• English
  • Business News
Friday, October 24, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Uwargidan Tinubu Ta Ƙaddamar Da Ɗakin Karatu Na E-learning A Zamfara

by Hussein Yero
22 hours ago
Ɗakin

Uwargidan shugaban ƙasa, Sanata Remi Tinubu, ta ƙaddamar da ɗakin karatu na zamani na E-learning a Gusau, babban birnin Jihar Zamfara.

Uwargidan gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal ce, ta wakilci Sanata Remi Tinubu a wajen taron.

  • An Kammala Taron JKS Inda Aka Amince Da Shawarwari Kan Shirin Ci Gaban Kasar Sin Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 15
  • Gwamna Abba Ya Jaddada Mubaya’arsa Ga Kwankwaso 

Ta yaba da wannan shiri na ilimin zamani da Gwamnatin Tarayya ta kawo, inda ta ce zai taimaka wajen bunƙasa ci gaban ƙasa baki ɗaya.

Hajiya Huriyya ta ce wannan ɗakin karatu na zamani na E-learning na daga cikin waɗanda aka kafa a jihohi 10 a ƙasar nan, ƙarƙashin shirin Renewed Hope Initiative tare da haɗin gwiwar Hukumar Bunƙasa Fasahar Sadarwa ta Ƙasa (NITDA).

Ta bayyana cewa, shirin ba wai game da fasaha kawai ba ne, yana nufin ƙarfafa matasa da buɗe musu sabbin hanyoyin ilimi da ƙirƙire-ƙirƙire a Jihar Zamfara da ƙasar baki ɗaya.

LABARAI MASU NASABA

Gombe Ta Ƙulla Yarjejeniya Da Rano Air Don Fara Jigila Tsakanin Abuja Zuwa Gombe

Tinubu Ya Sauya Hafsoshin Tsaron Nijeriya

Ta ce, ta hanyar wannan E-library, ɗalibai, malamai da masu bincike za su samu damar amfani da bayanai da ilimin zamani cikin sauƙi.

A cewarta, Renewed Hope Initiative wanda Sanata Oluremi Tinubu ke jagoranta, na da manufar tallafa wa ilimi, ƙirƙire-ƙirƙire da ci gaban al’umma.

Wannan ɗakin karatu, in ji ta, alamar hangen nesan uwargidan shugaban ƙasa ne wajen inganta ilimi a Nijeriya.

Ta gode wa ma’aikatar sadarwa, ƙirƙire-ƙirƙire da tattalin arziƙin zamani, da kuma NITDA, saboda yadda suka aiwatar da aikin cikin nasara.

Ta kuma yaba wa mijinta, Gwamna Dauda Lawal, bisa jajircewarsa wajen kawo ci gaba a ɓangaren ilimi a Zamfara.

A nasa jawabin, Daraktan NITDA, Kashifu Inuwa, ya buƙaci ɗalibai da malamai a Zamfara da su yi amfani da wannan ɗakin karatu yadda ya kamata domin amfaninsu.

Shi ma Kwamishinan Ilimi na Kimiyya da Fasaha, Mallam Wadatau Madawaki, wanda Sakatariyar Dindindin Maryam Shantali ta wakilta, ya ce aikin ya yi daidai da manufofin Gwamna Dauda Lawal wanda tun zuwansa mulki ya bai wa ilimi fifiko.

Ta ƙara da cewa, a madadin ma’aikatar ilimi da al’ummar Zamfara, suna godiya ga Uwargidan shugaban ƙasa, Sanata Oluremi Tinubu, saboda kawo wannan shiri mai amfani.

Ta tabbatar da cewa ɗalibai, malamai, da masu bincike za su yi amfani da wannan ɗakin karatu yadda ya dace domin amfanin ilimi a jihar.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Gombe Ta Ƙulla Yarjejeniya Da Rano Air Don Fara Jigila Tsakanin Abuja Zuwa Gombe
Labarai

Gombe Ta Ƙulla Yarjejeniya Da Rano Air Don Fara Jigila Tsakanin Abuja Zuwa Gombe

October 24, 2025
Irin Ministocin Da ‘Yan Nijeriya Ke Tsammani Daga Gwamnatin Tinubu
Manyan Labarai

Tinubu Ya Sauya Hafsoshin Tsaron Nijeriya

October 24, 2025
Ɗan’uwa Ya Kwaƙule Idanuwan Ƙanwarsa Don Yin Tsafin Neman Kuɗi A Bauchi
Labarai

Ɗan’uwa Ya Kwaƙule Idanuwan Ƙanwarsa Don Yin Tsafin Neman Kuɗi A Bauchi

October 24, 2025
Next Post
Harkokin Ciniki Da Zuba Jari Tsakanin Sin Da Afirka Sun Samu Ci Gaba Mafi Girma a Shekaru 5 Da Suka Gabata

Harkokin Ciniki Da Zuba Jari Tsakanin Sin Da Afirka Sun Samu Ci Gaba Mafi Girma a Shekaru 5 Da Suka Gabata

LABARAI MASU NASABA

Gombe Ta Ƙulla Yarjejeniya Da Rano Air Don Fara Jigila Tsakanin Abuja Zuwa Gombe

Gombe Ta Ƙulla Yarjejeniya Da Rano Air Don Fara Jigila Tsakanin Abuja Zuwa Gombe

October 24, 2025
Shugaban Kasar Sin Zai Halarci Taron APEC Da Ziyarar Aiki A Korea Ta Kudu

Shugaban Kasar Sin Zai Halarci Taron APEC Da Ziyarar Aiki A Korea Ta Kudu

October 24, 2025
Irin Ministocin Da ‘Yan Nijeriya Ke Tsammani Daga Gwamnatin Tinubu

Tinubu Ya Sauya Hafsoshin Tsaron Nijeriya

October 24, 2025
Ɗan’uwa Ya Kwaƙule Idanuwan Ƙanwarsa Don Yin Tsafin Neman Kuɗi A Bauchi

Ɗan’uwa Ya Kwaƙule Idanuwan Ƙanwarsa Don Yin Tsafin Neman Kuɗi A Bauchi

October 24, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025 Sanata Uba Sani: Mai Haɗa Kan Al’ummar Da Suka Rarrabu

Gwarzon Gwamnan Shekarar 2025, Injiniya Abdullahi Sule

October 24, 2025
Ƴansanda Sun Sake Kama Sowore Bayan An Bayar Da Belinsa

Ƴansanda Sun Sake Kama Sowore Bayan An Bayar Da Belinsa

October 24, 2025

Gwarzon Gwamnan 2025 Sanata Uba Sani: Mai Haɗa Kan Al’ummar Da Suka Rarrabu

October 24, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Sheriff Oboreɓwori: Gwamnan Da Ya Ginu Kan Tabbatar Da Zaman Lafiya Da Ci Gaban Al’umma

October 24, 2025
An Kafa Cibiyoyi 296 Na Koyon Fasahar Zamani A Faɗin Nijeriya

An Kafa Cibiyoyi 296 Na Koyon Fasahar Zamani A Faɗin Nijeriya

October 24, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Ma’aikatan INEC Uku Da Wasu

Ƴan Bindiga Sun Sace Ma’aikatan INEC Uku Da Wasu

October 24, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.