC

1 week ago
2027: Fastocin Takarar Shugaban Ƙasa Na Gwamnan Bauchi Sun Bayyana
Manyan Labarai

Gwamnan Bauchi Ya Gargaɗi Magoya Bayan Wike A PDP

1 week ago
Next Post
Gwamnatin Tarayya Ta Sanar Da Sabon Sharaɗi Na Buɗe Asusun Banki

Gwamnatin Tarayya Ta Sanar Da Sabon Sharaɗi Na Buɗe Asusun Banki

LABARAI MASU NASABA

Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

September 13, 2025
Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

September 13, 2025
Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi

Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi

September 13, 2025
An Shirya Haɗin Gwiwa Da Hukumomi Don Magance Matsalar Ambaliyar Ruwa

An Shirya Haɗin Gwiwa Da Hukumomi Don Magance Matsalar Ambaliyar Ruwa

September 13, 2025
Majalisar Tarayya Ta Magantu Kan Gawar Da Aka Samu A Harabarta

Majalisar Tarayya Ta Magantu Kan Gawar Da Aka Samu A Harabarta

September 13, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Sanar Da Sabon Sharaɗi Na Buɗe Asusun Banki

Gwamnatin Tarayya Ta Sanar Da Sabon Sharaɗi Na Buɗe Asusun Banki

September 13, 2025
PDP Ta Dage Kan Gudanar Da Taronta Duk Da Sabbin Sharuɗɗan Da Ɓangaren Wike Ya Gindaya

PDP Ta Dage Kan Gudanar Da Taronta Duk Da Sabbin Sharuɗɗan Da Ɓangaren Wike Ya Gindaya

September 13, 2025
Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango

Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango

September 13, 2025
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

September 13, 2025
Gwamnatin Tarayya Za Ta Inganta Muhimman Abubuwan More Rayuwa Don Ci Gaban Ƙasa

Gwamnatin Tarayya Za Ta Inganta Muhimman Abubuwan More Rayuwa Don Ci Gaban Ƙasa

September 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.