ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, December 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yansanda Sun Ƙaryata Shirin Kai Harin Ta’addanci Jihar Kogi

by Sani Anwar and Sulaiman
3 weeks ago
Kogi

Rundunar ‘Yansandan Jihar Kogi, ta bukaci mazauna yankin da su yi watsi da rahotannin da ke yawo a kafafen sada zumunta na yanar gizo, kan batun wani harin ‘yan bindiga da ake zargin ‘yan ta’adda na shirin kai wa, musamman a yankin Kogi ta Gabas.

Kwamishinan ‘yansandan jihar, Naziru Bello Kankarofi ne ya bayyana haka, a wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yansandan, CSP William Aya ya fitar a daren ranar Litinin.

  • Tsohon Gwamnan Kaduna, El-Rufai, Ya Fice Daga SDP, Ya Koma ADC
  • Dambarwar Amurka Da Sace ‘Yan Makarantar Kebbi Da Neja: Shugaba Tinubu Ya Yi Rawar Gani

Ya bayyana rahoton a matsayin wanda ba shi da tushe, ballantana asali.

ADVERTISEMENT

Sai dai, rundunar ‘yansandan ta tabbatar wa da jama’a cewa, an samar da dukkanin matakan da suka dace, domin dakile dukkannin wata matsala ta tsaro a fadin jihar.

Har ila yau, sanarwar ta ce; “Muna kira ga jama’a da su kwantar da hankulansu tare da tabbatar da bayanai ta hanyar majiyoyin hukuma, kafin su kai ga yarda da su.

LABARAI MASU NASABA

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

Ya kara da cewa, ya kamata mazauna yankin; su hanzarta kai rahoto ga hukumomin tsaro tare da lura da cewa; “tsaro alhakin kowa da kowa ne.”

CP Kankarofi ya bayar da umarnin tura tawagogin sanin makamar aiki, ciki har da rundunar ‘yansanda ta wayar tafi-da-gidanka, sashen yaki da ta’addanci da sassan leken asiri zuwa wurare masu mahimmanci a fadin jihar.

A cewar sanarwar, an kuma aike da karin wasu karin muhimman kayayyakin tsaro zuwa yankunan da suke da rauni, domin mayar da martani ga duk wani abu da ka iya bijirowa.

Kwanaki dai, kafafen sada zumunta na yanar gizo, sun yi ta yawo da ikirari na harin ‘yan bindiga da ke shirin kai wa a Kogi ta Gabas, bisa zargin “rahoton sirri na ‘yansanda” da ke yawo a tsakanin jami’an tsaro.

Rahoton da aka yada ya bayyana cewa, ‘yan bindiga sun kutsa cikin jihar daga Nasarawa ta Karamar Hukumar Bassa da kuma Jihar Benuwe ta Agatu da Bagana a Karamar Hukumar Omala.

Kazalika, an kuma yi zargin cewa; daliban jami’ar Prince Abubakar Audu da ke Anyigba (PAAU) da makarantar sakandire ta Ochaja da ke Karamar Hukumar Dekina da kuma wasu sassan garin Anyigba ne aka kai harin.

Rundunar ‘yansandan ta sake nanata cewa, babu kamshin gaskiya a wannan labarin, inda kuma ta bukaci daukacin al’umma da su yi watsi da ire-iren wadannan jita-jita.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta
Manyan Labarai

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka
Ra'ayi Riga

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

December 21, 2025
Tinubu
Manyan Labarai

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Next Post
Sin Ta Gina Cibiyoyin Fasahar Aikin Gona Na Gwaji Guda 24 A Afirka

Dogaro Da Noman Gargajiya Kadai Ba Zai Iya Wadatar Da  Nijeriya Ba – Farfesa Rabi'u

LABARAI MASU NASABA

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

December 21, 2025
Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

December 21, 2025
Tinubu

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025
Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

December 21, 2025
Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

December 21, 2025
Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

December 21, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

An Cafke Wani Mutum Da Ya Lakada Wa Dansa Duka Har Lahira A Edo

December 21, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.