ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 6, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Birtaniya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Mutane 33 A Zamfara

by Abubakar Sulaiman
10 months ago
Birtaniya

Gwamnatin Birtaniya ta bayyana damuwarta tare da yin Allah-wadai da kisan fursunoni 33 da ’yan bindiga suka kashe a jihar Zamfara, duk da cewa an biya su kuɗin fansa Naira miliyan 50 kafin kisan.

Rahotanni sun bayyana cewa ƴan bindigar da suka kai harin ƙarƙashin jagorancin shahararren ɗan ta’adda mai suna Ɗan Sadiya, sun sace fiye da mutane 50 a garin Banga da ke ƙaramar hukumar Kaura Namoda, kafin daga bisani su saki mutum 17 daga cikinsu, yawancinsu mata, bayan karɓar kuɗin fansar.

  • Gwamnan Zamfara Ya Naɗa Abdulkadir Ibrahim A Matsayin Sabon Sarkin Katsinan Gusau Na 16
  • CDD Ta Soki NBC Kan Cin Tarar Trust TV Da Wasu Miliyan 20

A wani taron manema labarai da aka gudanar a ranar Talata dangane da shirin faɗaɗa aikin cibiyar haɗin gwuiwa ta yaƙi da garkuwa da mutane, mai wakiltar Birtaniya a Nijeriya, Gill Levers, ta bayyana cewa satar mutane da garkuwa da su babban laifi ne wanda ke dagula zamantakewa da ci gaban al’umma. Ta ƙara da cewa hakan yana shafar lafiyar ƙwaƙwalwa da jiki na mutane, kuma dole ne a kawo ƙarshensa.

ADVERTISEMENT

Levers ta bayyana cewa an ƙirƙiro Cibiyar  Yaƙi da Garkuwa da Mutane a matsayin wani shiri na shekaru uku domin haɗa kai tsakanin hukumomin tsaro na Nijeriya wajen yaƙi da garkuwa da mutane. Cibiyar za ta riƙa tattarawa da nazari da raba daftarin bayanai ga ofishin mai baiwa shugaban ƙasa shawara kan harkokin tsaro.

Shugaban Cibiyar Yaƙi da Ta’addanci ta Kasa (NCTC), Manjo Janar Adamu Laka, ya ce cibiyar tana aiki kafaɗa da kafaɗa da rundunonin Soji da jami’an tsaro tun kafuwarta, inda take taimakawa wajen daƙile hare-haren garkuwa da mutane a faɗin ƙasar. Ya ce cibiyar na ci gaba da gina dangantaka da hukumomin tsaro a matakin jihohi domin samun sakamako mai kyau a matakin ƙasa da na ƙasa-ƙasa.

LABARAI MASU NASABA

Matsalar Tsaro Da Tsadar Kayan Noma Na Barazana Ga Samar Da Abinci A Daminar Bana

Ban Sha Wata Wahala Ba A Gwagwarmayar Shiga Harkar Fim —Hadiza

Birtaniya
Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Darajar Naira Ta Sauka A Kasuwar Musayar Kuɗaɗe
  • Abubakar Sulaiman
    Hadimin El-Rufai Ya Zargi ICPC Da Hana Shi Samun Kulawar Likita
  • Abubakar Sulaiman
    Nijeriya Da Turkiyya Sun Ƙulla Yarjejeniyar Haɗin Gwuiwa Don Bunƙasa Harkar Ma’adinai
  • Abubakar Sulaiman
    Sace Ɗalibai Ya Karu A Mulkin Tinubu Fiye Da Gwamnatocin Baya – Obi

MASU ALAKA

Matsalar Tsaro Da Tsadar Kayan Noma Na Barazana Ga Samar Da Abinci A Daminar Bana
Rahotonni

Matsalar Tsaro Da Tsadar Kayan Noma Na Barazana Ga Samar Da Abinci A Daminar Bana

June 6, 2026
Ban Sha Wata Wahala Ba A Gwagwarmayar Shiga Harkar Fim —Hadiza
Labarai

Ban Sha Wata Wahala Ba A Gwagwarmayar Shiga Harkar Fim —Hadiza

June 6, 2026
Sanata Wamakko Ya Koka Kan Taɓarɓarewar Sha’anin Tsaro
Manyan Labarai

Sanata Wamakko Ya Koka Kan Taɓarɓarewar Sha’anin Tsaro

June 6, 2026
Next Post
Xi Ya Yi Kira Da A Yi Azamar Kare Rayukan Al’umma Yayin Da Ake Fuskantar Ibtila’in Ambaliya A Wasu Sassan Kasar Sin

Xi Ya Yi Kira Da A Yi Azamar Kare Rayukan Al’umma Yayin Da Ake Fuskantar Ibtila’in Ambaliya A Wasu Sassan Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

Rundunar Sojan Kasar Sin Ta Sa Ido Kan Jirgin Ruwan Yakin Kasar Holland Da Ya Tsallake Mashigin Tekun Taiwan

Rundunar Sojan Kasar Sin Ta Sa Ido Kan Jirgin Ruwan Yakin Kasar Holland Da Ya Tsallake Mashigin Tekun Taiwan

June 6, 2026
Sin Tana Adawa Da Karin Takunkumin Da Amurka Ta Sanya Wa Cuba

Sin Tana Adawa Da Karin Takunkumin Da Amurka Ta Sanya Wa Cuba

June 6, 2026
Matsalar Tsaro Da Tsadar Kayan Noma Na Barazana Ga Samar Da Abinci A Daminar Bana

Matsalar Tsaro Da Tsadar Kayan Noma Na Barazana Ga Samar Da Abinci A Daminar Bana

June 6, 2026
Ban Sha Wata Wahala Ba A Gwagwarmayar Shiga Harkar Fim —Hadiza

Ban Sha Wata Wahala Ba A Gwagwarmayar Shiga Harkar Fim —Hadiza

June 6, 2026
Alfanu Da Rashin Alfanun Tallata Hotunan Ango Da Amarya Kafin Daura Aure

Alfanu Da Rashin Alfanun Tallata Hotunan Ango Da Amarya Kafin Daura Aure

June 6, 2026
Darajar Naira Ta Sauka A Kasuwar Musayar Kuɗaɗe

Darajar Naira Ta Sauka A Kasuwar Musayar Kuɗaɗe

June 6, 2026
Yadda Ake Miyar Margi Da Kifin Tarwad

Yadda Ake Miyar Margi Da Kifin Tarwad

June 6, 2026
Sanata Wamakko Ya Koka Kan Taɓarɓarewar Sha’anin Tsaro

Sanata Wamakko Ya Koka Kan Taɓarɓarewar Sha’anin Tsaro

June 6, 2026
A Matsayinki Na Mace, Kada Ki Yi Wasa Da Wadannan Abubuwa

A Matsayinki Na Mace, Kada Ki Yi Wasa Da Wadannan Abubuwa

June 6, 2026
Hadimin El-Rufai Ya Zargi ICPC Da Hana Shi Samun Kulawar Likita

Hadimin El-Rufai Ya Zargi ICPC Da Hana Shi Samun Kulawar Likita

June 6, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.