• English
  • Business News
Thursday, November 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsaro: Wainar Da Aka Toya A Taron Gwamnoni Da Sarakunan Arewa A Abuja

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
Abuja

Sakamakon yawaitar rashin tsaro a Nijeriya musamman a yankin arewa ta sa gwamnoni da sarakunan gargajiya na yankin sun goyi bayan kafa ‘yansandan jihohi.

A ranar Talata da ta gabata ce, kungiyar gwamnonin arewa (NGF) suka gana da majalisar sarakunan gargajiya na arewa a Abuja, wanda sakamakon ganawar suka bullo da kudurin kafa ‘yansandan jihohi domin dakile matsalar tsaro a yankin da ma Nijeriya gaba daya.

  • Kotu Ta Dage Karar Da Gwamnatin Tarayya Ta Kai ASUU

LEADERSHIP ta ruwaito cewa majalisar kasa ta dade tana watsi da kiraye-kirayen kafa ‘yansandan jihohi lokacin gyaran tsarin mulki, bisa fargabar gwamnonin na iya amdani da su ba bisa ka’ida ba.
Daga cikin matsaloli da aka tattauna a karshen wannan ganawa da ta gudana a otel din Transcorp Hilton da ke Abuja, ‘yan siyasan arewa da sarakunan gargajiya sun sake bibiyar matsalar tsaro a yankin arewa da sauran matsaloli da suka hana yankin ci gaba tare da kawo mafita da kuma goyon bayan yi wa tsarin mulki kuskwarima ta yadda za a samu damar kafa ‘yansandan jihohi.

Shugaban kungiyar gwamnonin arewa kuma gwamnan Jihar Filato, Rt. Hon Simon Lalong shi ne ya karanta manyan batutuwan taron, inda ya bayyana cewa samar da ‘yansandar jihohi zai magance matsalolin tsaro da suka addabi yankin.
A bangaren sakarunan gargajiya kuwa, Mai Alfarma Sarkin Musulmi, Muhammad Sa’ad Abubakar III shi ne ya jaroranci sarakunan, wanda suka hada har da Shehun Borno, Sarkin Kano, Zazzau, Fika, Lafiya, Anka, Gumi, Attah Igala, Ochi Doma, Aku Uka na Wukari da dai sauransu.

Shugabannin dai sun bayyana cewa sun tattauna ne kan al’amuran da suka shafi tsaro da inganta rayuwar al’umma da noma da kasuwanci da zuba jari da nauyin da suka rataya a kan sarakunan gargajiya wajen samar da zaman lafiya da tsaro a yankin arewa.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Amince da Gina Sabbin Gidaje Ga Alƙalai, Da Samar Da Ruwa A  FCT

Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 

Tattaunawar ta samu halartar wakilan kungoyoyin fararen hula da suka hada da Kungiyar Mata ta NFWP’ da ta bunkasa ilimin ‘ya`ya mata ta AGILE’, wanda dukkan su bankin duniya ne ya kafa su.
A halin da ake cikin kuma, Shugaban Kasa Muhammadu Buhari ya bayyana cewa gwamnatinsa ta yi matukar kokari wajen samar da tsaro da ababen more rayuwa.

Shugaban kasan ya bayyana hakan ne lokacin da yake yi wa masu ruwa da tsaki jawabi a fadar gwamnatin Jihar Imo da ke Owerri bayan da ya kaddamar da babban hanyar Owerri zuwa Orlu da na Owerri zuwa Okigwe da sake gyaran ginin majalisar dokokin jihar da gwamna Hope Uzodimma ya yi.
Ya ce duk da karancin kudade da gwamnatinsa ta fuskanta ta samu nasarori masu dinbin yawa.
“Gwamnatina ta samu nasarar magance matsalolin ababen more rayuwa da na tsaro a Nijeriya idan aka kwatanta da shekarun da ke tsakanin 1999 har zuwa 2015 lokacin da muka karbi mulki,” in ji shi.

