ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yaushe Ne Ƙarshen Rikicin Yajin Aiki Tsakanin ASUU Da Gwamnatin Tarayya A Nijeriya?

by Sulaiman
7 months ago
ASUU

Masu karatu barkanmu, yau shafin na mu wani muhimmin batu ya zakulo mana, wato Kungiyar Malaman Jami’o’i, ASUU! Wannan kungiya tsawon shekaru ta dade tana zama manyan kanun labarai a manyan gidajen labarai da suka hada da gidajen talabijin, rediyo, jaridu da sauran kafofin watsa labarai a fadin Nijeriya. 

 

Mahimmancin kungiyar ya kai matukar kololuwa a idon iyaye da ɗaliban jami’o’in Nijeriya. ASUU, kungiya ce ta Malaman jami’o’in tarayya da jihohi a fadin kasar.

ADVERTISEMENT

 

Duk wani yunkuri da ka iya sanya ASUU ta yi barazanar tsunduma yajin aiki, iyaye da daliban Jami’a ba sa maraba da wannan yunkurin domin yana kawo cikas ga ci gaban karatun daliban.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

 

Kungiyar ASUU, tana rajin kare hakkin walwalar mambobinta, da samar da ababen more rayuwa don samun ingantaccen yanayin koyarwa, inda duk wannan hakkokin take neman su a wurin gwamnati.

 

Don haka, kungiyar ke fafutuka da gwagwarmaya kullum a wurin gwamnati da nufin kare muradunta da bukatunta.

 

Wacece ASUU kuma yaushe aka kafata?

Ƙungiyar Malaman Jami’o’i (ASUU) ta samo asali ne daga Ƙungiyar Malaman Jami’o’i ta Nijeriya (NAUT). An kafa ƙungiyar NAUT a shekarar 1965, wadda ta ƙunshi ma’aikatan ilimi a Jami’ar Ibadan, Jami’ar Nijeriya, Nsukka, Jami’ar Ahmadu Bello, Zariya, Jami’ar Ife, Ile-Ife da Jami’ar Legas, da ke Legas.

 

NAUT ta fi mayar da hankali kan kyautata yanayin hidimar mambobinta, da kuma walwalar zamantakewa da tattalin arziki da siyasa ta ƙasar. Sai dai, a cewar Attahiru Jega, ƙungiyar NAUT ba ta ɗauki wani matsayi mai muhimmanci ba kan batutuwan ƙasa ko siyasa.

 

A ra’ayin masana, NAUT ta fi kusa da tsarin kungiyoyi matsakaita. Ba kasafai take fitar da wata sanarwa ta bai ɗaya ba, sannan kuma, ba ta tsaurara wa gwamnati kan bukatunta saboda tausayawa gwamnatin.

 

Sauye-sauye da aka fara samu a ɓangaren zamantakewa ta siyasa da alkiblar tattalin arziki da kasar tafara fuskanta, wani masani Eskor Toyo, ya bayyana cewa, manufofin NAUT ba su dace da wannan zamani ba, akwai bukatar a yi mata kwaskwarima, inda ya ce gwagwarmayar kungiyar zai fi dace wa a kira ta da ASUU.

 

An kafa ASUU a shekarar 1978, a lokacin da kakar kasuwar man fetur ta fara raguwa, inda ƙasar ta fara girbar kuskuren shugabanninta na kin yin amfani da arzikin da aka samu na man fetur wurin kafa masana’antu domin samar da jin dadi da walwalar jama’a.

 

Mulkin kama-karya na soja ya yi tasiri matuka wurin gurgunta ‘yancin al’ummar Nijeriya. Fannin ilimi da jami’o’in Nijeriya suka rasa ‘yancin da suke da shi, sabida mulkin kama-karya na soja. Tallafin ilimi, da kuma na jami’o’i, ya koma ƙamas. Waɗannan abubuwan su suka kara taimakawa ASUU ta fara tsoma baki a fannin siyasa tun daga shekarar 1980.

 

Jagoraorin ASUU suka zama masu kaushi da tsauri ga gwamnati, inda kungiyar a lokacin ta fi damuwa da manyan batutuwan ƙasa, kuma ƙungiyar ta tsaya tsayin daka kan manufofin dakile zalunci da rashin dimokuraɗiyya na ƙasar.

…. za mu ci gaba a mako na gaba

ASUU
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • Sulaiman
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • Sulaiman
    Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
  • Sulaiman
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

MASU ALAKA

Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku
Manyan Labarai

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso
Manyan Labarai

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Next Post
ASUU

Wasu Kura-kurai Da Matan Aure Ke Yi Ke Sa 'Yan Aiki Aure Mazajensu

LABARAI MASU NASABA

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.