ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, September 14, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Birtaniya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Mutane 33 A Zamfara

by Abubakar Sulaiman
1 year ago
Birtaniya

Gwamnatin Birtaniya ta bayyana damuwarta tare da yin Allah-wadai da kisan fursunoni 33 da ’yan bindiga suka kashe a jihar Zamfara, duk da cewa an biya su kuɗin fansa Naira miliyan 50 kafin kisan.

Rahotanni sun bayyana cewa ƴan bindigar da suka kai harin ƙarƙashin jagorancin shahararren ɗan ta’adda mai suna Ɗan Sadiya, sun sace fiye da mutane 50 a garin Banga da ke ƙaramar hukumar Kaura Namoda, kafin daga bisani su saki mutum 17 daga cikinsu, yawancinsu mata, bayan karɓar kuɗin fansar.

  • Gwamnan Zamfara Ya Naɗa Abdulkadir Ibrahim A Matsayin Sabon Sarkin Katsinan Gusau Na 16
  • CDD Ta Soki NBC Kan Cin Tarar Trust TV Da Wasu Miliyan 20

A wani taron manema labarai da aka gudanar a ranar Talata dangane da shirin faɗaɗa aikin cibiyar haɗin gwuiwa ta yaƙi da garkuwa da mutane, mai wakiltar Birtaniya a Nijeriya, Gill Levers, ta bayyana cewa satar mutane da garkuwa da su babban laifi ne wanda ke dagula zamantakewa da ci gaban al’umma. Ta ƙara da cewa hakan yana shafar lafiyar ƙwaƙwalwa da jiki na mutane, kuma dole ne a kawo ƙarshensa.

ADVERTISEMENT

Levers ta bayyana cewa an ƙirƙiro Cibiyar  Yaƙi da Garkuwa da Mutane a matsayin wani shiri na shekaru uku domin haɗa kai tsakanin hukumomin tsaro na Nijeriya wajen yaƙi da garkuwa da mutane. Cibiyar za ta riƙa tattarawa da nazari da raba daftarin bayanai ga ofishin mai baiwa shugaban ƙasa shawara kan harkokin tsaro.

Shugaban Cibiyar Yaƙi da Ta’addanci ta Kasa (NCTC), Manjo Janar Adamu Laka, ya ce cibiyar tana aiki kafaɗa da kafaɗa da rundunonin Soji da jami’an tsaro tun kafuwarta, inda take taimakawa wajen daƙile hare-haren garkuwa da mutane a faɗin ƙasar. Ya ce cibiyar na ci gaba da gina dangantaka da hukumomin tsaro a matakin jihohi domin samun sakamako mai kyau a matakin ƙasa da na ƙasa-ƙasa.

LABARAI MASU NASABA

Ka Kyale Ni Nayi Wa Mutanen Binuwai Aiki – Gwamna Alia Ga Ortom

Makiyaya Sun Yi Asarar Shanu 200,000 Ta Dalilin Rikice-Rikice – MACBAN

Birtaniya
Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Ka Kyale Ni Nayi Wa Mutanen Binuwai Aiki – Gwamna Alia Ga Ortom
  • Abubakar Sulaiman
    Makiyaya Sun Yi Asarar Shanu 200,000 Ta Dalilin Rikice-Rikice – MACBAN
  • Abubakar Sulaiman
    Farashin Man Fetur Ya Sake Tashi A Abuja
  • Abubakar Sulaiman
    Mutane 24 Sun Mutu Bayan Shan

MASU ALAKA

Ka Kyale Ni Nayi Wa Mutanen Binuwai Aiki – Gwamna Alia Ga Ortom
Labarai

Ka Kyale Ni Nayi Wa Mutanen Binuwai Aiki – Gwamna Alia Ga Ortom

September 13, 2026
Ka Kyale Ni Nayi Wa Mutanen Binuwai Aiki – Gwamna Alia Ga Ortom
Labarai

Makiyaya Sun Yi Asarar Shanu 200,000 Ta Dalilin Rikice-Rikice – MACBAN

September 13, 2026
Birtaniya
Labarai

Malamai Da Limamai 3,000 Sun Yi Addu’ar Zaman Lafiya Da Nasarar Tinubu A 2027

September 13, 2026
Next Post
Xi Ya Yi Kira Da A Yi Azamar Kare Rayukan Al’umma Yayin Da Ake Fuskantar Ibtila’in Ambaliya A Wasu Sassan Kasar Sin

Xi Ya Yi Kira Da A Yi Azamar Kare Rayukan Al’umma Yayin Da Ake Fuskantar Ibtila’in Ambaliya A Wasu Sassan Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

Manchester Derby: City Ta Nunawa United Kwanji A Old Trafford

Manchester Derby: City Ta Nunawa United Kwanji A Old Trafford

September 13, 2026
Ka Kyale Ni Nayi Wa Mutanen Binuwai Aiki – Gwamna Alia Ga Ortom

Ka Kyale Ni Nayi Wa Mutanen Binuwai Aiki – Gwamna Alia Ga Ortom

September 13, 2026
Ka Kyale Ni Nayi Wa Mutanen Binuwai Aiki – Gwamna Alia Ga Ortom

Makiyaya Sun Yi Asarar Shanu 200,000 Ta Dalilin Rikice-Rikice – MACBAN

September 13, 2026
Birtaniya

Farashin Man Fetur Ya Sake Tashi A Abuja

September 13, 2026
Shugabannin BRICS Sun Amince Da Sanarwar Hadin Gwiwa A Taron Koli Na New Delhi

Shugabannin BRICS Sun Amince Da Sanarwar Hadin Gwiwa A Taron Koli Na New Delhi

September 13, 2026
Birtaniya

Malamai Da Limamai 3,000 Sun Yi Addu’ar Zaman Lafiya Da Nasarar Tinubu A 2027

September 13, 2026
An Samu Babban Sakamako Kan Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa Na Duniya

An Samu Babban Sakamako Kan Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa Na Duniya

September 13, 2026
Ministan Kimiyya Na Afirka Ta Kudu Ya Yi Kiran Zurfafa Hadin Gwiwar Kimiyya Da Fasaha Da Sin

Ministan Kimiyya Na Afirka Ta Kudu Ya Yi Kiran Zurfafa Hadin Gwiwar Kimiyya Da Fasaha Da Sin

September 13, 2026
Birtaniya

An Gudanar Da Sallar Zana’idar Tsohon Gwamnan Gongola

September 13, 2026
Yajin Aikin ASUU: Malaman Jami’ar Jihar Kaduna Sun Bijirewa El-rufa’i

Gwamna Uba Sani Ya Amince Da Ƙarin Albashi Ga Ma’aikatan KASU

September 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.