ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mai Cin Moriyar Kai Da Mai Cin Moriyar Juna

by CGTN Hausa and Sulaiman
11 months ago
Moriya

Ana kira Madagarscar kasar Vanilla, sakamakon ingancin tsirran Vanilla da ake samarwa a kasar, har ma yawan Vanilla da ake samarwa a kasar da ma fitarwa zuwa ketare ya kai na farko a duniya. Kasar Amurka kuma sakamakon yawan Askirim da ake sayarwa a kasar, ta kasance kasar da take kan gaba a yawan shigowa da Vanilla daga kasar Madagascar. Sai dai munanan matakan haraji da Amurka ta dauka a kan kasa da kasa, ya haifar da cikas ga Madagarscar wajen fitar da Vanilla, matakin da har ya daga farashin Askirim da ake sayarwa a kasar. Daidai kamar yadda wani jami’in diplomasiyya na kasar Madagarscar ya fada, harajin da Amurka ta sanya yana haifar da tasiri ga ‘yan kasuwa da al’umma na kasar Madagarscar, sai dai a sa’i daya, yana kuma tasiri ga masu sayayya na cikin gidan Amurka. 

“Munafunci dodo ya kan ci mai shi”. A hakika yadda gwamnatin kasar Amurka ta dauki matakan haraji ba bisa ka’ida ba yana haifar da munanan illoli ga kanta. Ta fannin abinci, bayan matsalar karancin kwai da aka fuskanta a kasar Amurka a farkon bana, a watan Yunin da ya gabata, farashin naman sa ya hau har zuwa wani matsayin da ba a taba ganin irinsa ba a tarihi, inda farashin nikakken naman sa ya karu da kusan kaso 12% kwatankwacin makamancin lokacin bara. Ban da haka, ‘yan kasuwar shigar da kayayyaki daga waje na kasar sun yi gargadin cewa, sakamakon matakan haraji da gwamnatin kasar ta dauka, farashin tumatir, da na sauran ‘ya’yan itatuwa da ganyaye ma ka iya karuwa da sauri. Hasali ma dai, matakan haraji na haifar da matsaloli ga tattalin arziki na kasar. Rahoton da kamfanin General Motor na kasar ta fitar game da harkokin kudinta cikin rubu’i na biyu na bana ya nuna cewa, matakan haraji na gwamnatin Amurka ta dauka ya haddasa hasarori kimanin dalar Amurka biliyan 1.1 ga kamfanin, kuma ribar da ya ci ma ya ragu da kaso 35.4%. Sai kuma alkaluman da ma’aikatar kasuwanci ta kasar Amurka ta samar a karshen Yuni ya shaida cewa, alkaluman tattalin arziki GDP na kasar cikin rubu’i na farko na bana ya ragu da kaso 0.5% kwatankwacin rubu’in karshe na bara. Har ila yau, kamfanin Fitch Ratings ya rage hasashen da ya yi game da makomar kaso 1/4 na sana’o’in kasar Amurka har ya bayyana ta a matsayin tabarbarewa, bisa dalilin rashin tabbas da ake kara fuskanta da kuma raguwar saurin bunkasar tattalin arzikin kasar.

  • Kar Ka Zuga Ƴan Arewa Kan Tinubu — Nabena Ya Gargaɗi Kwankwaso
  • Gwamnonin Nijeriya Sun Yi Ta’aziyyar Waɗanda Suka Rasu A Ambaliyar Ruwa A Adamawa

A akasin haka, wani rahoton da hukumar kididdiga ta kasar Sin ta bayar kwanan nan game da tattalin arzikin kasar Sin cikin farkon rabin shekarar bana, ya nuna cewa, alkaluman tattalin arzikin GDP ya karu da 5.3% a kasar Sin. Wannan ba karamar nasara ba, musamman a yayin da kariyar ciniki ke addabar duniya tare da haifar da cikas ga farfadowar tattalin arzki, wanda ya shaida ingancin tattalin arzikin kasar Sin, tare da sake tabbatar da al’ummar duniya cewa, bude kofa yana samar da ci gaba, yayin da rufe kofa kan haifar da koma baya. A hakika, tun bayan kafuwar jamhuriyar jama’ar kasar Sin, saurin bunkasar kasar ta fannonin tattalin arziki da zaman al’umma ya tabbata ne sakamakon yadda kasar ke bude kofarta ga ketare, da ma aiwatar da hadin gwiwar cin moriyar juna da kasa da kasa. A sa’i daya kuma, babbar kasuwar kasar Sin, da fasahohin zamani da cikakken tsarin masana’antu na kasar su ma sun samar da alfanu ga kasa da kasa. Duba da cewa, a cikin ‘yan shekarun baya, kasar ta samar da gudummawar da ta kai kimanin kaso 30% na bunkasuwar tattalin arzikin duniya baki daya, lamarin da ya sa ta zama babban ginshikin bunkasuwar tattalin arzikin duniya.

