• English
  • Business News
Saturday, October 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Soma Shari’ar Matashin Da Ya Yi Sanadin Yanke Kafar Wata Yarinya A Sakkwato 

by Sadiq
3 years ago
in Manyan Labarai
0
An Soma Shari’ar Matashin Da Ya Yi Sanadin Yanke Kafar Wata Yarinya A Sakkwato 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Al’umma dai sun zura ido su ga yadda zata kaya a shari’ar da aka fara ta wani matashi dan shekara 18 mai suna Aliyu Sanusi Umar, wanda ya yi sanadin yanke kafar wata yarinya daliba ‘yar shekara 16 Fatima Sulaiman a Jihar Sakkwato.

Shari’ar dai ta dauki hankalin jama’a sobada ana ganin kamar ana sako-sako da lamarin, musamman duba da fitowar da aka yi kotu a baya wanda ba a yi zaman shari’ar ba.

  • Magidanci Ya Nemi Matarsa Ta Biya Naira Miliyan 1.6 Kafin Ya Sake Ta A Kaduna
  • Shugaba Xi Ya Ba Da Umarnin Ba Da Fifiko Ga Ceton Rayuka A Gundumar Luding Da Girgizar Kasa Ta Aukawa

Labarin Fatima Sulaiman daliba ‘yar shekara 16 da ta rasa kafarta sanadiyyar bige ta da mota da Aliyu Sanusi Umar ya yi, lokacin da suke murnar kammala jarabawar NECO, ba bakon abu bane ga duk mai amfani da kafafen sada zumunta ko kafafen watsa labarai.

Fatima Sulaiman, ta ce yaron ba dan makarantar su bane kuma daga farko sai da aka kore shi da ya shigo makarantar inda daliban ke wasan murnar kammala jarabawa.

Ta ce bayan an tashi makarantar sun fito waje sai yaran da ke wasan suka dauko motoci suna wasa.

Labarai Masu Nasaba

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

A cewarta su kuma suna zaune su uku suna jiran a zo daukar su sai motar ta nufo wurin da suke zaune, biyu daga cikin daliban da ke zaune suka gudu ita ma ta yunkura ta gudu sai ta fadi motar ta murkushe ta, ta ce tana neman a yi mata adalci ga halin da ta samu kanta ciki.

Bayan da jama’a suka yi ta yada hotonan wata fitowa kotun da aka gurfanar da yaron wadanda suke cike da shakku, yanzu dai kotun ta zauna cikin tsattsauran tsaro, inda aka tuhumi yaron da laifuka uku da suka hada da tukin mota ba tare da lasisi ba, tukin ganganci da kuma yin sanadin samuwar mummunan rauni.

A zaman kotun dai lauya mai kare wanda ake zargi, Jacob Ochidi SAN, ya nemi bukatar bayar da yaron beli domin a cewarsa laifukan da ake tuhumarsa ba manyan laifukan da ba a bayar beli ba ne.

“Doka ta ce ana bayar da beli ga laifukan da ba manyan laifuka sai in akwai wasu kwararan dalilai na kin bayar da shi, to a wannan shara’ar babu dalilan da kan iya hana a bayar da shi beli, muna tausaya wa yarinyar da iyayenta a kan yanayin da suka shiga, dukanmu ‘yan Adam muke abin da ya faru abin tausayi ne don haka muke tausaya wa iyayenta”

Sai dai lauyan masu shigar da kara, Jamilu Malami, ya kalubalanci wannan bukatar.

Ya ce, “lauyoyin yaron sun shigar da bukatar beli amma dai bangaren gwamnati da bangaren yarinyar sun ki aminta, domin sun samu wani bayanin sirri cewa yaron ya samu gurbin karatu a kasar waje don haka akwai yiwuwar zai iya barin kasar nan kowane lokaci, sannan kuma akwai yiwuwar cewa ko don lafiyar shi ya kamata a bar shi gidan gyaran hali har kura ta kwanta.”

Alkalin kotun majistire, Mariya Haruna Dogon Daji, ta dage zaman zuwa 8 ga wannan wata don yanke hukunci a kan bayar da belin ko akasin haka.

Mutane da dama na ganin dacewar hukunta yaron don zama izina ga na baya masu irin wannam dabi’a tasa ta wasa da mota.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BeliHukunciKotuMatashiMatashiyaRasa KafaSakkwatoShari'aTuhuma
ShareTweetSendShare
Previous Post

Magidanci Ya Nemi Matarsa Ta Biya Naira Miliyan 1.6 Kafin Ya Sake Ta A Kaduna

Next Post

Mutane 8 Sun Mutu A Ruwa A Jihar Jigawa

Related

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram
Manyan Labarai

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

26 minutes ago
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce
Manyan Labarai

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

2 hours ago
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP
Manyan Labarai

Tinubu Zai Ziyarci Jos Domin Halartar Jana’izar Mahaifiyar Shugaban Jam’iyyar APC Na Ƙasa

22 hours ago
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12
Manyan Labarai

PENGASSAN Ta Yi Watsi Da Tayin Dangote Na Biyan Ma’aikata Albashin Shekaru 5 Ba Tare Da Yin Aiki Ba

1 day ago
NAFDAC Ta Rufe Manyan Shaguna 2 Na Ƴan China A Abuja
Manyan Labarai

NAFDAC Ta Rufe Manyan Shaguna 2 Na Ƴan China A Abuja

1 day ago
Nijeriya A Shekara 65: Kwan-gaba Kwan-baya A Sha’anin Tsaro Da Siyasa Da Zamantakewa
Manyan Labarai

Nijeriya A Shekara 65: Kwan-gaba Kwan-baya A Sha’anin Tsaro Da Siyasa Da Zamantakewa

2 days ago
Next Post
Mutane 8 Sun Mutu A Ruwa A Jihar Jigawa

Mutane 8 Sun Mutu A Ruwa A Jihar Jigawa

LABARAI MASU NASABA

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

October 4, 2025
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

October 4, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

October 4, 2025
Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

October 4, 2025
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

October 4, 2025
Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

October 4, 2025
Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

October 4, 2025
Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

October 4, 2025
Xi Da Takwaransa Na Bangladesh Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kulla Alakar Kasashensu

Xi Da Takwaransa Na Bangladesh Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kulla Alakar Kasashensu

October 4, 2025
An Nada Adamar Kamaye Sarautar Jakadiya A Kasar Ghana

An Nada Adamar Kamaye Sarautar Jakadiya A Kasar Ghana

October 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.