ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dogaro Da Noman Gargajiya Kadai Ba Zai Iya Wadatar Da  Nijeriya Ba – Farfesa Rabi’u

by Abubakar Abba and Sulaiman
7 months ago
Noman gargajiya

Darakta a Cibiyar Binciken Aikin Noma ta Jami’ar Ahmadu Bello da ke Zariya, Farfesa Rabi’u Adamu, ya bayyana cewa; dogaro da noman gargajiya kadai, ba zai iya wadadar da kasar nan da abincin da ake bukata ba, musamman duba da karuwar yawan al’ummar da kuma yadda kasar noma ke kara lalacewa.

Ya kara da cewa, kasancewar Nijeriya da ke da yawan al’umma a nahiyar Afirka, amma ana noma tan miliyan 12.4 na Masara ne kadai, wanda hakan ya gaza da tan miliyan 18 da kasar ke bukata.

  • An Yi Jana’izar Sheikh Dahiru Usman Bauchi
  • Sanya Dokar Ta -Ɓaci Kan Tsaro Bai Da Amfani – Datti Baba-Ahmed

Haka zalika, Farfesan ya yi nuni da cewa; za a iya cike wannan gibin ne kadai, idan gwamnatin tarayya ta amince da gabatar da shuka ingantaccen Irin Masara, mai saurin girma tare da kuma jurewa kowane irin yanayi da kuma jurewa kamuwa da kwari da lalata amfanin gona.“Har yanzu, akwai bukatar Nijeriya ta kara yawan adadin amfanin gonar da ake nomawa a kasar,” in ji Farfesan.

ADVERTISEMENT

Hak nan, a kan batun tantamar da wasu ke da ita na shafar lafiyar jama’a wajen amfani da Irin da aka sarrafa a zamanance, wato GMO, Farfesan ya bayyana cewa; hatta amfanin gonar da ake shigowa da shi daga ketare zuwa cikin kasar nan, sai an tabbatar da hukumomin da abin ya shafa sun tantance su, domin tabbatar da cewa; ba za su shafi lafiyar mutane ba, kafin a sahale sayarwa mutane. Ya sanar da cewa, wasu alkaluman bincike sama da 200 da aka gudanar kan nau’in na GMO, Tarayyar Turai da kasar Amurka da kuma wasu kasashen da ke Afrika, sun bayyana cewa; kan nau’in na GMO, wanda hakan ya tabbatar da sahihancin, wannan nau’in tare da kuma sahalewar, ana iya cin amfanin gonar da aka shuka aka kuma noma ba tare da wata matsalar shafar lafiyar jama’a ba.

Kazalika, ya kara da cewa; babu wani rahoto da ya fito daga Hukumar Kula da Lafiya ta Duniya da kuma Sashen Kula da Aikin Noma na Majalisar Dinkin Duniya, suka bayyana cewa; yin amfani da wannan nau’in, na shafar lafiyar jama’a da kuma ta dabbobi.  Ya yi nuni da cewa, a yanzu haka, akwai irin wannan nau’in da ake ci gaba da amfani da shi, wanda aka shuka Masara da Tumatir da Waken Soya, wadanda kuma ake sayarwa a kasuwanin kasar nan.

LABARAI MASU NASABA

Hukumar FAO Ta Samar Da Shirin Kiwon Tarwada A Jihar Gombe

Gwamnatin Tarayya Ta Raba Buhunan Taki Kyauta Ga Manoma 20,160

“Yin amfani da wannan nau’in ne ya bai wa Nijeriya kwarin gwiwar shiga cikin yarjejeniyar Geneba, musamman domin kasar ta bayar da umarnin a rika yin amfani da nau’in a wajen yin noma.

Ya kara da cewa, hatta ita kanta Nijeriya, ta sahale wa manoma amfani da wannan nau’in, wanda a farko ta amince kan yin Auduga samfurin Bt a shekarar 2020 da noman farin Wake samfarin SAMPEA 20T a shekarar 2021, sai kuma noman Masara samfarin Tela maize, a shekarar 2024.

Noman gargajiya
Abubakar Abba
+ posts Bio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Hukumar FAO Ta Samar Da Shirin Kiwon Tarwada A Jihar Gombe
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Dalilin Da Ya Sa Matatar Dangote Ta Kara Habaka Tura Man Fetur
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Manoma 67 Suka Amfana Da Horon Cibiyar  NIHORT
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Dalilan Da Suka Sa Fannin Kiwo Ke Fuskantar Kalubale A Nijeriya —Gwamnatin Tarayya
Noman gargajiya
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya
  • Sulaiman
    Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari
  • Sulaiman
    Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana
  • Sulaiman
    Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

MASU ALAKA

Hukumar FAO Ta Samar Da Shirin Kiwon Tarwada A Jihar Gombe
Noma Da Kiwo

Hukumar FAO Ta Samar Da Shirin Kiwon Tarwada A Jihar Gombe

June 13, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Raba Buhunan Taki Kyauta Ga Manoma 20,160
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Raba Buhunan Taki Kyauta Ga Manoma 20,160

June 12, 2026
Manoma 67 Suka Amfana Da Horon Cibiyar  NIHORT
Noma Da Kiwo

Manoma 67 Suka Amfana Da Horon Cibiyar  NIHORT

June 6, 2026
Next Post
Kuskure Ne Tattaunawa Da Ƴan Bindiga, Yafi Dacewa A Nemi Tallafin Ƙasashen Waje – Obasanjo

Kuskure Ne Tattaunawa Da Ƴan Bindiga, Yafi Dacewa A Nemi Tallafin Ƙasashen Waje - Obasanjo

LABARAI MASU NASABA

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026
Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

June 13, 2026
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.