• English
  • Business News
Tuesday, July 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NIS Da UNODC Sun Gabatar Da Rahoton Binciken Kwararar ‘Yan Nijeriya Zuwa Ƙasashen Ƙetare

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
in Labarai
0
NIS Da UNODC Sun Gabatar Da Rahoton Binciken Kwararar ‘Yan Nijeriya Zuwa Ƙasashen Ƙetare
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar shige da fice ta ƙasa (NIS) tare da haɗin gwiwar Ofishin Majalisar Ɗinkin Duniya da ke yaƙi da shan miyagun ƙwayori da aikata laifuka (UNODC) sun gabatar da rahoton binciken da suka yi a kan ‘yan Nijeriya da ke kwarara zuwa ƙasashen ƙetare.

Rahoton da aka yi masa laƙabi da SOM an ƙaddamar da shi ne a shelkwatan NIS da ke Abuja a ranar Talata.

UNODC

Da yake gabatar da jawabin maraba, shugaban hukumar NIS, CGI, Idris Isa Jere ya bayyana cewa duk wani bincike yana da sakamakon. Don haka suka ƙaddamar da wannan rahoton wanda yake buƙatar ɗaukan mataki bayan an kammala nazari tare da yin aiki da shi.

  • Katafaren Jirgin Ruwa Ya Kife Da Mutane A Kogin Ibi Da Ke Jihar Taraba

CGI Isah Jere, wanda ya samu wakilcin DCG Haliru ya jinjina wa UNODC bisa gudanar da kyakkyawan aiki na samun nasarar bankaɗo yawan ‘yan Nijeriya da ke yin hijira zuwa ƙasashen ƙetare ba bisa ƙa’ida ba.

Labarai Masu Nasaba

Babu Wata Karamar Hukumar Dake Ƙarƙashin Ikon Ƴan Ta’adda A Filato -Gwamna Mutfwang

Matashi Ya Kashe Surukarsa Saboda Shigarta Cikin Sha’anin Aurensu

UNODC

A cewarsa, hukumarsa za ta yi aiki da wannan rahoton wajen yaƙi da safarar ‘yan Nijeriya zuwa ƙasashen ƙetare. Sannan ya yi kira da dukkan jami’an hukumar NIS da su gudanar da ayyukansu kamar yadda doka ta tanada.

A nasa jawabin, wakilin UNODC, Oliver Stolpe ya bayyana cewa an gudanar da wannan bincike ne domin samun nasarar daƙile safarar mutane ba bisa ƙa’ida ba. Ya ce wannan rahoton zai taimaka wa ƙasashe wajen toshe ɓarnar safarar mutane ta mummunar hanya.

UNODC

Ya ƙara da cewa UNODC tana ƙoƙarin taimaka wa mambobin ƙasashe da ke cikin Majalisar Ɗinkin Duniya wajen hana safarar mutane ba bisa ƙa’ida ba, wanda zai haddasa haɗin kai a tsakanin ƙasa da ƙasa wajen gudanar da sintirin yaƙi da safarar mutane.

Ya ce wannan bincike ba zai taɓa samun nasara ba sai da haɗin gwiwar shugabancin hukumar NIS da gwamnatin ƙasashen Kanada da Danmak wajen bayar da kuɗaɗe domin samun nasara.

Wakilin ya ce binciken ya samar da alƙamuman yawan ‘yan Nijeriya da ke karara zuwa ƙasashen waje domin faɗakar da gwamnatin Nijeriya da sarakuna da malaman addinai da dukkkan sauran al’umma.

UNODC

Ya ce ‘yan Nijeriya ne suka fi yin balaguro zuwa ƙasashen Turai da Asiya a tsakanin ƙasashen yammacin Afirka.  Ya ƙara da cewa sun haɗa kai ne da hukumar NIS da sauran hukumomi da ƙungiyoyin fararen hula domin yaƙi da safarar ‘yan Nijeriya ta mummunar hanya.

Shi ma ministan harkokin cikin gida, Ogbeni Rauf Aregbesola ya bayyana cewa safarar mutane ba bisa ƙa’ida ya zama ruwan dare a cikin al’umma saboda matsalolin tattalin arziki, wanda ke sauya asalin ɗabi’un al’umma. Ministan wanda ya samu wakilcin babbar jami’an ma’aikatan harkokin cikin gida Atiruke Ajiboye. Ya ce yana gode wa dukkan waɗanda suka bayar da goyon baya har wannan rahoton ya kammala na safarar mutane ba bisa ƙa’ida ba.

UNODC

Ya nuna farin cikinsa game da wannan shirin da zai tsaftace al’umma wajen faɗakar da mutane illar safarar mutane domin ceto rayukansu.

