• English
  • Business News
Saturday, June 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nasarar Tsarin CBN Na Samar Da Kudaden Habaka Tattalin Arzikin Nijeriya

by Leadership Hausa
3 years ago
in Labaran Kasuwanci
0
Nasarar Tsarin CBN Na Samar Da Kudaden Habaka Tattalin Arzikin Nijeriya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A daukacin fadin duniya manyan Bankuna na bayar da gagarumar gudunmawa wajen habbaka wa da kuma bunkasa tattalin arzikin kasashe ta fannoni da dama.

A zahiri suna bayar gudunmawar ce saboda irin wadannan Bankunan nan ne makura wajen bayar da rancen kudade, kirkiro da tsare-tsaren kudade, musamman ganin cewa, irin wannan bankunan na a karkashin Gwamnati su ne ke tabbatar da samar da daitaito a tsare-tsaren hanyoyin da suka dace a tunkara don samar da canje-canjen sa suka kamata ga fannin tattalin arziki.

  • Asalin Abin Da Ya Sa Jama’a Ba Su Ganin Alfanun Tallafin Mai – Dakta Yakubu
  • ‘Yan Boko Haram Sun Kashe Masunta A Tafkin Chadi

Alal misali, a Nijeriya, dora Godwin Emefiele a matsayin Gwamnan Babban Bankin Nijeriya CBN za a iya cewa ya zuwa yanzu, kwaliiya ta biya kudin sabulu domin da hawarsa karagar shugabancin CBN ya kara inganta ayyukan Bankin, musamman ta hanyar inganta tsare-tsaren samar da kudade, inganta kasuwanin hada-hadar kudade da samar da hanya mai sauki don karbar kudade daga CBN don zuba jari a fannin kasuwanci ta hanyar samun rancen kudade daga CBN.

Daukin da Emefiele ya samar a bangaren harkokin Bankuna ya taimaka wa Gwamnatin matuka, ya na da kyau a sanar da cewa, koda yake irin wannan daukin na samar da kudade ba sabon abu ba ne domin an faro hakan ne tun a shekarar 1920.

Bugu da kari, akasarinManyan Bankuna da ke a kasashen da suka ci gaba suna samar da saukakar hanyoyi don bayar da goyon baya ga farfado da tattalin arzikinsu, inda alal misali, ko a shekarar 2008 zuwa 2009, irin wadannan kasashen sun taka muhimmiyar rasa wajen tsamo kasashen su daga matsayin tattalin arziki da da suka tsinci kansu a ciki da kuma a lokacin da duniya ta fuskanci kalubalen bullar annobar Korona, wanda samar da kudade na daga cikin dabarun da kasashen ke yi suna yi ne, don kara bunkasa tattalin arzikinsu.

Labarai Masu Nasaba

Kuratan Sojoji 1,196 Aka Yaye A Makarantar Horar Da Sojoji Ta Zariya

Za Mu Tabbatar Da Samun Kyakkyawar Alaka Da Gwamnati Don Ci Gaban Kasuwar Kofar Ruwa – ‘Yanleman

A bangaren Gwamnati mai ci a yanzu, ta samar da dauki na zuba sama da Naira Tiriliyan 3, inda wadannan kudaden suka taimaka wajen kara samar da ayyukan yi da kuma da kara bunkasa tattalin arzikin kasar nan, inda hakan ya sa CBN tun a shekarar 2015, ya na ci gaba da kirkiro da shirye-shirye iriiri na samar da dauki yadda tattalin arzikin Nijeriya zai ci gaba da tafiya yadda ake bukata.

Misalin, CBN ya kirkiro da tsarin (PPP) wanda za a mayar da hankali wajen karfafa kamfanonin cikin gida don ci gaba da sarrafa kaya a cikin kasar nan, wanda kuma hakan zai rage yawan shigo da kaya daga ketare da kara samar da aikin yi ga ‘yan Nijeriya da sauransu Har ila yau, a ranar 31 zuwa 28 na watan Janairun ne a babban bankin kasa CBN da ke Abuja aka kaddamar da mika Cakin Banki na jimllar Naira biliyan 23.2 ga bankunan kasuwanci bakwai da suka shiga cikin shirye-shiyen sa, inda su kuma wadannan Bankunan da suka amfana, za su yi amfani da wasu daga cikin kudaden wajen habbaka ayyukan su, samar da ayyukan yi a ‘yan kasar da sauransu.

Hakazalika, bisa wata kididdiga da aka samo daga CBN ta nuna cewa, CBN ya samar da daukin kudade ga fannin kerere da suka kai na jimllar Naira biliyan 803.36 inda tuni an zuba wadannan kudaden a cikin ayyuka 228 daban-daban da suka hada da Noma, Hakar Ma’adanai, inganta masana’antu da sauransu.

Haka kuma, CBN a watan Mayun 2020 ya gabatar da tsaretsaren wanzar da samar da dauki bayan bullar annobar Korona a kasar nan, wanda daya daga cikin manufar haka ita ce don a cike gibin da ake ganin bullar annobar za ta haifar ga fannoni daban-daban na tattalin arzikin Nijeriya da kuma masana’antu masu zaman kansu dake a kasar.

Kafin Godwin Emiefele ya samar da wannan daukin, fannin kere -kere na Nijeriya na samar da kasa da kashi 15 ne kacal ne a cikin dari, ga tattalin arzikin Nijeriya, inda hakan ya nuna babbar damuwar, ita ce yadda aka ci gaba da shigo da kaya daga ketare bayan alhali Nijeriya na da karfin da za ta iya sarrafa kaya har ta fitar zuwa ketare.