ADVERTISEMENT

Ko da yake har yanzu Amurka tana kare aniyarta ta sanya harajin da bai dace ba kan kasa da kasa, amma ko kadan kasar Sin ba za ta tsayar da bude kofarta da hadin gwiwa da sauran kasashe ba. A satin da ya wuce, kasar ta samu babban ci gaba wajen gina tashar ciniki marar shinge ta Hainan, inda ta sanar da cewa, za a fara aiwatar da tsarin aikin kwastam mai zaman kansa a duk fadin tsibirin Hainan tun daga ranar 18 ga watan Disamban bana. Wato ya zuwa lokacin, za a fadada nau’o’in hajojin da ake cire musu harajin kwastan daga 1900 na yanzu har zuwa 6600, adadin da ya kai kimanin kaso 74% na gaba dayan hajoji.

Amurka tana daukar munanan matakan haraji ne don neman cimma burinta na “mai da Amurka a gaba da komai”, mataki mai son kai ne wanda ba kawai ya lalata moriyar sauran kasashe, har ma da ita kanta. Kasar Sin a nata bangare, tana dukufa a kan bude kofarta ga ketare, don kowa ya ci moriya.

LABARAI MASU NASABA

Hadin Gwiwar Noma Tsakanin Sin Da Afirka: Daga “Sari Ka Ba Ni” Zuwa ” Zamanintar Da Kansu Tare”

Cudanyar Al’Adu Tana Tabbatar Da Kyakkyawar Makomar Sin Da Afirka 

Jama’a, shin mene ne ra’ayinku?

Moriya
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Japan Ta Kwaye Lullubin Da Take Fakewa Da Shi Wajen Kiran Kanta Mai Kaunar Zaman Lafiya
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Yanayin Bunkasar Hada-hadar Cinikayyar Sin Ya Shaida Karkon Manufofin Raya Tattalin Arzikin Kasar
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN Ya Shaida Gamsuwar Masu Bayyana Ra’ayoyi Da Gudunmawar Sin Game Da Tsarin Jagorancin Hakkin Bil’adama
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Kasar Sin Ta Sanar Da Sanya Takunkumi A Kan Ministan Tsaron Kasar Philippines Da Iyalansa
Moriya
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar
  • Sulaiman
    Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”
  • Sulaiman
    Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ya Soki Dabarar Siyasa Ta Sakataren Tsaron Philippines
  • Sulaiman
    Africa CDC Ta Yaba Da Hadin Gwiwar Sin A Yakin Da Afrika Ke Yi Da Cutar Ebola

MASU ALAKA

Hadin Gwiwar Noma Tsakanin Sin Da Afirka: Daga “Sari Ka Ba Ni” Zuwa ” Zamanintar Da Kansu Tare”
Ra'ayi Riga

Hadin Gwiwar Noma Tsakanin Sin Da Afirka: Daga “Sari Ka Ba Ni” Zuwa ” Zamanintar Da Kansu Tare”

June 12, 2026
Cudanyar Al’Adu Tana Tabbatar Da Kyakkyawar Makomar Sin Da Afirka 
Ra'ayi Riga

Cudanyar Al’Adu Tana Tabbatar Da Kyakkyawar Makomar Sin Da Afirka 

June 10, 2026
Labarin Yin Yuzhen: Sin Tana Hadin Gwiwa Da Ketare Don Cika Alkawarin Kiyaye Muhallin Duniya
Ra'ayi Riga

Labarin Yin Yuzhen: Sin Tana Hadin Gwiwa Da Ketare Don Cika Alkawarin Kiyaye Muhallin Duniya

June 5, 2026
Next Post
Birtaniya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Mutane 33 A Zamfara

Birtaniya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Mutane 33 A Zamfara

LABARAI MASU NASABA

Hukumar FAO Ta Samar Da Shirin Kiwon Tarwada A Jihar Gombe

Hukumar FAO Ta Samar Da Shirin Kiwon Tarwada A Jihar Gombe

June 13, 2026
Yawan Man Da Nijeriya Ke Hakowa Ya Karu Da Ganga 177,000 A Janairu

Dalilin Da Ya Sa Matatar Dangote Ta Kara Habaka Tura Man Fetur

June 13, 2026
Zan Saki Nnamdi Kanu Idan Na Zama Shugaban Ƙasa – Peter Obi

Zan Saki Nnamdi Kanu Idan Na Zama Shugaban Ƙasa – Peter Obi

June 13, 2026
NPA Ta Tara Kudin Shiga Naira Biliyan 758.2 A 2024

NPA Da Birtaniya Sun Kulla Yarjejeniyar Zamanantar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Nijeriya

June 13, 2026
Sukar Da Ake Yi Wa Mbappé Ta Yi Yawa — Dembélé

Sukar Da Ake Yi Wa Mbappé Ta Yi Yawa — Dembélé

June 13, 2026
Yadda Rufe Kan Iyakoki Ke Ci Gaba Da Zama Barazana Ga Tattalin Arzikin Nijeriya

Yadda Rufe Kan Iyakoki Ke Ci Gaba Da Zama Barazana Ga Tattalin Arzikin Nijeriya

June 13, 2026
Mutum 53,000 Ke Mutuwa Duk Shekara Sakamakon Amfani Da Gurbataccen Abinci —Gwamnati

Mutum 53,000 Ke Mutuwa Duk Shekara Sakamakon Amfani Da Gurbataccen Abinci —Gwamnati

June 13, 2026
Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

June 12, 2026
2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

June 12, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

June 12, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.