  • https://www.unodc.org/

Rahoton na NIS da UNODC zai bude sabon babi na bullo da sabbin hanyoyin dakile safarar mutane ba bisa ka’ida ba

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

IAEA: Za A Tattauna Batun Hadin Gwiwa Tsakanin Amurka Da Birtaniya Da Australiya

Next Post

Majalisar Dokokin Nijeriya Ta Gargadi Gwamnati Kan Ta Inganta Ilimin Bai-Daya

Related

Babu Wata Karamar Hukumar Dake Ƙarƙashin Ikon Ƴan Ta’adda A Filato -Gwamna Mutfwang
Labarai

Babu Wata Karamar Hukumar Dake Ƙarƙashin Ikon Ƴan Ta’adda A Filato -Gwamna Mutfwang

19 minutes ago
Matashi Ya Kashe Surukarsa Saboda Shigarta Cikin Sha’anin Aurensu
Labarai

Matashi Ya Kashe Surukarsa Saboda Shigarta Cikin Sha’anin Aurensu

2 hours ago
Birtaniya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Mutane 33 A Zamfara
Labarai

Birtaniya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Mutane 33 A Zamfara

3 hours ago
Mai Cin Moriyar Kai Da Mai Cin Moriyar Juna
Ra'ayi Riga

Mai Cin Moriyar Kai Da Mai Cin Moriyar Juna

4 hours ago
Kar Ka Zuga Ƴan Arewa Kan Tinubu — Nabena Ya Gargaɗi Kwankwaso
Labarai

Kar Ka Zuga Ƴan Arewa Kan Tinubu — Nabena Ya Gargaɗi Kwankwaso

4 hours ago
Gwamnatin Katsina Ta Fara Bayar Da Maganin Zazzabi Kyauta A Asibitoci
Labarai

Gwamnatin Katsina Ta Fara Bayar Da Maganin Zazzabi Kyauta A Asibitoci

8 hours ago
Next Post
Majalisar Dokokin Nijeriya Ta Gargadi Gwamnati Kan Ta Inganta Ilimin Bai-Daya

Majalisar Dokokin Nijeriya Ta Gargadi Gwamnati Kan Ta Inganta Ilimin Bai-Daya

LABARAI MASU NASABA

Babu Wata Karamar Hukumar Dake Ƙarƙashin Ikon Ƴan Ta’adda A Filato -Gwamna Mutfwang

Babu Wata Karamar Hukumar Dake Ƙarƙashin Ikon Ƴan Ta’adda A Filato -Gwamna Mutfwang

July 29, 2025
Shugaba Xi Ya Aike Da Sako Ga Taron Wanzar Da Zaman Lafiya Na Matasan Kasa Da Kasa

Shugaba Xi Ya Aike Da Sako Ga Taron Wanzar Da Zaman Lafiya Na Matasan Kasa Da Kasa

July 29, 2025
Morocco Ta Shigar Da Ƙara Kan Nasarar Super Falcons A Gasar WAFCON

Morocco Ta Shigar Da Ƙara Kan Nasarar Super Falcons A Gasar WAFCON

July 29, 2025
An Fitar Da Kudaden Farfado Da Sassan Birnin Beijing Da Bala’in Ambaliyar Ruwa Ya Shafa

An Fitar Da Kudaden Farfado Da Sassan Birnin Beijing Da Bala’in Ambaliyar Ruwa Ya Shafa

July 29, 2025
Matashi Ya Kashe Surukarsa Saboda Shigarta Cikin Sha’anin Aurensu

Matashi Ya Kashe Surukarsa Saboda Shigarta Cikin Sha’anin Aurensu

July 29, 2025
Xi Ya Yi Kira Da A Yi Azamar Kare Rayukan Al’umma Yayin Da Ake Fuskantar Ibtila’in Ambaliya A Wasu Sassan Kasar Sin

Xi Ya Yi Kira Da A Yi Azamar Kare Rayukan Al’umma Yayin Da Ake Fuskantar Ibtila’in Ambaliya A Wasu Sassan Kasar Sin

July 29, 2025
Birtaniya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Mutane 33 A Zamfara

Birtaniya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Mutane 33 A Zamfara

July 29, 2025
Mai Cin Moriyar Kai Da Mai Cin Moriyar Juna

Mai Cin Moriyar Kai Da Mai Cin Moriyar Juna

July 29, 2025
Kar Ka Zuga Ƴan Arewa Kan Tinubu — Nabena Ya Gargaɗi Kwankwaso

Kar Ka Zuga Ƴan Arewa Kan Tinubu — Nabena Ya Gargaɗi Kwankwaso

July 29, 2025
Gwamnatin Katsina Ta Fara Bayar Da Maganin Zazzabi Kyauta A Asibitoci

Gwamnatin Katsina Ta Fara Bayar Da Maganin Zazzabi Kyauta A Asibitoci

July 29, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.