ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yaushe Ne Ƙarshen Rikicin Yajin Aiki Tsakanin ASUU Da Gwamnatin Tarayya A Nijeriya?

by Sulaiman
6 months ago
ASUU

Masu karatu barkanmu, yau shafin na mu wani muhimmin batu ya zakulo mana, wato Kungiyar Malaman Jami’o’i, ASUU! Wannan kungiya tsawon shekaru ta dade tana zama manyan kanun labarai a manyan gidajen labarai da suka hada da gidajen talabijin, rediyo, jaridu da sauran kafofin watsa labarai a fadin Nijeriya. 

 

Mahimmancin kungiyar ya kai matukar kololuwa a idon iyaye da ɗaliban jami’o’in Nijeriya. ASUU, kungiya ce ta Malaman jami’o’in tarayya da jihohi a fadin kasar.

ADVERTISEMENT

 

Duk wani yunkuri da ka iya sanya ASUU ta yi barazanar tsunduma yajin aiki, iyaye da daliban Jami’a ba sa maraba da wannan yunkurin domin yana kawo cikas ga ci gaban karatun daliban.

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

 

Kungiyar ASUU, tana rajin kare hakkin walwalar mambobinta, da samar da ababen more rayuwa don samun ingantaccen yanayin koyarwa, inda duk wannan hakkokin take neman su a wurin gwamnati.

 

Don haka, kungiyar ke fafutuka da gwagwarmaya kullum a wurin gwamnati da nufin kare muradunta da bukatunta.

 

Wacece ASUU kuma yaushe aka kafata?

Ƙungiyar Malaman Jami’o’i (ASUU) ta samo asali ne daga Ƙungiyar Malaman Jami’o’i ta Nijeriya (NAUT). An kafa ƙungiyar NAUT a shekarar 1965, wadda ta ƙunshi ma’aikatan ilimi a Jami’ar Ibadan, Jami’ar Nijeriya, Nsukka, Jami’ar Ahmadu Bello, Zariya, Jami’ar Ife, Ile-Ife da Jami’ar Legas, da ke Legas.

 

NAUT ta fi mayar da hankali kan kyautata yanayin hidimar mambobinta, da kuma walwalar zamantakewa da tattalin arziki da siyasa ta ƙasar. Sai dai, a cewar Attahiru Jega, ƙungiyar NAUT ba ta ɗauki wani matsayi mai muhimmanci ba kan batutuwan ƙasa ko siyasa.

 

A ra’ayin masana, NAUT ta fi kusa da tsarin kungiyoyi matsakaita. Ba kasafai take fitar da wata sanarwa ta bai ɗaya ba, sannan kuma, ba ta tsaurara wa gwamnati kan bukatunta saboda tausayawa gwamnatin.

 

Sauye-sauye da aka fara samu a ɓangaren zamantakewa ta siyasa da alkiblar tattalin arziki da kasar tafara fuskanta, wani masani Eskor Toyo, ya bayyana cewa, manufofin NAUT ba su dace da wannan zamani ba, akwai bukatar a yi mata kwaskwarima, inda ya ce gwagwarmayar kungiyar zai fi dace wa a kira ta da ASUU.

 

An kafa ASUU a shekarar 1978, a lokacin da kakar kasuwar man fetur ta fara raguwa, inda ƙasar ta fara girbar kuskuren shugabanninta na kin yin amfani da arzikin da aka samu na man fetur wurin kafa masana’antu domin samar da jin dadi da walwalar jama’a.

 

Mulkin kama-karya na soja ya yi tasiri matuka wurin gurgunta ‘yancin al’ummar Nijeriya. Fannin ilimi da jami’o’in Nijeriya suka rasa ‘yancin da suke da shi, sabida mulkin kama-karya na soja. Tallafin ilimi, da kuma na jami’o’i, ya koma ƙamas. Waɗannan abubuwan su suka kara taimakawa ASUU ta fara tsoma baki a fannin siyasa tun daga shekarar 1980.

 

Jagoraorin ASUU suka zama masu kaushi da tsauri ga gwamnati, inda kungiyar a lokacin ta fi damuwa da manyan batutuwan ƙasa, kuma ƙungiyar ta tsaya tsayin daka kan manufofin dakile zalunci da rashin dimokuraɗiyya na ƙasar.

…. za mu ci gaba a mako na gaba

ASUU
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
  • Sulaiman
    Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
  • Sulaiman
    Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
  • Sulaiman
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

MASU ALAKA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya
Manyan Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya

June 3, 2026
Next Post
ASUU

Wasu Kura-kurai Da Matan Aure Ke Yi Ke Sa 'Yan Aiki Aure Mazajensu

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.