Shugaban Buhari ya yaba wa gwamnatinsa bisa kokarin magance matsalolin Boko Haram a yankin arewa maso gabas da inganta ababen more rayuwa wanda gwamnatinsa ta gada tun a lokacin zamanin mulkin PDP.
Buhari ya ce gwamnatin tarayya za ta ci gaba da goyon bayan gwamnatin Jihar Imo da na sauran jihohi domin samar da kyakkyawan dimokoradiyya wanda mutane za su yi alfahari da akidar jam’iyyarsu.

A nasa bangaren kuwa, shugaban kugiyar Ohanaeze Ndigbo, Farfesa George Obiozor ya bayyana cewa rashin tsaro da karancin ababen more rayuwa su ne babban matsaloli guda biyu da suke addabar yankin kudu maso gabashin Nijeriya. Ya yi kira ga gwamnatin tarayya da ta yi kokarin magance wadannan matsaloli guda biyu.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Ta Amince da Gina Sabbin Gidaje Ga Alƙalai, Da Samar Da Ruwa A  FCT
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Amince da Gina Sabbin Gidaje Ga Alƙalai, Da Samar Da Ruwa A  FCT

November 6, 2025
Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 
Manyan Labarai

Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 

November 6, 2025
Gwamnatin tarayya
Labarai

Ta’addanci Ba Zai Yi Nasara Ba A Ƙasarmu — Tinubu

November 6, 2025
Next Post
NDLEA Ta Kwace Maganin Cutar Hauka Mai Nauyin Kilo 150 A Gombe

NDLEA Ta Cafke Mutum 761 Bisa Hada-hadar Miyagun Kwayoyi A Kaduna

LABARAI MASU NASABA

An Yi Taron Kaddamar Da Tsarin Kawancen Kafafen Watsa Labarun Kasashe Masu Tasowa Da Dandalin Yada Labarai Na Bidiyo Karo Na 13 A Xi’an

An Yi Taron Kaddamar Da Tsarin Kawancen Kafafen Watsa Labarun Kasashe Masu Tasowa Da Dandalin Yada Labarai Na Bidiyo Karo Na 13 A Xi’an

November 6, 2025
CMG Ya Kaddamar Da Wasu Tashoshin Talabijin Uku A Dandalin FAST

CMG Ya Kaddamar Da Wasu Tashoshin Talabijin Uku A Dandalin FAST

November 6, 2025
Baje Kolin CIIE Ya Bayar Da Tabbaci Ga Duniya

Baje Kolin CIIE Ya Bayar Da Tabbaci Ga Duniya

November 6, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Amince da Gina Sabbin Gidaje Ga Alƙalai, Da Samar Da Ruwa A  FCT

Gwamnatin Tarayya Ta Amince da Gina Sabbin Gidaje Ga Alƙalai, Da Samar Da Ruwa A  FCT

November 6, 2025
Manufofin Sin Na Yaki Da Sauyin Yanayi: Gani Ya Kori Ji

Manufofin Sin Na Yaki Da Sauyin Yanayi: Gani Ya Kori Ji

November 6, 2025
Shugaba Xi Ya Jaddada Bukatar Gina Ingantaccen Yankin Ciniki Cikin ’Yanci Na Tashar Ruwa Ta Hainan

Shugaba Xi Ya Jaddada Bukatar Gina Ingantaccen Yankin Ciniki Cikin ’Yanci Na Tashar Ruwa Ta Hainan

November 6, 2025
Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 

Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 

November 6, 2025
A Karon Farko An Gabatar Da Ka’idar Kasa Da Kasa Ta Fasahar 5G Mai Amfani Ga Masana’antu

A Karon Farko An Gabatar Da Ka’idar Kasa Da Kasa Ta Fasahar 5G Mai Amfani Ga Masana’antu

November 6, 2025
Gwamnatin tarayya

Ta’addanci Ba Zai Yi Nasara Ba A Ƙasarmu — Tinubu

November 6, 2025
Bikin Baje Kolin CIIE: Da Abokin Daka Ake Shan Gari

Bikin Baje Kolin CIIE: Da Abokin Daka Ake Shan Gari

November 6, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.