ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Boko Haram Sun Kashe Masunta A Tafkin Chadi

by Muhammad
4 years ago
'Yan

‘Yan ta’addar Boko Haram sun kai hari kan masuntan Nijar, inda suka yi awon gaba da wasu tare da kashe wasu a yankin tafkin Chadi da ke Jamhuriyar Nijar, kamar yadda wata majiya ta bayyana.

‘Yan ta’addar sun yi nasarar kashe masunta da dama daga tsibirin Kwatar Kaoulaha da ke yankin Diffa a ranar Lahadi zuwa Litinin, inda suka yi wa wasu yankan rago tare da yin garkuwa da wasu saboda rashin bin umarnin da aka ba su na barin yankin, kamar yadda masunta suka shaida wa kamfanin dillancin labarai na AFP.

  • An Kashe ‘Yan Boko Haram 49 A Sansaninsu 3 Yayin Luguden Wuta Ta Sama
  • Sojoji Sun Kashe Mayakan Boko Haram 6, Sun Kama Wasu A Borno

“An kashe masunta da yawa tare da yin garkuwa da wasu da mayakan Boko Haram masu biyayya ga Baakura Buduma suka yi garkuwa da su saboda sun gaza ficewa daga yankin kamar yadda aka umarce su,” in ji wani masunta, Kallah Sani, yayin da yake magana kan wani shugaban kungiyar Boko Haram na yankin.

ADVERTISEMENT

Sani bai iya bayar da takamaiman adadin wadanda suka mutu ba amma ya ce wadanda suka tsere ba, sun shaida masa masunta da dama suna tsibirin a lokacin da aka kai harin.

Sani yana cikin masunta kimanin 300 da suka yi biyayya ga sanarwar barin aiki na awa daya, inda suka hakura da kama su da sauran dukiyoyinsu ga ‘yan ta’addar.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

“Sun gaya mana cewa za su kwashe duk abin da muka mallaka a matsayin ganima tun lokacin da gwamnatinmu ta kama kudadensu,” kamar yadda ya shaida wa AFP.

A ranar Juma’ar da ta gabata ne kungiyar Boko Haram ta umarci masuntan wadanda galibinsu ‘yan Arewa maso Yammacin Nijeriya ne da su bar yankin su bar dukiyoyinsu a matsayin ganima ga mayakan, in ji wani masunci, Anas Ibrahim.

“Su (Boko Haram) sun zo ne da kwale-kwale masu gudu guda biyu, suka umarce mu da mu bar tsibirin, kada mu dauki komai sai kayan da muke da su,” Ibrahim ya shaida wa AFP.

“Masu tayar da kayar bayan sun dawo ne a ranar Lahadi inda suka kashe wadanda suka samu, tare da lalata kwale-kwalen su na kamun kifi da hana su tserewa,” in ji shi.

Wata majiyar tsaron Nijeriyar ta kuma tabbatar da faruwar lamarin da kuma kashe-kashen, inda ta ce ‘yan ta’addar sun ji haushin yadda Nijar ta kama masu sayar musu da abinci da wani mai safarar kudi.

Gwamnatin Nijar ba ta amsa kiraye-kirayen neman tabbaci ba.

Sai dai wani jami’in yankin Nijar daga yankin ya shaidawa kamfanin dillancin labaran Faransa na AFP cewa ‘yan jihadin sun umarci mazauna yankin da su fice daga tsibirin tare da kashe wadanda ba su yi ba.

“Na ga gawawwaki 11 da suka hada da na masunta kuma a cikinsu akwai ‘yan Nijeriya uku, sauran ‘yan Nijar ne,” inji majiyar.

“Sun ce akwai wasu mace-mace a tsibirin.”

Fadin tafkin Chadi mai fadin fadama ya ratsa kan iyakokin Nijeriya da Nijar da Kamaru da Chadi, kuma masu jihadi sun yi amfani da kananan tsibiran da suke da su a matsayin mafaka.

A shekarar 2014 ne kungiyar Boko Haram ta kwace tsibiran da ke tafkin Chadi bayan munanan hare-hare, lamarin da ya tilastawa masunta tserewa daga gidajensu. Har yanzu dai kungiyar Boko Haram na rike da tsibiran da ke gefen tafkin na Nijar.

A shekarar 2020, kungiyar Islamic State West Africa Province, wacce ta balle daga Boko Haram, ta kwace mafi yawan yankunan da Boko Haram ke iko da su, tare da barin masunta su komen.

'Yan
Muhammad
+ postsBio
  • Muhammad
    Cikin Shekaru 28, Kudiri Ƙasa Da 10 Sanatocin Zamfara Ta Arewa Suka Gabatar A Majalisa – Shinkafi
  • Muhammad
    2027: NNPP Ta Yi Wa Korarrun Mambobinta Afuwa, Ta Yi Alƙawarin Basu Tikitin Kai-tsaye
  • Muhammad
    Musulunci Na Fuskantar Barazana A Karƙashin Mulkin Tinubu — Datti Baba-Ahmed
  • Muhammad
    Kwankwaso Tamkar Tsuntsu Ne A Siyasa Da Yake Sauya Sheƙa Daga Nan Zuwa Can – Ganduje

MASU ALAKA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Labarai

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Next Post
Nasarar Tsarin CBN Na Samar Da Kudaden Habaka Tattalin Arzikin Nijeriya

Nasarar Tsarin CBN Na Samar Da Kudaden Habaka Tattalin Arzikin Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.