Har ila yau, tsarin da Emefiele ya kirkiro ya kara inganta dangantaka da Bankunan hada-hadar kudade na DMB da kuma a tsakanin sauran Cibiyoyin hada-hadar kudade inda daukacin su suka mayar da hankali a fannonin aikin noma, fannin kere-kere.

Bugu da kari, a karkashin samar da ainihin kayan aiki wato a Turance, (RSF), CBN ya zuba jimllar Naira tiriliyan 1.40 zuwa Naira tiriliyan 331, musamman domin amfani da kudaden a fannin aikin noma da fannin

ma’adanai da sauransu, inda kuma a daukin da CBN ya samar a shirin (RSSF), ya zuba Naira biliyan 166.21 don yin ayyyuka guda 25.

CBN ba wai ya mayar da hankali ne wajen samar da daukin kudade ba ne kawai, har da kuma wayar da kan masu bukatar zuba jari domin su zuba nasu jarin a fanoni don a kara bunkasa tattalin arzikin Nijeriya.

Har ila yau, a daukin da CBN a watan Afirilun 2022, ya samar biyo bayan bullar annobar Korona a kasar nan, ya dauki matakai da dama na fadada samar da dauki a fannin kiwon lafiya, inda CBN ya fitar da Naira biliyan 93 don a kara habaka fannin da kuma gudanar da ayyukan da ake sa burin cimma a kasar.

Manufar shirin shi ne, samar da bashi ga kamfanonin cikin gida da ke sarrafa magunguna, inda kuma tsarin ke bukatar ganin an kara samar da masu zaman kansu da ke son zuba jari a fannin kiwon lafiya, musamman don a rage yawan ‘yan Nijeriya da ke fita zuwa ketare neman lafiya.

Babban misali a nasarar da CBN ya samar a fannin na inganta kiwon lafiya a kasar shi ne, yadda a kwanan baya Mataimakin Shugaban Kasa Yemi Osinbajo yaje wani Asibitin da ke a cikin kasar nan don a duba lafiyarsa.

Wannan ya nuna a zahiri tsarin na Emefiele ya nuna akwai bukatar a kara wa bankunan kasuwanci na kasar kwarin gwiwa don su hadaka da masu son zuba jari a daukacin fannonin tattalin arzikin Nijeriya, kamar yadda Emefiele ke yawan yin kiraye-kiraye akai.

Akpan mazauni ne a garin Kalaba mai kuma yin fashin baki a kan tattalin arziki.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Babban Bankin NijeriyaBankunaCBNEmefieleHabaka Tattalin ArzikiKasashe
ShareTweetSendShare
Previous Post

‘Yan Boko Haram Sun Kashe Masunta A Tafkin Chadi

Next Post

Me Ya Sa Ba A Fara Shekarar Hijirah Da Ranar Badar Ko Ranar Cikar Wahayi Ba? (I)

Related

Kuratan Sojoji 1,196 Aka Yaye A Makarantar Horar Da Sojoji Ta Zariya
Labaran Kasuwanci

Kuratan Sojoji 1,196 Aka Yaye A Makarantar Horar Da Sojoji Ta Zariya

1 week ago
Za Mu Tabbatar Da Samun Kyakkyawar Alaka Da Gwamnati Don Ci Gaban Kasuwar Kofar Ruwa – ‘Yanleman
Labaran Kasuwanci

Za Mu Tabbatar Da Samun Kyakkyawar Alaka Da Gwamnati Don Ci Gaban Kasuwar Kofar Ruwa – ‘Yanleman

6 months ago
Alternative Bank Shi Ne Mafi Inganci Da Baya Amfani Da Kuɗin Ruwa Da Zuwa Da Fasaha A 2024
Labarai

Alternative Bank Shi Ne Mafi Inganci Da Baya Amfani Da Kuɗin Ruwa Da Zuwa Da Fasaha A 2024

7 months ago
Kamfanin NNPCL Zai Cefanar Da Matatun Mai Na Kaduna Da Warri
Labarai

Kamfanin NNPCL Zai Cefanar Da Matatun Mai Na Kaduna Da Warri

10 months ago
Ministan Ma’adanai Ya Bukaci Masu Harkar Ma’adanai A Jihar Nasarawa Su Zauna Lafiya
Labaran Kasuwanci

Ministan Ma’adanai Ya Bukaci Masu Harkar Ma’adanai A Jihar Nasarawa Su Zauna Lafiya

10 months ago
Rikicin Dangote Da NMDPRA: Gwamnatin Tarayya Zata Yi Sasanci
Labaran Kasuwanci

Rikicin Dangote Da NMDPRA: Gwamnatin Tarayya Zata Yi Sasanci

11 months ago
Next Post
Me Ya Sa Ba A Fara Shekarar Hijirah Da Ranar Badar Ko Ranar Cikar Wahayi Ba? (I)

Me Ya Sa Ba A Fara Shekarar Hijirah Da Ranar Badar Ko Ranar Cikar Wahayi Ba? (I)

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

June 28, 2025
An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

June 28, 2025
Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

June 28, 2025
Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

June 28, 2025
Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

June 28, 2025
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

June 28, 2025
Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

June 28, 2025
An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

June 28, 2025
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

June 28, 2025
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

June 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.