• English
  • Business News
Friday, November 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Majalisar Wakilai Ta Yi Tir Da Harin Da Aka Kai Wa Tawagar Ɗan Majalisar Neja

by Abubakar Sulaiman
8 hours ago
Wakilai

Majalisar Wakila ta nuna ƙin amincewa da kakkausar murya kan harin da wasu ƴan bindiga suka kai wa tawagar ɗan majalisa mai wakiltar mazaɓar Borgu/Agwara ta jihar Neja, Hon. Jafaru Mohammed Ali, wanda ya yi sanadiyyar mutuwar jami’an tsaro da dama tare da jikkatar wasu.

Majalisar ta bayyana harin a matsayin mummunan aika-aikar ta’addanci da rashin imani, tana mai nuna alhini kan rayukan da suka salwanta tare da alƙawarin tallafawa duk wani yunkuri na kama masu laifin don su fuskanci hukunci.

  • Gwamnatin Neja Ta Bayar Da Hutun Kwanaki 2 Don Zaɓen Ƙananan Hukumomi
  • Majalisar Kano Na Tattauna Batun Fara Amfani Da Harshen Hausa A Wurin Koyarwa A Makarantu 

Harin ya faru ne a ranar Talata da rana a kan hanyar Lumma–Babanna da ke ƙaramar hukumar Borgu ta jihar Neja, wacce ta shahara da matsalar hare-haren ƴan fashi da kuma ƙungiyoyin ɓa ɓarayi masu ɗauke da makamai daga iyakar ƙasashen dake makwabtaka da Nijeriya. Rahotanni sun ce harin ya auku tsakanin ƙarfe 1:00 da 2:00 na rana, a yayin da tawagar ta isa garin Babanna, kusa da iyakar Jamhuriyar Benin.

Wannan sanarwa da mai magana da yawun majalisar, Akin Rotimi, ya fitar a ranar Juma’a ya tabbatar da cewa an kashe jami’an tsaro da dama, wasu kuma sun ji rauni, kuma motocin sun lalace.

Majalisar ta bayyana cewa Hon. Ali na kan aikin mazaɓarsa lokacin da iftila’in ya faru, tana mai jaddada cewa irin waɗannan al’amura na nuna yadda ƴan majalisa ke shiga wurare masu haɗari don tabbatar da aiyuka ga jama’arsu.

LABARAI MASU NASABA

Yadda PDP Ta Yi Asarar Kudancin Kaduna

Jerin Gwarazan Taurarinmu!

“Wannan mummunan hari ya yi sanadiyyar mutuwar jaruman jami’an tsaro da suka sadaukar da rayukansu wajen kare shi,” in ji sanarwar.

Majalisar ta yi ta’aziyya ga iyalan waɗanda suka mutu, da hukumomin tsaro, da al’ummar jihar Neja, tare da yi wa waɗanda suka ji rauni fatan samun sauƙin cikin gaggawa.

A ƙarshe, Majalisar Wakilai ta sake tabbatar da jajircewarta wajen ganin an tabbatar da tsaron jama’a da jami’an gwamnati. Ta yi alƙawarin ci gaba da bai wa ɓangaren zartarwa da hukumomin tsaro goyon bayan doka wajen yaƙi da ta’addanci, da fashi da makami, da sauran nau’o’in laifuka da ke barazana ga zaman lafiyar ƙasar.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

APC Da Uba Sani Ba Su Lashe Zaben Gwamnan Kaduna Ba -PDP
Labarai

Yadda PDP Ta Yi Asarar Kudancin Kaduna

November 7, 2025
Jerin Gwarazan Taurarinmu!
Rahotonni

Jerin Gwarazan Taurarinmu!

November 7, 2025
‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri 4, Sun Ƙwato Makamai A Filato
Labarai

Zaben Kananan Hukumomi A Neja Ya Bar Baya Da Kura

November 7, 2025
Next Post
GORON JUMA’A

GORON JUMA'A

LABARAI MASU NASABA

An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi

An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi

November 7, 2025
Kasar Sin Za Ta Dage Dakatar Da Shigo Da Waken Soya A Kan Kamfanonin Amurka Uku 

Kasar Sin Za Ta Dage Dakatar Da Shigo Da Waken Soya A Kan Kamfanonin Amurka Uku 

November 7, 2025
Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya

Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya

November 7, 2025
An Yi Kira Da A Zurfafa Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka Don Bunkasa Masana’antu A Sassan Afirka

An Yi Kira Da A Zurfafa Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka Don Bunkasa Masana’antu A Sassan Afirka

November 7, 2025
APC Da Uba Sani Ba Su Lashe Zaben Gwamnan Kaduna Ba -PDP

Yadda PDP Ta Yi Asarar Kudancin Kaduna

November 7, 2025
Kasar Sin Ta Musanta Zargin Da Wakilin Amurka Ya Yi Game Da Batun Sauyin Yanayi

Kasar Sin Ta Musanta Zargin Da Wakilin Amurka Ya Yi Game Da Batun Sauyin Yanayi

November 7, 2025
Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Halarci Taron COP30 A Brazil

Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Halarci Taron COP30 A Brazil

November 7, 2025
Jerin Gwarazan Taurarinmu!

Jerin Gwarazan Taurarinmu!

November 7, 2025
‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri 4, Sun Ƙwato Makamai A Filato

Zaben Kananan Hukumomi A Neja Ya Bar Baya Da Kura

November 7, 2025
Gwamnatin Zamfara Ta Ɗauki Malaman Makaranta 500 Aiki

Gwamnatin Zamfara Ta Ɗauki Malaman Makaranta 500 Aiki

November 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.