ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Boko Haram Sun Kashe Masunta A Tafkin Chadi

by Muhammad
4 years ago
'Yan

‘Yan ta’addar Boko Haram sun kai hari kan masuntan Nijar, inda suka yi awon gaba da wasu tare da kashe wasu a yankin tafkin Chadi da ke Jamhuriyar Nijar, kamar yadda wata majiya ta bayyana.

‘Yan ta’addar sun yi nasarar kashe masunta da dama daga tsibirin Kwatar Kaoulaha da ke yankin Diffa a ranar Lahadi zuwa Litinin, inda suka yi wa wasu yankan rago tare da yin garkuwa da wasu saboda rashin bin umarnin da aka ba su na barin yankin, kamar yadda masunta suka shaida wa kamfanin dillancin labarai na AFP.

  • An Kashe ‘Yan Boko Haram 49 A Sansaninsu 3 Yayin Luguden Wuta Ta Sama
  • Sojoji Sun Kashe Mayakan Boko Haram 6, Sun Kama Wasu A Borno

“An kashe masunta da yawa tare da yin garkuwa da wasu da mayakan Boko Haram masu biyayya ga Baakura Buduma suka yi garkuwa da su saboda sun gaza ficewa daga yankin kamar yadda aka umarce su,” in ji wani masunta, Kallah Sani, yayin da yake magana kan wani shugaban kungiyar Boko Haram na yankin.

ADVERTISEMENT

Sani bai iya bayar da takamaiman adadin wadanda suka mutu ba amma ya ce wadanda suka tsere ba, sun shaida masa masunta da dama suna tsibirin a lokacin da aka kai harin.

Sani yana cikin masunta kimanin 300 da suka yi biyayya ga sanarwar barin aiki na awa daya, inda suka hakura da kama su da sauran dukiyoyinsu ga ‘yan ta’addar.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

“Sun gaya mana cewa za su kwashe duk abin da muka mallaka a matsayin ganima tun lokacin da gwamnatinmu ta kama kudadensu,” kamar yadda ya shaida wa AFP.

A ranar Juma’ar da ta gabata ne kungiyar Boko Haram ta umarci masuntan wadanda galibinsu ‘yan Arewa maso Yammacin Nijeriya ne da su bar yankin su bar dukiyoyinsu a matsayin ganima ga mayakan, in ji wani masunci, Anas Ibrahim.

“Su (Boko Haram) sun zo ne da kwale-kwale masu gudu guda biyu, suka umarce mu da mu bar tsibirin, kada mu dauki komai sai kayan da muke da su,” Ibrahim ya shaida wa AFP.

“Masu tayar da kayar bayan sun dawo ne a ranar Lahadi inda suka kashe wadanda suka samu, tare da lalata kwale-kwalen su na kamun kifi da hana su tserewa,” in ji shi.

Wata majiyar tsaron Nijeriyar ta kuma tabbatar da faruwar lamarin da kuma kashe-kashen, inda ta ce ‘yan ta’addar sun ji haushin yadda Nijar ta kama masu sayar musu da abinci da wani mai safarar kudi.

Gwamnatin Nijar ba ta amsa kiraye-kirayen neman tabbaci ba.

Sai dai wani jami’in yankin Nijar daga yankin ya shaidawa kamfanin dillancin labaran Faransa na AFP cewa ‘yan jihadin sun umarci mazauna yankin da su fice daga tsibirin tare da kashe wadanda ba su yi ba.

“Na ga gawawwaki 11 da suka hada da na masunta kuma a cikinsu akwai ‘yan Nijeriya uku, sauran ‘yan Nijar ne,” inji majiyar.

“Sun ce akwai wasu mace-mace a tsibirin.”

Fadin tafkin Chadi mai fadin fadama ya ratsa kan iyakokin Nijeriya da Nijar da Kamaru da Chadi, kuma masu jihadi sun yi amfani da kananan tsibiran da suke da su a matsayin mafaka.

A shekarar 2014 ne kungiyar Boko Haram ta kwace tsibiran da ke tafkin Chadi bayan munanan hare-hare, lamarin da ya tilastawa masunta tserewa daga gidajensu. Har yanzu dai kungiyar Boko Haram na rike da tsibiran da ke gefen tafkin na Nijar.

A shekarar 2020, kungiyar Islamic State West Africa Province, wacce ta balle daga Boko Haram, ta kwace mafi yawan yankunan da Boko Haram ke iko da su, tare da barin masunta su komen.

'Yan
Muhammad
+ postsBio
  • Muhammad
    Yadda Na Tsira Daga Cutar Mashaƙo A Katsina: “Na Fara Da Tsartuwar Jini Tare Da Yawu”
  • Muhammad
    An Naɗa Yusuf Nasidi Nasir A Matsayin Talban Barayan Kano
  • Muhammad
    Wani Kamfani Ya Tallafa Wa Masu Sana’ar Shayi A Kano
  • Muhammad
    Kosan Waka Ya Rasu, Gwamnan Kano Ya Jajanta Wa Iyalansa

MASU ALAKA

'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina
Labarai

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare
Labarai

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Next Post
Nasarar Tsarin CBN Na Samar Da Kudaden Habaka Tattalin Arzikin Nijeriya

Nasarar Tsarin CBN Na Samar Da Kudaden Habaka Tattalin Arzikin Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.