ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, December 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yaushe Ne Ƙarshen Rikicin Yajin Aiki Tsakanin ASUU Da Gwamnatin Tarayya A Nijeriya?

by Sulaiman
4 weeks ago
ASUU

Masu karatu barkanmu, yau shafin na mu wani muhimmin batu ya zakulo mana, wato Kungiyar Malaman Jami’o’i, ASUU! Wannan kungiya tsawon shekaru ta dade tana zama manyan kanun labarai a manyan gidajen labarai da suka hada da gidajen talabijin, rediyo, jaridu da sauran kafofin watsa labarai a fadin Nijeriya. 

 

Mahimmancin kungiyar ya kai matukar kololuwa a idon iyaye da ɗaliban jami’o’in Nijeriya. ASUU, kungiya ce ta Malaman jami’o’in tarayya da jihohi a fadin kasar.

ADVERTISEMENT

 

Duk wani yunkuri da ka iya sanya ASUU ta yi barazanar tsunduma yajin aiki, iyaye da daliban Jami’a ba sa maraba da wannan yunkurin domin yana kawo cikas ga ci gaban karatun daliban.

LABARAI MASU NASABA

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

 

Kungiyar ASUU, tana rajin kare hakkin walwalar mambobinta, da samar da ababen more rayuwa don samun ingantaccen yanayin koyarwa, inda duk wannan hakkokin take neman su a wurin gwamnati.

 

Don haka, kungiyar ke fafutuka da gwagwarmaya kullum a wurin gwamnati da nufin kare muradunta da bukatunta.

 

Wacece ASUU kuma yaushe aka kafata?

Ƙungiyar Malaman Jami’o’i (ASUU) ta samo asali ne daga Ƙungiyar Malaman Jami’o’i ta Nijeriya (NAUT). An kafa ƙungiyar NAUT a shekarar 1965, wadda ta ƙunshi ma’aikatan ilimi a Jami’ar Ibadan, Jami’ar Nijeriya, Nsukka, Jami’ar Ahmadu Bello, Zariya, Jami’ar Ife, Ile-Ife da Jami’ar Legas, da ke Legas.

 

NAUT ta fi mayar da hankali kan kyautata yanayin hidimar mambobinta, da kuma walwalar zamantakewa da tattalin arziki da siyasa ta ƙasar. Sai dai, a cewar Attahiru Jega, ƙungiyar NAUT ba ta ɗauki wani matsayi mai muhimmanci ba kan batutuwan ƙasa ko siyasa.

 

A ra’ayin masana, NAUT ta fi kusa da tsarin kungiyoyi matsakaita. Ba kasafai take fitar da wata sanarwa ta bai ɗaya ba, sannan kuma, ba ta tsaurara wa gwamnati kan bukatunta saboda tausayawa gwamnatin.

 

Sauye-sauye da aka fara samu a ɓangaren zamantakewa ta siyasa da alkiblar tattalin arziki da kasar tafara fuskanta, wani masani Eskor Toyo, ya bayyana cewa, manufofin NAUT ba su dace da wannan zamani ba, akwai bukatar a yi mata kwaskwarima, inda ya ce gwagwarmayar kungiyar zai fi dace wa a kira ta da ASUU.

 

An kafa ASUU a shekarar 1978, a lokacin da kakar kasuwar man fetur ta fara raguwa, inda ƙasar ta fara girbar kuskuren shugabanninta na kin yin amfani da arzikin da aka samu na man fetur wurin kafa masana’antu domin samar da jin dadi da walwalar jama’a.

 

Mulkin kama-karya na soja ya yi tasiri matuka wurin gurgunta ‘yancin al’ummar Nijeriya. Fannin ilimi da jami’o’in Nijeriya suka rasa ‘yancin da suke da shi, sabida mulkin kama-karya na soja. Tallafin ilimi, da kuma na jami’o’i, ya koma ƙamas. Waɗannan abubuwan su suka kara taimakawa ASUU ta fara tsoma baki a fannin siyasa tun daga shekarar 1980.

 

Jagoraorin ASUU suka zama masu kaushi da tsauri ga gwamnati, inda kungiyar a lokacin ta fi damuwa da manyan batutuwan ƙasa, kuma ƙungiyar ta tsaya tsayin daka kan manufofin dakile zalunci da rashin dimokuraɗiyya na ƙasar.

…. za mu ci gaba a mako na gaba

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta
Manyan Labarai

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tinubu
Manyan Labarai

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani
Manyan Labarai

Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

December 21, 2025
Next Post
ASUU

Wasu Kura-kurai Da Matan Aure Ke Yi Ke Sa 'Yan Aiki Aure Mazajensu

LABARAI MASU NASABA

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

December 21, 2025
Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

December 21, 2025
Tinubu

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025
Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

December 21, 2025
Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

December 21, 2025
Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

December 21, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

An Cafke Wani Mutum Da Ya Lakada Wa Dansa Duka Har Lahira A Edo

December 21, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.