ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wasu Kura-kurai Da Matan Aure Ke Yi Ke Sa ‘Yan Aiki Aure Mazajensu

by Bilkisu Tijjani and Sulaiman
7 months ago
Aure

Ba sabon abu bane a ji cewa ‘yar aiki ta aure maigida ko kuma ta kori uwargidan ma gaba daya.

Wannan matsalar tana faruwa ba tun yanzu ba, wanda kuma har wannan lokacin wasu matan sun kasa ganewa su ne ke jawo hakan da kansu har abin ya zo ya dame su.

Mafi yawan mazaje sun fi son ‘yar aiki mace ta kula da ayyukan cikin gida maimakon namiji saboda da dalilai na tsaro. Wasu matan kuma sun gwammace namiji ya yi musu ayyukan gidan domin gudun kada su kawo wacce za ta iya musu illa.

ADVERTISEMENT

Amma da yake maza sun fi karfin su a daukar matsayi hakan ya sa wasu matan suke saduda amma ba domin suna so ba. Sai dai kuma matan ke jawo matsalar da suke fuskanta da ‘yan aikinsu da kansu, domin su ne suke zabar wacce za ta yi musu aikin ba mazajensu ba.

Ga kura kuren da mata suke yi har ‘yan aikin su ke zama kishiyoin su kamar haka:

LABARAI MASU NASABA

Nasiha Ga Uwargida Kan Zafin Kishi (1)

Abin Da Yake Kashe Matanmu Na Hausawa

1. Dauko wacce ta fita wayo: Mata da dama idan sun tashi dauko ‘yar aiki a rashin sani sai su dauko macen da ta fi su wayo a badini amma a zahiri ta yi kama da doluwa.

Irin wadannan matan ba sa yadda su fito da fuskar kyawunsu na asali idan za su je neman aiki, sai su yi biji-biji yadda mace idan ta ganta tamkar wata abar tausayi. Amma da zarar ta saki jiki sai ta fara fito da halittunta yadda duk wanda ya ganta ta yi.

2. Saka su ayyuka na musamman: Akwai wasu ayyukan da duk rashin son aikin mace ita ya kamata ta yi wa mijinta shi amma ba ta saka wata ta yi masa ba muddin dai ba ‘yar cikinsa bace.

Ayyuka irin na gyaran dakin miji. Yi wa miji girki fita da miji sayayya duk bai dace mace ta bari ‘yar aikinta ta ke mata ba.

3. Barin ‘yar aiki ta fahimci matsalarki da mijinki: Muddin za ku bari ‘yar aiki tana fahimtar abin da yake hada ki da mijinki sabani to tabbas za ta iya amfani da wannan damar ita kuma ta rika dadada masa da abin, yadda har zai fara sha’awar ina ma ita ce matarsa. Don haka ki kiyaye hira da ‘yar aiki akan matsalolinki da mijinki.

Za Mu Ci Ci Gaba Mako Mai Zuwa Idan Allah Ya Kai Mu

Aure
Bilkisu Tijjani
+ posts Bio
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    Yadda Ake Wainar Masara Da Miyar Yaji
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    Hanyoyin Hada Humra Mai Kamshi
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    Yadda Ake Miyar Margi Da Kifin Tarwad
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    A Matsayinki Na Mace, Kada Ki Yi Wasa Da Wadannan Abubuwa
Aure
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
  • Sulaiman
    Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje
  • Sulaiman
    Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa
  • Sulaiman
    Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

MASU ALAKA

Wasu Abubuwa Da Ke Sa Maza Hana Mata Fita Unguwa (Uwargida)
Uwargida Sarautar Mata

Nasiha Ga Uwargida Kan Zafin Kishi (1)

June 21, 2026
Abin Da Yake Kashe Matanmu Na Hausawa
Uwargida Sarautar Mata

Abin Da Yake Kashe Matanmu Na Hausawa

May 30, 2026
Kafin Ki Nemi Saki, Nemi Amsar Waɗannan Tambayoyi Da Kanki
Uwargida Sarautar Mata

Kafin Ki Nemi Saki, Nemi Amsar Waɗannan Tambayoyi Da Kanki

May 24, 2026
Next Post
Gyaran Gashi Ya Yi Kyau Da Laushi

Yadda Za Ki Kara Wa Kanki Tsawon Gashi

LABARAI MASU NASABA

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.